Showing 156001 words to 159000 words out of 239422 words
Chapter 53 - Nakasa Ba Kasawa Bace Part 2 Complete by Aisha Aliyu Garkuwa .txt
ce ba karuwarsa bace kamar Dina da ya Amir so dan Allah ki sawa ranki salama, ki fauwalawa Allah lamarinki kamar forko, shi zai ɗaga daraja da kimarki a wurin mijinki wlh Abban Adeel yana sonki".
Dai-dai lokacin suka isa ƙofar gidan Samira, cikin sanyi Ameena tace.
"In sha Allah zan kula dan wlh ni kaina nasan Abban Adeel yana son farin cikina".
Kai Samira ta jinjina tare da cewa.
"Yauwa ƙawata ki kula gudun kada ki ɓarar da damarki sai gobe in mun haɗu zamu ƙara tattaunawar zan baki shawarwarin yadda zaki samu sauƙin kishin kuma ki yarda yana sonki."
Cikin jin daɗi Ameena tace.
"To Allah ya kaimu gashi yauma itace dashi gobema itace sai ran monday zan ƙarɓeshi kuma kinga ran monday ɗin munada off zan wuni a gida kusa da Mijina da ɗana, Allah dai ya bani ƙarfin hali irin naki, amman in sha Allah bazan sake tayar da hankali naba".
Amin Amin Samira tace lokacin data fita,
Kai tsaye cikin gidanta ta wuce, ita kuma Ameena taja motarta ta koma gida.
Koda Ameena ta dawo nono ta bawa Adeeli take kuwa yayi shiru kamar ba shine ya wuni koke-koke ba.
Anan sashin Ummin tayi magriba, tana idarwa kuwa ta tattara komanta ta wuce sashinta, dan yau ba itace da girki ba Zaleeha ce, shiyasa gaba ɗaya komai keneman dawo mata sabo donma tayi dace da shawarwari Samira aminiya ta gari mai imani ta nusar da ita ta koyi kauda ido kan miji da kishiyarta kada ta tsananta binciken cewar sai ta gano waya fi so a cikinsu ta kuma cire zargi, to Alhamdulillah kuma ta gamsu da shawarwarin Samira tasirin ƙawa ta gari kenan.
Zaleeha kuwa koda ta idar da sallan isha, wani haɗaɗɗen riga da wando me taushin gaske tasa, rigan irin mai hannun vest ɗinnan ne, tabi gaba ɗaya surar jikinta ta lafe, har takai ga ana iya hango shatin nipples ɗinta, dan batasa bra ba, wandon kuwa meɗan faɗi ne, amma duk da haka bai hana mayataccen hips ɗinta bayyana ba, dogon gashinta ta tubke sannan ta feshe gaba ɗaya jikinta da turare, wani irin kasala haɗi da bacci takeji, saboda hakane ma yasa batajin zata koma sashin Ummi, hayewa saman gadonta tayi, tare da jawo hand bag ɗinta, diary milk ta ɗauko, tare da ɓarewa, kwanciya tayi tana ɗan gutsuransa kaɗan kaɗan, wayarta ce ahannunta tana ɗan kallon hotuna a IG wanda duk hotunan Hamma Saif ne take gani wanda Hayatuddeen ke sakasu kamar ba gobe ta rasa me take ji a kanshi a haka ko mintuna 15 batayi ahaka ba, bacci ya ɗauketa, da diary milk riƙe ahannunta, takarasa akusa da bakinta, wayarta kuwa tabar data akunne saƙonni sai shigowa suke. Ɓangaren Saifuddeen kuwa saida akayi sallan isha kafun yake shigowa cikin gidan, sashin Umminsa yaje suka ɗan taɓa hira dasu Ahmad, sai wajen ƙarfe 9 ya nufo part ɗin nasu, kaitsaye ɗakinsa ya wuce, wanka yayi tare da shirya kansa cikin wasu kayan bacci masu taushi, sun kuwa yi masa kyau sosai, turarensa maidaɗin ƙamshi ya fesa, sannan ya nufi ɓangaren Ameena. Ahankali ya murɗa ƙofar ɗakin ya shiga, tana nan zaune akan gado, ko kayan bacci bata saba, ta zuba uban tagumi, ga kuma idanunta da suka cika da ƙwalla, gaba ɗaya komai bayayi mata daɗi, sam arayuwarta bata ƙaunar taga ranan girkin Zaleeha ya