Showing 129001 words to 132000 words out of 239422 words

Chapter 44 - Nakasa Ba Kasawa Bace Part 2 Complete by Aisha Aliyu Garkuwa .txt

06 Dec 2024

11848

ɗan ɗaga kansa yayi ya kalli agogon dake saƙale ajikin bangon ɗakin. Ganin 3:30 pm yasanyashi ɗaukan wayansa da kuma laptop ɗinsa, ahankali yake tafiyar da wheelchair ɗinsa har ya fice daga cikin ɗakin, sam bayaso ya makara dan ƙarfe 4:00 pm daidai zasu gudanar da meeting acan ƙungiyarsu ta JONAPWD.


Cikin nutsuwa ya fito compound ɗin gidan, nan ya iske Sule driver da kuma Bala megadi suna al'walan sallan la'asar, cikin body language ɗinsa yayiwa Sule driver alaman cewa yafito da mota zasu fita, kai Sule driver'n ya jinjina masa alaman "To." saida ya jira suka gama alwalan, sannan sule driver ya fito da motar, ya shiga ayarinsu suka wuce masallaci.
Koda suka idar da sallan azkar yayi, sannan ya tashi ya hau kan kekensa, ganin haka yasa shima Sule driver miƙewa tsaye.
Shi ya buɗewa Saifuddeen ɗin murfin motar ya shiga, sannan shima ya zaga ɓangaren driver ya zauna, Bala mai gadi ne yayi musu adawo lafiya, sannan sule yaja motar suka tafi, kai tsaye ƙungiyar Jonapwd ɗin suka nufa.


Acan ɓangaren Ummi kuwa, bayan sunyi Sallan la'asar, Raleeya ne ta wuce kitchine dan ɗaura dinner.
Zaleeha kuwa koda ta idar da sallan falo ta fito, ganin Raleeya a kitchine yasa itama ta nufi kitchine ɗin, amsan girkin tayi tare da cewa. "Raleeyan taje ta huta." duk yanda Raleeya taso suyi aikin tare Zaleeha taƙi, dole haka Raleeya ta koma falo ta zauna ita kuma Zaleeha ta ci gaba da aikin.
Tana nan acikin kitchine ɗin, Ameena ta dawo daga wajen aiki, ɗakin Ummi tafara zuwa ta gaishe da ita, sannan ta wuce ɓangarenta.
Zaleeha kuwa ana ƙiran sallan magriba ta gama girke-girken nata, nan kan dinning ta jere abincin wanda gaba ɗaya ƙamshinsu ya cika falon, Hayatuddeen dake zaune afalo kuwa sai faman haɗiye yawu yake, koda tana girkin ya shigo kitchine ɗin yafi sau uku, duk shigansa kuwa sai ya buɗe tukunya ya ɗanɗani stew ɗin da Zaleehan ta haɗa, wanda yaji naman kaji, ganin yanda yake lashe mata tukunya ne yasa ta saki murmushi, nan ta zuba masa pepper meat acikin wani ɗan plate, tare da kama hannunsa ta turasa falo, dan yaƙi ya barta tayi aikinta cikin nutsuwa.
Hayatuddeen kuwa dama abunda yake nema kenan, haka ya bararraje ƙafafu yana cin pepper meat ɗin, sai faman kaɗa kai yake yana santi.
Yana gamawa kuwa ya wuce masallaci.
Itama Zaleehan ɗaki ta wuce, wanka tayi sannan ta ɗauro al'wala, wani body lotion ta shafa, tare da fesa turaren white oud ajikinta, take kuwa gaba ɗaya jikinta ya gauraye da ƙamshi.
Wata ƴar siririyar pencil gown me stones ta sanya ajikinta, sosai kuwa rigan tayi mata kyau, dogon gashinta wanda ya kwanto har gadon bayanta ta ɗaure da ribbom sannan ta ɗaura hijab akan kayan, nan kan darduma ta hau tare da tada Sallah.


