Showing 51001 words to 54000 words out of 130248 words
taimaketa ba'ai mai gaba ɗaya ba yasa ta Miƙe sbd wani iri data keji a jikinta ta nufi bathroom tare da zame rigar jikinta, ta sakarwa kanta ruwan sanyi dan ba zata iya jira ta haɗa na zafi ba. Yana ta zaune kafin yaji ta buɗe ƙofa ta fito kanta a ƙasa ta fito domin ko kula da shi ba tayi ba, inda aka ajjiye mata wasu ƙananun kayanta ta buɗe ta ɗauki wasu Sleep wears na prada dark brown masu kyau, idanunsa a kanta tana ƙoƙarin zame towel taji yay tari shima kansa bai san lokacin da tarin ya kwace masa ba, da sauri jikinta na rawa tai bathroom da gudu tana haƙƙi tare da dafe ƙirjinta, dry kawai yay kana ya kwanta saman bed ɗin domin yasan kota fito babu abinda zai mata shi tausayinta ma ya keji, Fannah kam bayan ta sanya kayan da sukai mata wani bala'in kyau kasa fitowa tayi sai da taji alamar ya fita, Sannan ta fito kai tsaye kwanciya tayi ta rufe idanunta cikin sauri ta buɗe su sbd Sheikh daya faɗo mata da kuma kukan da yake sai taji gaba ɗaya jikinta yay sanyi menene dalin daya sanya yake kuka? Kodan ta hanashi taɓa jikinta a yadda take jin son sa ƙaunar sa ko rayuwarta zata iya bayar indai zai farin ciki da wannan tunanin bacci ɓarawo ya ɗauke ta. Mami ruwan zafi sosai ta shiga zafi da kuma raɗaɗin bata keji yasa ta shafa versiline ita da sweet Imam ɗinta ne bata da wata matsala sai daɗin abinda daza taji amma Barrister ya wargatsa mata dukkan shirinta kuma wlh saita rama. Sheikh yadda yaga rana haka yaga dare sam ko runtsawa bai ba, da ƙyar ya nemi duvet ya rufe jikinsa. Da asuba Granny ta tura ƙofar sosai tai mmkin ganinta a buɗe tunda ta shigo yake binta da kallo harta ƙarasu gadon tabi da kallo tace "Yaya haka Imamu? Meye duk ka hargitsa gadon fisabilillahi kamar dai wanda ya samu filin sukuwa?" Bai tankata ba abinda ya keji a zcyarsa bazai taɓa barinsa yay mgn, ji a matuƙar sanyaye ya zuro ƙafafuwan sa ƙasan bed ɗin tare da zura wasu Slippers ɗin Berluti masu tsada sosai da kuma rashin nauyi, Warm water yasa Granny ta haɗa masa a cikin jakuzzie kana ta fita Lumshe idanunsa yay lokacin da ruwan ya ratsa cikin jikinsa ya shiga sauke numfashi wahala, har zuwa lokacin kuma hjyar nan inda take sai da ya sakar mata ruwan zafi sosai sannan ta dai-dai ta amma har yanzu mararsa ciwo take masa, daɗin ruwan zafin yasa wani bacci ya fara fisgarsa da ƙyar ya lallaɓa ya hau saman wheelchair dake bathroom ɗin ya ƙarasa wajan shower ya ɗaure raye jikinsa kana yay ɗaura alwala tare dayin brush, bathrobe ya saka a sanyaye ya shiga buga ƙofar Granny nice ta shigo ganin yanayinsa na yau yasa bata ƙara yin mgna ba sai duk ta firgita tunaninta ya shiga bata ko Aljanar ce ta dawo, a gurguje ta gama shafa masa wani versiline mai ƙamshi a saman fatarsa kana ta ɗauko kayansa ta bashi, abun yay mmki ya bata ganin bai yasa cire kayansa ba sai da ya juya mata baya Mmki duk ya cika Granny, bayan yasa Maroon ɗin jallabiyar ta fesa masa parfumes ɗinsa mai ƙamshi, sosai ya ƙara kyau ya fito a Sheikh ɗinsa har Parlo Granny ta kaisa tana jiran fitowar Barrister can kuma Fareeq ya fito shima sanye da Jallabiya kallonsa Granny tayi tace "To ina Uban naku kuma?" Fareeq yace "bai fito ba" haɓa ta riƙe tace "Yau naga abinda yafi ƙarfina ni Faɗimatu wacce rashin kunya ce wannan yaushe ya zama gantalalle