Showing 126001 words to 129000 words out of 239422 words

Chapter 43 - Nakasa Ba Kasawa Bace Part 2 Complete by Aisha Aliyu Garkuwa .txt

06 Dec 2024

11868

haka yake ba, ta ɗauka irin musakan nan ne masu matacciyar zuciya wanda sun kele sun yaɗe sun shanye irin waɗanda ba zasu iya smfanan kansu Bama bare wani.
Ɗago kai Zaleeha tayi ta kalli Maman, ɗan lumshe idanunta dake zubar da ƙwalla tayi, asanyaye tace.
"Mama." Dubanta Maman tayi, tare da ƙura mata idanu.
Ɗan jan sheshsheƙa tayi, cikin muryarta da bata fita sosai tace.
"Na aikata laifi mafi girma, wanda yasa saboda haka Babana da kuma duka ƴan uwana suke fushi dani, sanadiyar haka har Adda Maryam ta rasu, bamu sake ganawa ba, nabar kowa da komai saboda idanuna sun rufe da son wanda ni kaina yanzu na yarda bazan sake ganinshiba, sai-dai kuma nasan awannan lokacin da ban samu goyon bayanki ba Mama, tabbas da bazan tafi nabar kowa ba, nayi kuskure me girma arayuwata, wanda kuma bana fatan sake maimaita irinsa agaba ɗaya rayuwata, fushin Baba Malam da Hamma Saif fushin Allah ne, bakuma zanso su sake fushi dani ba, ayanzu al'barka kawai nake nema, saboda na ɗauki al'ƙawarin zan zauna agidan aurena da daɗi ko ba daɗi, saboda haka ina buƙatar kyakkyawan fata daga gareki, domin har gaban abada ke uwace agareni, wanda kuma bazan taɓa sanjaki ba." taƙare maganar tana me kama hannun Mama, tuni hawaye kuwa wani nakoran wani akan fuskarta.
Idanun Maman ne suka ciko da hawaye, tabbas tayi nadaman abun da ta aikata na bin zugar kafurar yauarta, tunda ga lokacin da labarin rasuwar Adda Maryam ya riski kunnuwanta, tayi nadama ƙwarai sannan jikinta yayi sanyi sosai, duban Zaleehan tayi sosai, ganin yanda Zaleehan ta rame, ta zama wata abun tausayi, lokaci guda ta fita hayyacinta, yasa taji kuka nason zuwar mata, cikin sauri ta miƙe tsaye ta nufi ɗakinta, dan tsayawarta zai iya baiyanar da raunin zuciyarta tana gab da shiga ne tace.
"ALLAH ya baku zaman lfy Zaleeha."


Ganin haka yasa Zaleeha kwantar da kanta ajikin kujeran da Maman tatashi, ta saki wani marayan kuka,


Aunty Aisha ne ta share hawayen da suka cika idanunta, asanyaye tace. Ta kalli Zaleeha cikin sanyi tace.
"Jiya Solomon da matarsa sunzo sunyi gaisuwa, sunce suna son ganinki akwai abu mai mahimmancin da sukeso sanar dake, to lokacin bamu san inda kikeba sun kira layinki kuma baya shiga, amman sunce zasu zo nan bada daɗewa ba."
Wani irin sanyine ya ziyarci Zaleeha Allah yasa musulta zasuyi, Allah yasa musultan sune yayi sanadin zuwanta garin Numan".
cikin nitsuwa Aunty Shatu tace.
"Saifuddeen kamata kuje, Allah Ubangiji yayiwa rayuwar aurenku al'barka, ya baku zuri'a me al'barka."
Kansa yaɗan jinjina, sannan ahankali ya murza wheelchair ɗinsa ya ƙaraso har gaban Zaleehan, hannunsa yasanya yaɗan ɗago kafaɗunta, tare da miƙar da ita tsaye, hannunta ya kama, cikin nutsuwa ya jata suka nufi hanyar barin falon,
Aunty Ruda kuwa baki ta sake tana kallonsu, har suka fice daga cikin falon.
Haka suka fito compound ɗin gidan yana riƙe da hannunta, yayinda Zakariyya kuwa ke biye dasu abaya sai kallonsu yake, sai ayau yasake ganin dacewar Hamma Saifuddeen ɗin da Zaleeha, kallo ɗaya zakayi musu kaga kaman dansu biyun akayi kowannensu.
Sule driver na hangosu cikin hanzari ya buɗe musu murfin motar, zuwa lokacin kuwa tuni har ma Dirankadi yabar gidan, dan dama akwai inda zaije, sakin hannunta yayi, tare da juyowa ya sake bawa Zakariyya hannu sukayi musabaha, cikin ɗan jin daɗi Zakariyya yace. "Asauƙa lafiya Hamma, Allah Ya saka da al'khairi."
Kai kawai ya jinjina masa, sannan ya shige cikin motar bayan itama ta shiga.
Cikin nutsuwa Sule driver ya ja motar suka bar cikin gidan, Zakariyya kuwa saida yaga fitarsu kafun yake komawa cikin gida.