Acan ɓangaren Saifuddeen kuwa, kusan awa biyu suka ɗauka a Jonapwd suna meeting, koda suka kammala kowa ya watse, hira suka ɗan taɓa shida Ishaq kafun ya shiga mota suka kamo hanyar gida, anan masallacin dake jikin gidan sukayi sallan magriba, koda suka idar da sallan zama yayi acikin masallacin, har lokacin sallan isha ya cika, bayan sun idar da sallan ne ya sanya hannuwansa ya dafa ƙasa, ahaka yake ɗan jan jikinsa har ya ƙarasa bakin ƙofar shigowa masallacin inda anan yake aje wheelchair ɗinsa, yana hawa kuwa controlling wheelchair'n yayi, inda ta soma tafiya da kanta, dai-dai zai shiga gida ne suka haɗe da Ahmad, wanda shima daga masallacin yake, yawan jama'a shiyasa basuga juna ba, saman keken Saifuddeen ɗin ya kama, haka suka nufi cikin gidan, cikin body language ɗinsa ya ke bawa Ahmad ɗin labarin meeting ɗin da sukayi yau.
Ahaka har suka ƙarasa part ɗin Ummi, anan cikin falon kuwa, Ummi ne da kuma Raleeya, sai Hayatuddeen dake faman turo baki, waishi adole yunwa yakeji, kuma Ummi tace bazaici abinci ba sai yajira kowa yazo sun haɗu a dining area, dan daga yau gaba ɗaya ahalin gidan atare za suna cin abinci, daga kan break fast har zuwa dinner, lunch ne dai kowa zai iyayi aɗakinsa.
Shigowar su Hamman nashi ne yasa ya ɗanji sanyi aransa, dan yasan yanzu Ummi zatace suje suci abincin, shikansa yasan idan aka tsananta bincike ba yunwa yake jiba, kwaɗayine kawai ke damunsa, musamman ma yanda yaga yau Adda Zaleehan ta girka musu abubuwan daɗi kala kala.


Cikin girmamawa Ahmad yaɗan rusuna ya gaishe da Ummi, dan yau tun safe daya fita agidan baidawo ba sai yanzu, fuska asake Ummi ta amsa masa, tare da tambayansa ya aiki.
Ya amsa mata da "Alhmdlh."
Saifuddeen kuwa ƙarasowa wajen Ummin nasa yayi, tare da ɗan shafa gefen fuskarta, cikin kulawa haɗi da tsantsar soyayya yaɗan ɗaura kansa agefen kafaɗanta, murmushi Ummin tayi tare da shafa lallausan sumar kansa, tabbas yau yafaranta mata rai daya kai Zaleehan gida, har kuma Baba Malam ya yafe mata, cikin kulawa tace. "Ya meeting ɗin naku?" idanunsa yaɗan lumshe tare da jinjina kansa alaman,
"Komai ya tafi yanda akeso."


Jin sallaman Ameena ne yasasu duk suka ɗago kai suka kalleta, sanye take da riga da sket na atamfa, yayinda ta zuba meckup akan fuskarta, babu laifi ta kyau sosai, sannan kayan ma sunyi mata kyau, Adeel ne ɗauke a kafaɗanta, haka ta ƙaraso cikin falon, sai baza ƙamshi take, dan wani turare me shegen ƙarfi tasa, hwanda yasa gaba ɗaya falon ya ɗauka, murmushi ta sakarwa Saifuddeen wanda ke kallonta, shiɗin ma murmushin yayi mata, Ummi ne ta amshi Adeel tana yi masa wasa, Ameena kuwa nan kusa da Raleeya ta zauna, bayan ta gaishe da Ahmad, cikin sakin fuska kuwa ya amsa mata, harma da tambayanta ya aiki, tana murmushi ta amsa da "Alhamdulillah."


Hayatuddeen ne ya miƙe tsaye, tare da duban Ummi, cikin shagwaɓa yace.
"Ummi shikenan ai tunda dai kowa yazo ai sai muje muci abincin ko?".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"To acici."
Shiya fara zama akan dinning ɗin, sannan Ahmad da Saifuddeen suka rufa mishi baya dan duk yunwa sukeji, babuma kamar Ahmad wanda tun lunch da yayi baisake sa komai abakinsa ba sai ruwa.
atare Raleeya da Ameena suka ƙarasa kan dining ɗin, nan kujeran dake kusa dana Saifuddeen Ameena ta zauna, Raleeya kuma ta zauna akusa da Ahmad ɗinta, wanda keta jifanta da wani irin mayataccen kallo, ƙasa-ƙasa yake lumshe mata idanu, murmushi tayi tare da ɗan sa hannu ta muntsineshi, dan sarai ta gane me yake nufi, takarance sa tsab, da ta ga yana mata irin wannan kallon, to matsanancin feeling ɗinta yakeji.


Ummi ne ta ƙaraso nan kan dining ɗin, rungume da Adeel ajikinta, cikin kulawa tace. "Hayatuddeen jeka ƙira Zaleeha tazo taci abinci." Jin cewa Zaleeha zai ƙira yasa batare da ya musa ba ya nufi ɗakin nata, nan Ummi taja kujera ta zauna.
Ameena kuwa jin an ambaci sunan Zaleeha yasa taji wani abu ya tokare mata ƙirji, Allah ma yasani tana matsanancin kishin Saifuddeen, shiyasa ko sunan Zaleeha bataso taji anƙira, bawai tsanan Zaleeha takeji aranta ba, zallan kishine kawai sai kuma haushinta da takeji.