bani da labari? Sbd yana tare da matarsa shine yaƙi fitowa" da sauri Sheikh ya kalleta sbd ambaton matar da yaji tayi ƙasan zcyarsa ya shiga bugawa, gyaran murya yay hakan yasa Fareeq ya tura Wheelchair ɗin zuwa waje. Sai wajan 6 na safe sannan Fannah ta shiga buɗe idanunta jinta kuma a jikinta mutum yasa ta hantsila da sauri jikinta na rawa tana tashi shima ya fara yana mata wani shu'umin murmushi da sauri tai bathroom shima waje yay yana jin kansa yau a fresh haba Saudat daman babu abinda take dashi take masa iyaye yanzu ya kejin ya sauke dukkan abinda ya tara a mararsa, da wannan tunanin ya haura saman upstairs ya nufi flat ɗinsa yana mmkin yadda gari har yay haske ba tare kuma daya sani ba, wanka yay kana ya shirya ya gabatar da Sallah yana gamawa ya fita zuwa downstairs, Mai aikinsu ya gani tana ta shirya breakfast, gaishesa tayi shi kuma ya nufi bedroom ɗin da Fannah take,samunta yay har tayi Sallah ta koma bacci kayan daya kawo mata ya ajjiye kana ya shafa kanta yana jin soyayyyar ta na ƙara ratsa masa zcy. Arjun kam ji yake kamar bai taɓa jin daɗin rayuwa dama duniyar baki ɗaya, sam bai bacci ba sbd kukan da Aliyah ta kwana ta nayi masa, sai wajan 9 na ya tashi ya shiga shiryawa domin buddy ya tsaya masa a rai yana son yaje yaga yaya ya kwana kafin ta farka daga bacci. Mami tun 7 tabar gidan zuwa wajan aiki shima Barrister ya fita sbd wani meeting da yake da shi. Tsaye take gaban dressing mirror tana kallon yadda idanunta ya kumbura sbd kukan da tayi, tana sanye da wata pitatte gwon ɗin atamfa Holand Orange color wacce taji ɗinkin fatan a sanya mata masu stones masu kyau, ga shape ɗinta daya baiyana ta cikin rigar hips ɗinta sun samu damar zama, bata saba sanya ɗan kwali ba hakan yasa ta ɗauki veil ɗinta daya kasance milk kai Orange ɗin Flowers ta ɗura saman kanta kitson dake gaban goshinta ya ƙara fidda kyanta, yunwa ta keji sosai hakan yasa ta fito daga cikin bedroom ɗin tana fidda wani ƙamshi na abin mmki,babban parlon babu kowa gidan shiru rasa inda zatai tayi su take ko tea ta sami tasha ko taji dai-dai, kanta ta ɗaga taga wajan 12 na safe, abin abinda zcyarta ke gaya mata tayi hakan yasa tabi wata ƙofa wacce take tunanin kitchen ne, tana shiga ta sauke ajjiyar zuciya sbd ganin da gaske kitchen ɗin ne, ƙarasa shiga tayi ta fara duba flast ɗin dake ajjiye saman stool ɗin kitchen ɗin, cikin Sa'a ta samu ruwan zafi ta ɗauki mug ta zuba ta fara haɗa tea mai kauri sbd kayan tea ɗin data gani, bayan ta zuba komai ta ɗauki spoon ta fara juyawa, cikinta har wani ihu yake, ɗauka tayi tare da jin gina da kantar kitchen ɗin idanunta a rufe ta fara shan tea ɗin tana hurawa sbd zafi, ƙamshin da taji kuma ta tabbatar ba jikinta yake ba, bata kawo komai ba ta buɗe idanunta kai tsaye Idanunta ya sauka cikin nasa wanda da alama ya daɗe yana Kallonta, yana zaune saman wheelchair saika ɗauka wani ɗan sarki ne sbd yake da wani kwarjini da cika ido yana sanye da wata shadda white colour anyi masa ɗinkin half body sumar kansa a kwance luff domin ko hula bai saba, hanunsa riƙe da cup of tea yana juya a hankali tuni ya ɗauke idanunsa daga kanta yay kamar bai ganta ba, sbd tsorata da kyansa da kuma kwarjininsa da kuma tuna abinda ya faru jiya yasa wani tari ya kawo mata ziyara tea ɗin bakinta yay feshi ya sauka a saman fuskarsa....