zagayo, saboda batason abun dazai nesanta ta da Saifuddeen ko kaɗan. Ganin yanda tayi tagumi ne yasashi ƙarasowa cikin ɗakin, hannun da tayi tagumin dashi ya sauƙe ƙasa tare da ɗan shafa gefen fuskarta, cikin body language ɗinsa ya dubeta, tare dayi mata alaman cewa. "Meke damunta?" Kallo ɗaya tayi masa ta kawar da kanta gefe, zuciyarta duk ba daɗi, sanin cewa idan ya matsa mata da tambaya, zata sake bayyana kishinta ƙarara, yasashi ɗan ƙarasawa ya sakarwa Adeel kiss agoshinsa, hannunta ya kamo, tare da ɗan lumshe idanunsa, alama yayi mata kan cewar saida safe, sannan ya juya akalan kekensa, tana kallonsa ya fice daga cikin ɗakin.
Samun kanta tayi da danne kishinta, kan gado ta faɗa tare da jawo pillow ta rungume tana fidda zazzafan numfashi.
Shikuwa Saifuddeen yayi hakanne dan shine abun da yafi dacewa, saboda yasan tsayuwarsa awajen nata, tamkar ƙara mata wutar kishi ne acikin ranta.
Ta cikin falonsa yabi, inda ya shiga sashin Zaleehan, dama baiyi tunanin ganinta acikin falo ba, hakan yasashi wucewa ɗakinta, ahankali ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, sassanyan ƙamshin turare da kuma sanyin AC ne ke tashi acikin ɗakin, ɗan lumshe idanunsa yayi, tare da buɗewa, hangota da yayi akan gado ne yasashi ɗan ƙarasawa. Idanunsa ya zuba mata, tundaga kan ƴar yatsar ƙafarta yake kallonta, har ya gangaro zuwa ƙirjinta, wanda rabin breast ɗinta suka fito ta saman rigar, ga kuma shatin nipples ɗinta da suka bayyana kansu, ta cikin rigar, wani irin zubawa yaji tsikar jikinsa nayi, take yaji jijiyar jikinsa na neman miƙewa tsaye, saboda sexy dress ɗin dake jikin Zaleehan ya isa hautsuna tunanin duk wani ɗa namiji me lafiya, ahankali yaɗan lashi lips ɗinsa, tare da kai dubansa ga fuskarta, baccinta take cikin nutsuwa, ga kuma diary milk ɗin dake riƙe ahannunta, wani kyakkyawan murmushine ya suɓuce masa, saboda ya lura bata shiryawa baccin ba ya ɗauketa, gab da ita ya ƙaraso, tare da kai hannunsa yaɗan zare diary milk ɗin dake hannunta, ganin cewa chocolate ɗin yaɗan ɓata mata baki ne yasashi, kai hannunsa saman tausassun ƙaɓɓanta, yaɗan goge mata, wayarta ya ɗauka, tare da kashe mata datan, ya ɗaura mata wayar akan bedside, hannu yakai yaɗan shafi lallausan gashinta da ya watse akan pillow, anutse ya ɗan haɗe mata gashin nata waje ɗaya, idanu ya tsurawa kyakkyawar fuskarta, ji yake kaman ya buɗe cikin jikinsa ya sata aciki, kayan sunyi mata matuƙar kyau, ga kuma kyawawan breast ɗinta dake mugun ɗauke hankalinsa, saman breast ɗin nata yaɗan shafa, wani irin zut zut haka yaji mararsa nayi masa, take duk wani kuzarinsa ya kau, ahankali yaɗan ranƙwafo da kansa, kiss ya manna mata agoshinta, tare da ɗan shafa gefen fuskarta, jikinsa amatuƙar mace ya jawo blanket ya rufa mata, rage mata hasken wutan ɗakin yayi, sannan ya juya ya fice, gaba ɗaya jikinsa amace yake, wani irin fitinannen sha'awarta ne ke taso masa badan yasa a ranshi sai yaga ta nuna begenta gareshi zai kusancetaba tabbas da yau zai rabata da budurcinta, kaitsaye ɗakinsa ya koma ya kwanta, duk yanda kuwa yaso bacci ya ɗaukesa abun ya gagara, dan wani irin feeling ɗin Zaleehan yakeji, haka ya dinga juyi akan gado yana lumshe fitinannun idanunsa, sai wajen ƙarfe ɗaya kafun bacci ɓarawo ya sace shi.