Zaleeha kuwa tunda tayi sallan isha tana nan zaune akan sallayan bata tashi ba, suratul falaq take karantawa acikin ranta, dan nemawa Adda Maryam dama duk wani musulmin daya rigayemu gidan gaskiya gafara awajen Allah.
Shigowar Hayatuddeen ne yasa taɗan ɗago kanta ta kalleshi, cikin kulawa yace.
"Adda Zaleeha kizo muyi dinner inji Ummi."
Kanta ta jinjina masa, sannan ta soma ƙoƙarin tashi daga kan sallayan, hijab ɗin jikinta ta cire, nan cikin drawer'nta ta ciro wani ɗan mayafi mai kauri, ta yafa ajikinta, sosai tayi kyau, dan kalan mayafin ya karɓi kyakkyawar fuskarta, duk Hayatuddeen na tsaye ajikin ƙofa yana kallonta, ganin tana ƙoƙarin fitowa batare da ta saka turare ba, yasashi kamo hannunta suka koma cikin ɗakin, turaren daya saya mata ya ɗauka ya ƙara fesa mata, murmushi ta saki tare da cewa.
"Kaidai Hayatuddeen rigima ne dakai, ɗazu fa na fesa turaren kuma har yanzu akwai ƙamshin ajikina."
Kansa ya jinjina tare da cewa.
"Eh naji ai, amma so nake ki ƙara".
Murmushi kawai tayi sannan tabi bayansa suka fice daga cikin ɗakin.


Daddaɗan Ƙamshin turarenta shiya fara ziyartan hancinsu, ahankali yaɗan lumshe idanunsa tare da haɗiyan wani yawu daya tsaya masa amaƙoshi, Ameena kuwa da sauri ta juyo dan bakaɗan ba ƙamshin ya tafi da ita, idanunta na sauƙa akan Zaleeha taji gabanta ya faɗi, saboda wani irin kyau da taga Zaleehan ta ƙara, kau da kanta tayi tare da ƙara matsaya kusa da Saifuddeen, har jikinsu na gogan na juna, Zaleeha kuwa cikin nutsuwa ta ƙaraso kan dining ɗin, fuskarta ɗauke da ɗan murmushi tace.
"Ummi barka da dare." Murmushi Ummin tayi, tare da cewa.
"Yauwa dai Zaleeha sannunki, dan kema yau kinsha aiki, daga samun sauƙi kuma sai shiga kitchine".
ɗan murmushi Zaleehan tayi tare da miƙa hannu ta karɓi Adeel, dai-dai lokacin Saifuddeen ya buɗe idanunsa ya sauƙesu akanta, murmushin daya bayyana dimples ɗinta tayi, tare da ɗan manna fuskar ta da ta Adeel ta sakar masa kiss akan bakinsa, cike da ƙaunar yaron tace.
"I miss you my sweet papy na."
Baki Adeel ɗin ya wangale yana yi mata dariya.
Ɗan lumshe idanu Saifuddeen yayi, tare da lasan lips ɗinsa, dan kiss ɗin da Zaleehan tayiwa Adeel haka yaji kaman shi tayi wa, a ranshi yace.
"Uhummm da yadda akeson Adeel haka akeson Abbanshi da duniya tai mana daɗi, kalli yadda take son yaron kamar tana son ubanshi".
Kujera Zaleehan taja ta zauna, wanda kuma hakan yasa suke facing ɗin juna ita da Saifuddeen ɗin, ɗan kallon Ahmad tayi cikin muryarta me ɗauke da sanyi tace.
"Barka da dare Ya Ahmad."
Hakanan yaɗanji tausayinta ya kamasa, fuskarsa yaɗan saki sannan ya amsa mata.
Fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli Ameena wanda keta ƙara shigewa jikin Saifuddeen, murmushi tayi mata tare da cewa.
"Ummun Adeel sannunki da dare."
Duk yanda Ameena taso daure kishinta akan Zaleeha abun naneman fin ƙarfinta, dole haka ta daure ta ƙaƙalo murmushi, cikin muryarta da ta maƙale tace.
"Yauwa."
Ummi ne tasa hannu ta amshi Adeel ɗin, cikin kulawa tace.
"Kawo sa yanzu saiki fa ke dashi kiƙi cin abinci, nasan halinki sarai, tashi ma kiyi seving ɗin mu."
Murmushi Zaleehan tayi tare da miƙewa tsaye, food flasks da kuma plates ɗin ta jawo gabanta, cikin nutsuwa tashiga zubawa kowa abincin,
Kyawawan idanunsa ya zuba mata, a ƴan kyawawan yatsunta yake kallo, komai tanayinsa ne acikin nutsuwa.
Ameena da gaba ɗaya haushin Zaleehan ya cika zuciyarta, ɗan kallon Saifuddeen ɗin tayi, ganin ya ƙure hannun Zaleehan da ido, yasa taji kaman ta tashi awajen, wani baƙinciki da kishine suka tokare maƙoshinta, gaba ɗaya da zuwan Zaleehan sai duk taji ta raina kanta, hakanan taji babu ma irin ƙamshin da ta tsana kamar ƙamshin oud ɗin da ke jikin Zaleeha'n.
Zaleeha kuwa sam hankalinta ma ba akansu yake ba, cikin nutsuwa ta gama seving ɗin kowa, ɗan matsowa gabansa tayi ta ajiye masa nasa abincin, komawa tayi ta zauna, tare da jawo plate ɗin da ta zubawa kanta abinci aciki, dubanta Ummi tayi cikin kulawa tace.
"Zaleeha ɗan wannan abincin shi zaki ci kuma har ki ƙoshi".
Murmushi ta ɗanyi, tare da cewa.
"Eh Ummi, amma idan ban ƙoshi ba zanci na Hayatuddeen."
Kai Hayatuddeen ya jinjina, murmushi kawai Ummi tayi, haka suka shiga cin abincin.
Loman farko da yayi, ya lumshe kyawawan idanunsa, dan kuwa sosai yaji ɗanɗanon abincin abakinsa, tabbas Zaleeha ta iya girki sosai, wanda har yau yana mamakin a ina ta koyo girki kala kala haka.
Abinda bai saniba ƙabilar su mama sunyi zarra a iya girki kuma Zaleeha Mama ta gado a iya girki kana ta samu horon Mamy iya sarrafa abin da za'aci.