Tunda suka baro gidan take sakin sheshsheƙan kuka, haka ta ɓoye kanta acikin cinyoyinta tana sakin wani numfashi me zafi, duk abun da takeyi yana lure da ita, amma sai ya kawar da kansa gefe yayi kamar bai ganta ba,
saida tafiyar tasu ta ɗanyi nisa, kafun ta ɗago kanta, ahankali ta sauƙe idanunta akansa, wasu hawaye masu zafine suka sauƙo daga cikin idanunta, ji tayi gaba ɗaya zuciyarta tayi rauni sosai, wani irin ƙima da kuma girmansa ne suka cika idanunta, tabbas ayau ya taimaketa, yayi mata abun da mutane da yawa suka kasa yi mata shi, yau ya zame mata inuwa kuma majingina, ya kareta daga rana, sannan yayi ƙoƙarin haskaka rayuwarta, ya ɗaukota daga duhu ya kawota cikin haske, dame zata saka masa? wani irin kuka ne ya zo mata, hakan yasa ta faɗa jikinsa tare da rungumesa ƙam-ƙam tamkar zata haɗesu wuri ɗaya.
asakamakon hakan kuwa wani irin shock yaji ajikinsa, karon farko kenan da ta fara shiga cikin jikinsa dan kanta, hannayenta ta sanya ta zagayeshi, tare da ɗaura kanta akan faffaɗan ƙirjinsa, ta saki wani irin kuka mai taɓa zuciya, cikin kukan nata ne ta cusa fuskarta acikin ƙirjinsa, wanda hakan yasa aninayen dake gaban rigarsa ɗan ɓallewa, take kuwa fatan ƙirjinsa ta bayya, hakanne kuma yasa ahankali hancinta da laɓɓan bakinta ke gogan skin chest ɗinshi, wani irin kuka takeyi me taɓa zuciya, still kukan take tana ɗan jujjuya kanta acikin ƙirjinsa, hakan da takeyi ne yasa gaɓa ɗaya jikinsa yayi weak, wani irin abu ne yakeji na yawo ajikinsa, wanda zai iya rantsewa, cewa tunda yake aduniya bai taɓa jin irin hakan ba, wani fitinannen feeling yakeji, gefe guda kuma ga wani pleasure wanda ko sex suke da Ameena bai taɓa jin irin wannan pleasure da kuma feeling ɗin ba, babu abun dake neman zautar da tunaninsa kaman yanda tausassun laɓɓan bakinta ke gogan fatar ƙirjinsa,
A hankali ta ɗago kanta ta zuba mishi,ido shima idon ya zuma mata, goshinta na manne da haɓarss cikin Muryar me sarƙewa haɗi da sheshsheƙan kuka tace. "Nagode! Nagode!! Nagode!!! sosai Hamma Saif, tabbas ka taimakeni arayuwa, sanadinka gashi Baba Malam ya yafemin, nagode maka ƙwarai matuƙa, Allah Ubangiji ya biya maka buƙatunka na duniya da lahira, Allah yafaranta maka kamar yanda ka faranta min, Allahu rabbi ya gafarta maka zunubanka, kamar yadda kayi sanadin yafe min da Baba Malam yayi, tabbas kamin abun da kowa ya kasa min, nagode sosai Hamma S..a..i..f."
Kukane ya ci ƙarfinta, sai kawai ta sake rungumesa sosai. Ahankali yaɗan lumshe kyawawan idanunsa wanda suka soma runewa zuwa kalan ja, hannunsa yasa ya tallafo haɓarta, tare da ɗan ɗago fuskarta, hakan shi ya bawa fuskokinsu daman kusanci da juna, idanunsa wanda suke ɗan lumshewa kaɗan kaɗan ya zuba mata, ahankali ya matso da fuskarsa gareta har hancinsu na gogan na juna, goshinsa ya ɗaura kan nata hancishi na bisa tsinin hancinta haɗuwar numfashinsu waje ɗaya, shiya sanya suka lumshe idanunsu atare, ahankali laɓɓanta suka ɗan buɗe, saboda sheshsheƙan kukan da takeyi.
ɗan buɗe idanunsa yayi, kana ya ƙurawa kyawawan laɓɓanta, shanyayyun idanunsa, wani irin abune ke yawo acikin jikinsa, haka yakejin kamar ya kamo kyawawan laɓɓanta yayi kissing ɗinta,
Idonshi ya maida ya lumshe tare da ɗan zaro harshenshi ya ɗan lashi tattausan lips ɗinta,
da sauri ta buɗe ida nunta, ganin haka sai kuma ys janye fuskarsa baya yana sakin wata irin ajiyar zuciya yayi kamar bashi ya lashi laɓaɓɓan nataba, ahankali itama ta ɗan janye jikinta baya, nan kan kafaɗansa ta ɗaura kanta, ahankali take sakin ajiyar zuciya, har yanzu kuwa idanunta basu daina zubar da ƙwalla ba, saidai acikin zuciyarta farinciki ne me tarin yawa, ji take kaman anyaye mata duk wata damuwarta ta duniya, yafiyar Baba Malam da na Hamma Saif yasanya tanajin kanta, awata sabuwar duniya ta daban.
Hannunta ta saƙala acikin nasa, yayinda hawayenta ke ɗiga akan kafaɗansa.
Ahankali yaɗan jingina bayansa da jikin kujeran motar, tare da lumshe idanunsa, numfashinta dake sauƙa akan wuyansa, shiya sanya yaji gaba ɗaya jikinsa ya sake, yayinda tsikar jikinsa keta faman mimmiƙewa, dama akan Zaleeha shi namiji ne me yawan feelings, yanzu da take ajikinsa kuwa shikaɗai yasan me yake ji.
Zaleeha kuwa daɗin jikinsa da kuma sassanyan ƙamshin turarensa dake shiga hancinta, su suka taimaka wajen bata wani irin nutsuwa na musamman, sake lumshe idanunta tayi, tana me busa masa iskan numfashinta akan fatar wuyansa.