Ameena kuwa, yaƙi tasha da zuciyarta harta godewa Allah, babu abun dake ɗaga mata hankali kamar yanda zuciyarta, ke raya mata cewar. "Yanzu haka Saifuddeen ɗin nacan jikin Zaleeha, sai take tuno yadda ta samu Ya Amir da Dina sai tanaga yanzu shima Saifuddeen da Zaleeha suna can manne da juna."
wannan tunanin shike ƙara dagula mata lissafi. Haka nan ta tsinci kanta da cewa.
"To sai meye ba matarsa bace, in sha Allah daga yau bazan sake sawa raina damuwar kishin baiwar Allah nan da take son ɗanaba".
a haka tayi bacci cikin sanyin rai. Washe gari da safe kuwa, Zaleeha ita kaɗai ta shiga kitchine tayi musu break fast, simple foods kawai tayi musu, sai kuma chicken egg rolls.
Ko awajen breakfast ɗin gaba ɗaya fuskar Ameena babu wata alamar damuwa, haka takejin zuciyarta a sauƙaƙe, cin abincin kawai take hankalin na kan wayarta.
Saifuddeen kuwa duk yana lure da ita, har acikin ransa yana fatan Allah ya ragewa Ameenan kishinta, dan yaga alama da kishin na sawa tana takura kanta da yawa, gashi kuma wacce take kishin dan ita, batasan ma tanayi ba, wannan shine sakai a wahala sai dai ya lura da nitsuwar zuciyarta.
Tun kafun sugama break fast ɗin ta miƙe dan tafiya wajen aiki.
Ya lura kamar bata fiyo son zaman gidanba yanzu tafi jin daɗin tafiya aikinta in ba ran girkinta bane.
Cikin kula Saifuddeen ya dubeta cikin body language ɗinsa yace. "Ta tafi da Adeel, dan jiyama da tabarsa kuka yayi tayi."
Gane hakan yasa Zaleeha ɗan marairaice fuska dan kwata kwata batason atafi da Adeel ɗin.
Ameena kuwa ɗan jim tayi tana kallonsa, dan itama bawai tanason tafiya da Adeel ɗin bane, saboda idan taje dashi ma baya barinta tayi aikinta yanda ya kamata. Ummi ce tace.
"A'a meyasa za a tafi dashi, dan kawai yayi kuka jiya, ai baizama lalle yau yayi ba." Cikin zumuɗi Zaleehan tace.
"Eh kuma ma idan yayi kukan zan dama masa madaransa yasha, nasan ma bazaiyi kuka ba, jiyan ma halan wani abune ke damunsa, dan naɗanji jikinsa da zafi kaɗan, ko kuma kunnensa ne keyi masa ciwo."
Tsumammun idanunsa ya zuba mata, da hannu ya nunata cikin body language ɗinsa yace. "Idan yana kuka kuwa, kyasan yanda zakiyi dashi."
Kanta ta jinjina masa, alaman.
"Eh taji ta yarda."