Ameena ma tun aloman farko da tayi, gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, dan kuwa taji ɗanɗanon abincin ya banbanta da wanda Raleeya ta saba girkawa, maganan Hayatuddeen ne ya katse mata tunani, inda yace.
"Kai Adda Zaleeha wallahi kin iya girki."
Jin cewar Zaleehan ne tayi girkin yasa duk taji abincin yafita aranta, domin Zaleehan iya girki nesa ba kusa ba.
Ahmad shi kansa yau ya yaba da abincin dan buɗe cikinsa yayi yaci sosai.


Zaleeha kuwa ahankali take ɗan tsakuran abincin tana kaiwa bakinta, yanayin yanda take tauna abincin cikin nutsuwa shi yasa Saifuddeen yake ta faman satan kallonta.
Ganin haka yasa Ameena tsaida cin abincin tayi shiru, hakanan taji idanunta na neman kawo ruwa, ɗan juyowa Saifuddeen yayi ya kalleta, ganin yanda tayi shiru ne, yasa ya ɗan tsiyayi drinks acikin cup, hannunsa yasa miƙa mata cup ɗin,
Rau-rau tayi da ida nunta hawayen kishi na gab da zubo mata,
Tuni Saifuddeen ya karanci Ameena tanada masifar kishi, har ga Allah yasan ta tsananin sonshi amman yana mata addu'a Allah ya sassauta mata zafin kishinta.
Gani tana gabda zubda hawayene yasa yayi niyar bata abu mai sanyi tasha zataji sassaucin abinda takeji a ranta.
A hankali yakai cup ɗin drinks ɗin bakinta, ɗan shagwaɓe masa tayi, tare da buɗe baki ya bata drinks ɗin, saida tasha rabin cup ɗin sannan ya ajiye, da ido ya nuna mata filet ɗin alamun taci abincin,
kai ta sunkuyar cikin sanyi tasa hannu ta ɗauki spoon ɗin madadin taci sai tayi ta wasa da cikalin.
Numfashi ya ɗan fesar kana yasa hannunshi akan nata,
hannu dake gefenshi murza hannu yake ɗanyi a hankali alamun taci. itakam dama abun da take nema kenan, saboda haka saita biye masa, duk dan saboda tanason kawar da hankalinsa akan Zaleeha, Kallo ɗaya Ummi tayi musu ta watsar tare da girgiza kanta, dan ta fahimci cewa sam Saifuddeen bayajin kunyarta, Ahmad kuwa murmushi kawai yayi yaci gaba da cin abincinsa.
Raleeya ma ƙasa tayi da kanta, hakanan taji wani iri, sam batason abun da zaisa Zaleeha taji babu daɗi aranta.
Hayatuddeen kuwa baki ya sake yana kallonsu, har acikin ransa yana mamakin dalilin dayasa ayanzu Hamman nasa ke ƙoƙarin nunawa Ameena kulawa agaban kowa.