SIRRIN MU isn't free via WhatsApp number 08119237616 for more information ga ƴan Niger 84506476
NIMCYLUV
21/10/2021, 07:24 - 🤔🤔: *_NLUV💞_*
4️⃣1️⃣-4️⃣2️⃣
Bayan tea ɗin data fesa masa a fuska tsoran daya gama kamata yasa ta saki cup ɗin a ƙasa, gaba ɗaya bata tsammaci ganinsa ba hakan yasa da tai arba da shi gaba ɗaya ta gigice still kuma idanunta na kansa, Sheikh ko mutsawa bai ba kansa a ƙasa tamkar bai ganta ba haka yay pretending yaci gaba da shan tea ɗin cike da nutsuwa da kamala, a zahiri kuma idanunsa ne kawai baya gareta amma idon zcyarsa gaba ɗaya ya karkata ne gareta shi har kusan bashi dry tayi sbd yanayin da yaga tsoro ya shigeta kamar wacce taga dodo, ganin ko takan ta baibi ba yasa ta sunkuya tare da ɗaukan cup ɗin ta ajjiye, shi kam tuni yaja Wheelchair ɗin sa yay waje yana sauke numfashi domin baya jin zai iya ƙara some minutes a wajan, babban parlo ya koma tare da zamewa ya zauna saman duguwar sofa ya lumshe idanunsa yana sauke ajjiyar zuciya ganin zai faɗa wani tunani daban ya ɗauki remote ya sauya channel zuwa Aljazeera ya fara kallo duk da cewa ba wani fahimta yake ba,amma dole ya sabarwa kansa dasu sbd ragewa kansa damuwa da kuma wani banzan tunani, yana kallon amma rabin tunaninsa yana ga kitchen ɗin musamman da har yanzu hancinsa yake jiyo masa daɗaɗan turarenta kai ƙamshi da kuma sanyaya zcy. Yana fita ta dafe ƙirjinta tare sauke wata wahalalliyar ajjiyar, kasa aikata komai tayi sbd tuna yanayin da suka shiga shida ita a daren jiya, jikinta ne yay sanyi tana jin yadda zcyarta tayi mata nauyi har yanzu tana ganin girman abun da kuma muninsa,ko wacce mace burinta ta kai mutuncinta gidan mijinta ita gashi yanzu tayi auren duk da ba ƙaunar Barrister take ba kuma bata niyar dugun zama dashi,amma ganin Sheikh sai ya kure mata dukkan wani damuwar da take ciki Sheikh ya taɓa abinda Ubansa bai taɓa ba iya wannan kawai ya tabbatar so da kuma ƙaunarsa sun riga sunyi nisa a zcyarta,amma abu guda ke bata mmki mai yasa a aikata haka? daga ganin mace banda wani dalili ai ba zaka faɗa mata ba haka nan, wacece Airah? Tsaki taja kaɗan sbd sunan Airah data tuna, da kyar ta lallaɓa tasha ruwan tea ɗin ko madara bata iya sanyawa ba. Barrister ne zaune a cikin office ɗinsa yana operating system ɗinsa wayarsa ta fara ƙara alamar kira ya shigo tsayawa yay da abinda yake ganin sunan Uncle Sham yasa yay answering call ɗin yana faɗin "Evening Uncle" gyara zama Uncle Sham yay shima yana cikin office ɗin nasa yace "Barrister ykk ya kwanan amarya?" Murmushi jin daɗi Barrister yay yace "Wlh Allahamdulillah" Uncle Sham yace "Ma sha kasan dalilin kiran ai ko?" Girgiza kai Barrister yay kamar Uncle na kallonsa yace "A'a saika faɗa" shiru Uncle Sham yay yana nazarin abinda zai faɗa can dai yace "Bisa al'adar kanuri dole idan miji ya kwanta da matarsa a sani sbd tabbatar da mutuncinta, hakan tasa kawonta yay min mgn ni kuma nai maka abinda kace shi zan faɗa masa" baya Barrister yay sbd tuna yanayinsa na juya shida Fatimansa duk sai yaji kasala ta saukar masa idanunsa a rufe yace "haka fa, na kwanta da matata kamar yadda al'adar su saukesu,banda abinsu ma waye zai samu kamar dai Fatima kuma yay burus da ita ai sai mara lfy" jinsa kawai Uncle Sham yake amma ba komai ya fahimta