Gaba ɗayansu sun shagala, babu wani wanda yake cikin tunaninsa, musamman ma Saifuddeen daya tafi izuwa wata duniya ta daban, tsayuwar motar ne yasasu buɗe idanunsu, gani sukayi har sun iso gida. Akunyace taɗan janye jikinta daga na Saifuddeen ɗin, nan ta ɗan gyara mayafinta dake ƙoƙarin zamewa. Sule driver kuwa cikin hanzari ya zagayo ya buɗe mawa Saifuddeen ƙofar motar, bayan ya buɗe bot ya zaro masa kekensa.
Cikin nutsuwa kuwa ya hau kan keken nasa, Zaleeha ma jikinta asanyaye ta fito daga cikin motar, idanu ta zuba masa ganin ya nufi part ɗinsa, kanta ta ɗan sunkuyar ƙasa, sannan ta share ɗan gun hawayen dake maƙale ƙasan idanunta, cikin ɗan sassarfa ta nufi part ɗin Ummi, tun kafun ta ƙarasa shiga falon, take ƙiran sunan Ummi, Raleeya dake zaune acikin falon ne ta ƙurawa ƙofar shigowa ido, musamman yanda taji Zaleeha nata faman ƙiran sunan Ummi.
Murɗa handle ɗin ƙofar falon tayi ta shiga, fuskarta ɗauke da murmushi da kuma hawaye, ganin Raleeya yasa ta tafi da gudu ta faɗa jikinta, ganin murmushi da dariya akan fuskan Zaleehan yasa, Raleeya itama ta saki murmushi, ɗago kai Zaleehan tayi, tace. "Raleeya Baba Malam ya yafemin, haka Ya Ahmad dasu Mamy ma duk kowa ya yafemin, Raleeya Hamma Saifuddeen ya zama garkuwa agareni, ayau ya bani duk wani farinciki, sanadiyarsa Baba Malam ya yafemin, yanzu Baba Malam baya fushi dani." ta ƙare maganan hawaye na zuba daga cikin idanunta.
Itama Raleeya Idanunta ne suka ciko da ƙwalla, murmushin jin daɗi ta saki, tare da ƙara rungume Zaleehan, cikin farinciki tace.
"Masha Allah Zaleeha natayaki murna ƙwarai, yanzu kema zakiyi rayuwa cikin farinciki."
Dai-dai lokacin Ummi ta fito daga ɗaki, dan tun tana banɗaki takejin ƙiran da Zaleehan keyi mata,
ganin Ummi yasa cikin sauri tatashi daga jikin Raleeya, ƙarasawa tayi da sauri kaman wata ƴar ƙaramar yarinya ta raɓa jikin Ummi, tana sakin dariya me haɗe da hawaye.
Cikin nuna farin cikinta tace.
"Ummi Baba Malam ya yafemin, hakama su Mamy, Ummi har Ya Ahmad ɗina ma ya yafemin, kuma yanzu basa fushi dani, Ummi Hamma Saif ne yayi min komai, saboda shine duk kowa ya yafemin, shikenan yanzu Baba Malam ɗina baya fushi dani."
taƙare maganan tana me sake rungume Ummi, sam ita bata ɗauki Ummi mazaunin suruka ba, ko yaushe amatsayin uwa take ɗaukanta, dan abun da za tayiwa Mama da Mamy shi zatayiwa Ummin, saboda acikin jininta soyayyar Ummin take.
Cikin farin ciki Ummi ta shafi fuskarta, tare da cewa.
"Alhamdulillah, tabbas kinzo da labari me daɗi, kuma naji daɗin hakan sosai, dama nasan ke ta gaban goshin Baba Malam da ya Ahmad ne, saboda haka yanzu kuka ya ƙare, idan kuma nasake ganin hawaye akan wannan fuskar to fa zamu ɓata, kindai ji kam."