Itakam Zaleeha kallo ɗaya tayi musu ta maida kanta ƙasa , kwata kwata abun nasu baya damunta, wani lokaci ma sai abun da sukeyi ɗin yana bata dariya, dan ta fahimci kamar Ameena'n bata iya sirranta soyayyarta ba, amma ganin ba huruminta bane, shiyasa ma takeyin kamar bata gani ba.


Saifuddeen kam har acikin ransa da yakeyin hakan dan sassauta kishin Ameena, kana a wani sashin kuwa da gaggan yakeyi dan kawai Zaleehan taji wani abu aranta, Ameena kuwa gaba ɗaya ta sakankance, shiya dinga yi mata wani irin kallo, tana mejin wani irin daɗi acikin ranta, hakanan idan Saifuddeen na mata hakan agaban Zaleeha take jin kanta kaman tafi kowa a duniya.
ganin ta girgiza mishi kai alamun ta ƙoshine yasa ya sake bata abin sha.
Ɗagowan da Zaleeha zatayi ta gansu ahaka, take taji ƙirjinta ya buga. Cikin sauri ta kauda kanta wani sihirtaccen murmushi tayi kana ta miƙe a hankali hannu ta miƙa ta karɓi Adeel dake hannun Ummi, kana ta juya ta nufi cikin falon,
sam Ummi batayi yunƙurin hanata ba.


Wani irin murmushi Saifuddeen yayi, tare da ɗan cije laɓɓansa, cikin zuciyarsa yace.
*"Ƴarinya yanzu aka fara wasan."*


Hayatuddeen ne ya miƙe yayi ɗakinshi,
Hakama Raliya ta miƙe tabi bayan Ahmad.


Ido Ummi ta zubawa Saifuddeen ko ƙibtawa batayi,
ganin haka yasa itama Ameena ta miƙe ta nufi side ɗinsu dan taje ta sake wonka dan ta lura yau Saifuddeen a matsaye yake.


Shiru falon ba motsin kowa,
gaba ɗaya Ummi ta hana Saifuddeen motsi dan yasan tun yana yaro in ya mata laifi taka hukunta shi da hakan, cikin fargaba ya ɗan gyara zama tare da yin rau-rau da ida nunshi wanda da gaske sun cicciko da ruwa dan bai fahimci abinda yayi yanzu bane ya ɓata mata rai.
kai ya rangwafar tare da mata mgna da yarensu.
"Ki gafar ceni Ummi ban san me nayiba, na tuba gaya min laifiba?".
Kwaffa tayi tare da cewa.
"Uhummmm yayi kyau Saifuddeen kaci gaba da cusawa ƴar mutane baƙin ciki".
Kanshi ya jujjuya cikin alamun mgnarsu yace.
"Ummi me kuma nayi, na kaita gidan su na tayata bada haƙuri, duk sun yafe mata nima na yafe mata, kuma yanzu meya rage?".
miƙewa tsaye tayi tare da cewa.
"Key ɗin ɗakinta zaka bani, ta koma ɗakinta,kuma ka raba musu kwana kamar yadda shariya ta buƙata".
Wayarshi ya zaro tare da rubuta mata.
"Wlh Allah Ummi na mance inda na ɓoye key ɗin amman insha Allah zan neme shi in na ganshi zan bakishi".
kai ta jinjina tare da cewa.
"Tom yayi kyau".
Daga nan ta juya ta nufi ɗakinta.
Shiru Saifuddeen yayi yana saƙa da warwara a ranshi, wani irin munafikin murmushi yayi kana ya wuce side ɗinshi, yana tafe yana rubuta wa Ameena saƙo ya tura mata kana kai tsaye ya wuce ɗakinshi.








Wasa farin girki sannu-sannu bata hana zuwa sai dai a daɗe ba jeba, muna gab da shigo wani sashi mai ɗan karen zaƙi a littafinsa biya ɗarinki uku ki karanta ba tare da haƙƙin kowa a kankiba, in kina buƙata ga number ta 09097853276 ki turo katin mtn na 300 ko kimin transfer na 300 ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.






By


*Garkuwan Fulani*
10/4/20, 7:04 PM - Mmn Khalid:

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login