ba sauke numfashi yay kafin yace "Ok! Allah ya kyauta" yana faɗin hakan ya kashe kira idanunsa akan laptop ɗin sa yana duba ayyukansa can wayarsa tayi ƙarar Kawon Fannah ya gani kamar dai bazai ɗauka ba sai kuma ya ɗaga yana faɗin "Assalamu alaika" da sauri Kawo Madu yace "wasalamu alaika Shamsudeen yaya ake ciki?" Miƙewa Uncle Sham yay gaba ɗaya tare da ɗaukan key ɗin motarsa ya fita daga office ɗin gaba ɗaya yana tafe yana faɗin "Congratulations Allah ya sanya albarka a auren" Uncle Sham ya faɗa yana shiga cikin motarsa, daga can ɓangaren Kawo Madu yace "Ma sha Allah! Allahamdulillah! Allah dai yay mata albarka dashi Hamdan ɗin gaba ɗaya" da Ameen Uncle ya amsa bai tsaya ya ƙara jin wani abu ba ya kashe kiran gaba ɗaya tare da yiwa motarsa key ya fita daga hospital ɗin. Kawo Madu ne ya kalli matarsa mai suna Yagana yace "Ma sha Allah! Yarinya ta riƙe mana mutuncinta" Yagana tana dry tace "kai amma dai nai farin ciki wlh,daman yarinyar badai hankali da nutsuwa ba" Jinjina kai Kawo Madu yay yace "Haka fa, kinga sunyi nisa damu dole za'a a hqr da farin gyalle a zummar shaida,tunda mijinta ya faɗi hakan shkknan sai kiji wajan Maman Fannah ki gaya mata" da sauri ta miƙe tana ɗaukan Lafayar ta ta ɗaura tace "Ai babu zama wai an saci zanin mahaukaciya yanzu zani na shaida mata" yace "To Allah ya kiyaye" tace "haba dai kamar wacce zatai nisa" ware idanunsa yay waje yana faɗin "Kai amma dai a gaisheki idan Allah ya nufa sai kiga ko waje baki ƙarasa ba Ubangiji ya ɗauki ranki amma ana Allah ya kiyaye wai ba nisa zaki ba" kallonsa tayi tace "Kayi hqr bari naje ma dawo ta ngd da addu'a" tana faɗin haka tai waje. Mama kolo na zaune da Ya Falta sai Yana dukkansu suna parlo suna cin abinci brabisko da miyan yakuwa wacce taji nama manya² masu yawa Yagana tai sallama, gaba ɗaya suka amsa mata Mama kolo na faɗin "sannu da zuwa kece da rana haka?" Yagana ta zauna tana faɗin "Wlh Kawonsu ya tasu ni yanzu haka" Mama kolo tace "to Allah yasa dai lfy?" Murmushi kawai Yagana tayi ta fito da kwalin sabulo da ashana ta ajjiye gaban Mama kolo tare da rangaɗa buɗe, farin ciki da kuma jin daɗi yada Mama kolo sakin kuka daman tana da tabbacin tarbiyyar da tayiwa yaranta ba zasu tashi a banza ba, kusan al'adar su ce haka idan an samu yarinya a matakin budurwa dangin miji zasu bada kwalin sabulo da ashana matsayin tukuci idan kuma ba'a samu ba za'a dangwarar da kwalin sabulo a gabanki empty babu komai a ciki haka kuma shine shaidar ƴar ki bata tare da mutuncinta, tun a titi tayi gantali dashi Yagana tace "Kawonsu ne ya fanshi dangin Mijin tunda basu kusa shine ya bayar a bada kyautar Fannah" sun ɗan jima suna Shira tare da sawa Fannah albarka kana suka ƙara yiwa su Ya Falta faɗa sosai daga nan tai masu sallama ta koma gida. Ƙyakkyawar fuskarsa ta zubawa idanu tun bayan fitowar ta daga kitchen ta samesa yana bacci ya rungome pillow a ƙirjinsa,kasa tafiya tayi tai tsaye nesa dashi tana ƙara jinjina kyawon halittar da Allah ya bawa Sheikh, kallon agogo tayi taga lokacin sallar Zhur ya kusa gashi har yanzu bacci yake, a jikinsa yaji ana kallonsa kuma ya tabbatar da itace domin babu kowa a gidan tun safe Granny ta tisa driver a gaba zuwa a asibiti dubiya, zuwan Arjun ne ma ya taimaka masa har yay