Kansa ya jinjina, tare da ɗan sakin ɓoyayyen murmushi me ɗauke da ma'anoni kala-kala. Ameena kuwa ganin haka yasa, taɗan saki murmushin yaƙe, har acikin ranta tanajin daɗin yanda Zaleehan ke nunawa Adeel ɗin ƙauna, saidai kuma babu yanda ta iya da kishin dake cikin ranta, batare da ta karɓi Adeel ɗin ba, tayiwa su Ummi sallama, cewar ta wuce wajen aiki. "Adawo lafiya."
suka mata sannan ta fice daga cikin falon. Ahaka dai suka kammala break fast ɗin, kowa yayi nasa ɗakin, Zaleeha kuwa anan falon Ummi ta zauna tana yiwa Adeel ɗin wasa, sai ƙyalƙyala dariya yake, har dimples ɗinsa na lotsawa. Hayatuddeen ne yazo ya zauna sunayiwa Adeel ɗin wasa. Saifuddeen kuwa wanka yasakeyi, bayan yagama kimtsa kansa ne yayiwa sule driver magana suka fita, kasancewar duk kwana biyun nan suna da meeting. Zaleeha kuwa yau gaba ɗaya asashin Ummi ta wuni, ita da Raleeya ne suka ɗaura dinner, koda suka kammala tuni yamma ta rufa, dan kusan ƙarfe 5 ake nema, nan wajen Ummi ta ajiye Adeel ɗin, tare da cewa Ummi zataje tayi wanka. Ai kuwa tana fita daga falon Ummin Adeel yasaka kuka, Ummi ne ta ɗaukeshi tana ta faman rarrashinsa amma fir yaƙiyin shiru. Zaleeha kuwa tana isa bedroom ɗinta, ta soma rage kayan jikinta, wani ɗan mini towel ta ɗaura ajikinta, sannan ta shige bathroom, ruwan wanka meɗan ɗumi ta haɗawa kanta, tare da zuba wani irin fitinannen turare acikin ruwan, wankanta tayi cikin nutsuwa tare da ɗauro alwalan magriba, wani baby pink towel ta ɗaura ajikinta, wanda iyakansa cinyarta, haka ta fito daga cikin bedroom ɗin tana tsane jiƙaƙƙen gashin kanta.
Saifuddeen kuwa tun safe daya fita sai yanzu yake dawowa cikin gidan, kaitsaye sashin Ummi ya nufa, yana zuwa kuwa yasamu Ummi nata zirya afalo Adeel na ɗauke akan kafaɗanta, sai kuka yake, rarrashin duniya kuwa tayi masa ya ƙiyin shiru. Ummi naganinsa tace. "Yauwa Saifuddeen, wallahi Adeel tun ɗazu yaƙiyin shiru, nayi rarrashin amma abanza, anya kuwa ba wani abune ke damunsa ba?." kansa ya girgiza alaman rashin sani, tare da kai hannu ya amshi Adeel ɗin, jijjigasa yasomayi amma yaƙi daina kukan, kallon Ummi yayi cikin body language ɗinsa yace.
"Ina Zaleeha?." "Zaleeha taje wanka, amma nasan yanzu zata shigo."
Kansa ya jinjina, sannan ya juya akalan kekensa, yana rungume da Adeel ɗin haka yafice daga cikin falon. Kaitsaye sashin Zaleehan ya nufa, dan har yanzu Adeel ɗin kuka yake.
Zaleeha kuwa tsaye take agaban mirror tana tsane gashin kanta, yayinda towel ɗin jikinta yasoma ɗan warwarewa. Ahankali ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, dai-dai nan Adeel ya saka wani sabon kuka, amatuƙar razane Zaleeha ta juyo sakamakon jin kukan Adeel, ganin Saifuddeen ɗin rungume da Adeel yasa gaba ɗaya duk ta ruɗe, gaba ɗaya mantawa tayi cewar towel ne kaɗai ajikinta, cikin hanzari ta nufosu, hannu tasa ta amshi Adeel ɗin tana ɗan bubbuga bayansa, tare da ɗaurasa akan kafaɗanta, cikin kulawa tace.