wanka ya sauya kaya shine da zai tafi yace ya kawosa cikin kitchen ɗin, sam ba bacci yake ba yay hakanne kawai domin ya bata damar ƙare masa kallo kamar yadda take so, slowly ta janye idanunta tana mmki kujerar guragun data gani kusa dashi, bashi da ƙafa ne kome? Zara-zaran yatsun ƙafarsa ta kalla babu wata alama da zata nuna bashi da ƙafa, tana nan tsaye taji alamar buɗe ƙofar babban parlo cikin nutsuwa ta juya idanunta ya sauka a cikin na Mami gabanta ne ya faɗi da sauri kuma ta janye nata idanun, Kallonta Mami tayi from head to toe sai yanzu tasan dalilin auren ƴar cikinsa da yayi, wato yaga manyan bombom da kuma shafaffan ciki wanda ya bawa ƙirjinta damar bai yana sosai,ga farin da take dashi domin da ita da sweet Imam bata san wanda yafi wani jar fata ba, rufe ƙofar tayi tana takun ƙasaita ta ƙarasa shigowa cikin parlon,kamar yadda bata ƙara kallon Fannah ba itama Fannah bata sake kallonta ba, fuskarta ɗauke da Murmushi tace "Ohh my sweet darling Imam bacci a parlo kai da gidan Ubanka" ta faɗi haka tana ɗauke kansa tare da zama a gefensa,kansa ta ɗura saman cinyarta da sauri shi kuma ya tashi zaune idanunsa a lumshe, fuskarsa ta shafa tana shafo jajayen laɓɓansa tace "am sorry an barka kai ɗaya ba mutane a gidan ko?" Da sauri Fannah ta kalli Mami lallai ma matar nan tana nufin ita ba mutum bace, sai kuma wata zcyar tace kika sani ko Mamansa ce, girgiza kai tayi ita ɗaya ganin babu wata kama da suke da juna, a ganiye ya buɗe ido mai makon ya sauke ganinsa akan Mami sai kawai ya sauke a fararen hannunta wanda suka sha jan lalle mai kyau da tsari, idanunsa ya janye da baya jin zai jure kallon hannunta "Yaya jikin naka,i mean yaka kwana?" Da Mmki yake kallonta tayaya tasan ya kwana da wani abu? Ba tare daya kalleta ba Muryar very slow sbd kasalar data saukar masa yace "Allahamdulillah!" Miƙewa tayi tace "ya kamata kaje ka shirya time ɗin sallah ya kusa nima bana jin daɗi that is why bar wajan aikin na dawo gida da wuri" ta faɗi hakan tana jawo masa Wheelchair zuwa gabansa, zcyar Fannah ce ta buga da ƙarfi kardai tunaninta ya zama gsky tataya ƙyakƙyawan mutum zai zama gurgu saurin astagafirullah tayi a zcyrta, idanunta kuma ya cicciko da ƙwallar tausayinsa ga kuma soyayyyar sa data ƙara shiga zcyarta, ɗaga idanunsa yay suka haɗa ido zaro mata nasa idon yay tsoran da taji yasa ta saki ƙara da sauri kuma tai flat ɗin data kwana tana kuka, wani ƙawataccen Murmushi ya saki yana jan gemunsa tsaki Mami tayi tace "An kawo mana mahaukaciya dai" nan take launin fuskarsa ya sauya hanunsa yasa ya zame mata hannun daga Wheelchair da take ƙoƙarin turawa, gabansa ta dawo ta sanya dukkan tafin hannunta ta tallafo fuskarsa tace "My Sweet Imam me Maminka tayi maka kuma?" Banza yay mata yana zame fuskarsa zata ƙara taɓa sa yace "Stop please" ya faɗi hakan yana danna abinda ke jikin Wheelchair kai tsaye ya nufi flat ɗinsa. A dai-dai inda sautin kuka yake fitowa ya tsaya cikin ƙaramin lokaci kuma ya gane muryar mai kukan domin baya tunanin akwai abinda zai manta wanda ya shafe ta, runtsa idanunsa yay kana ya ƙarasa cikin bedroom ɗinsa. Bayan asar Arjun ne ke driving sai Sheikh dake gefensa yasha wata shadda wagambari amy color sai wula zanna yay kyau sosai, dawowarsu kenan daga gidan