"I am so sorry papyna, natafi nabarka ko, am sorry bazan sake ba." ɗan bubbuga bayansa take tana jijjigasa, amma hakan baisa ya daina kukan ba, hankalinta aɗan tashe ta buɗe fridge, ruwa taɗan ɗiba ta bashi yasha, still kukan nasa ƙaruwa yayi, hankalinta amatuƙar tashe ta ɗauki flask tare da haɗa masa madaransa aɗan ƙaramin cup ta bashi, sha ɗaya yayi ya ɗauke kansa, tare da sa mata ihu, haryana ciccilla ƙafa, hankalinta ne yayi matuƙar tashi, dan taga kaman Adeel ɗin na koƙarin shiɗewa, gaba ɗaya ta manta cewar daga ita sai towel ajikinta.
Saifuddeen kuwa idanu ya zuba mata, ya kasa koda kiftawa, sosai body structure'n ta ke tafiya da tunaninsa ga kuma kukan ɗansa. Hankalinta aɗan tashe ta ɗago ta kalli Saifuddeen ɗin, ɗan marairaice fuska tayi, tare da nuna masa Adeel ɗin, tace.
"Hamma Saif me yakeso? Meya sameshi? Faɗuwa yayi ne?".
dan kuka yaron yake sosai.
Baki ya taɓe tare da ɗaga mata kafaɗa, alaman.
"Ohon miki kisan yanda zakiyi dashi, ai dama nafaɗa miki, kikace kinji kin gani."
Shagwaɓe fuska tayi, take idanunta suka ciko da ƙwalla,
jikin Adeel ɗin ta shiga tattaɓawa, wai ko wani abune keyi masa ciwo, anan kan gado ta zauna tare da rungume Adeel ɗin ajikinta tuni hawayenta sun fara zubowa, cikin tausayawa tace.
"Bani number Momynshi in kirata ta dawo".
Ahankali ya ɗan turo kekensa, har ya ƙaraso gab da ita,
Ido ya zabuma mata ganin gaba ɗaya a gigice take,
hannunsa yakai jikinta, tare da kunce towel ɗin dake ɗaure kan ƙirjinta. Cikin tsananin tsoro da firgita haɗi da mamaki ta zaro Idanunta amatuƙar tsorace tana kallonsa, ƙoƙarin janye jikinta baya tasomayi tare dasa hannu zata janye towel ɗin ta rufe ƙirjinta,
hannunsa yasan ya damƙi nata hannun, wuƙi-wuƙi tayi da idanunta gaba ɗaya jikinta rawa ya ɗauka,
Shi kuwa Hamma Saif tallafo kan Adeel ɗin yayi da hannunsa ɗaya, ba zato ba tsammani taji ya sa hannunshin ɗaya ya kamo nononta tare da manna mata bakin Adeel akan nipples ɗinta.
Wani irin gigitaccen zillo Zaleehan, tayi jin Adeel ɗin ya cabke bakin nononta yana yi mata wani irin fitinenne tsotsa.
Idanu Zaleeha ta kuma zarowa afirgice, kanta ta soma girgiza tare da ƙoƙarin ƙwace jikinta, riƙeta yayi ƙam, cikin body language ɗinsa yace.
"Sai kiyi ai! dole sai yasha, wayace ki hana mamansa ta tafi dashi, kinsan abun da yakeso ai zaki zauna ki sani a gaba yana kuka kina min kuka".
Gaba ɗaya jikinta ne ya ɗauki rawa da karkarwa sai zazzare idanu takeyi tuni wani fitinenne zufa ya karyo mata, hannunta taketa yarfawa tare da fidda sautin.
"Hshhhhhhh wayyo Hamma Saif wlh zafi dan Allah ka bari, wlh bazan sake cewa mamanshi ta barshi ba".
Adeel kuwa ƙam ya kama nipples ɗin nata yana ta sha, duk da cewar babu abun dayake zuƙowa, amma bai sake mata nonon nata ba, sai ajiyar zuciya ya ke sauƙewa,
idanunta ta rumtse tare da cije laɓɓanta, wani iri takeji ajikinta, yayinda zufa keta keto mata, ko ina ɗinta rawa yake ga riƙon da Hamma Saif ɗin ya mata bana wasa bane, cikin mintunan da basu wuce 7 ba bacci ya ɗauki Adeel, ganin haka Saifuddeen daya kafeta da mayun idanunsa, ya