Murmushi me kama da dariya tayi, kamo hannun Ummin tayi cikin sanyi tace.
"Nagode sosai Ummi haƙiƙa kin cika uwa tagari, samun irinki awannan duniyar zaiyi wahala, Inasonki Ummi na, dan Allah ki ƙara yiwa Hamma Saif godiya, duk ta dalilinshi ne Baba Malam ya yafemin, ku ɗin kunzama majingina agareni, sannan kunzaman to mini lema, wanda daku ne zan kare ruwa da zafin rana, nagode sosai!".
tafaɗi maganar tana sakin wasu hawayen farinciki, tare da sake rungume Ummin.
Murmushi Ummi tayi, sosai takejin soyayyar Zaleehan acikin ranta, tabbas tasan Zaleeha mutumiyar ƙwarai ce, kuma tasan bazata taɓayin danasanin samunta amatsayin suruka ba.
Hayatuddeen wanda tun ɗazu ya shigo falon, ƙarasowa garesu yayi, tare da haɗasu su duka ya rungume ta gefen Ummi cikin farinciki yace.
"Nima Inasonki Adda Zaleehan Hamma, saidai kuma zan iyayin kishi dake ako da yaushe, dan naga kaman kinason maidamin Ummi na taki ke kaɗai."
Murmushi su dukansu sukayi.
ɗan ɗagowa Zaleeha tayi, tana share hawayen dake kan fuskarta tace.
"Ai dai kuma indai ina cikin gidannan Ummi tawa ce dan kai kayi ƙato. Ko Ummi?".
ta faɗa tana mutsutstsuka idanunta, hakan yasa tadawo kaman wata ƙaramar yarinya.
Ƴar dariya Ummi tayi tare da cewa.
"Ƙwarai kuwa, amma fa saidai in kin ɗauki al'ƙawarin cewa bazaki sakeyin kuka ko abayan idanuna ba, sannan kuma kada kice zaki sakeyiwa Adda Maryam kuka, nasan kinsan cewa mamaci bayason kuka, addu'a kawai yake buƙata, saboda haka Adda Maryam addu'a take buƙata awajenki ba kuka ba, daga yau kuma banso na ƙara ganinki cikin ƙunci, tun da Baba Malam ya yafe miki, inason ki saki jikinki, ki zauna acikin ƴan uwanki, sannan kuma daga yau banason naga kina takura kanki kinji ko." Kanta ta jinjina alaman. "To." Murmushi Ummi tayi tare da shafa kanta, cikin kulawa tace. "Allah yayi muku al'barka, ya kuma baku zaman lafiya keda abokiyar zamanki."
sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana wasa da ƴan yatsun hannunta tace "Ameen"
Hayatuddeen ne yaja hanunta suka dawo cikin falon, nan kusa da Raleeya suka zauna, kallonta yayi cikin nuna jin daɗinsa yace.
"Wallahi Adda Zaleeha kinfi kyau idan kina murmushi, yanzu da kina murmushi bakiga yanda kikayi kyau ba, sannan kuma nasan yau da dare zamu buga game sosai tunda naga kina cikin farinciki ko?."
Murmushi tayi tare da cewa.
"Ni dai bazan buga game da kai ba, abunda duk nasan halinka, rinto kakeyi, ranan ai naga kanata yiwa Raleeya rinto."
Ummi da Raleeya wacce waya takeyi da Raihana ne sukayi dariya, shikuwa Hayatuddeen murmushi mugunta yayi, cikin son tsokan Raleeyan yace.
"Adda Zaleeha bakisan wacece Adda Raleeya bane, itace fa bata iya game ɗin ba, shine kuke ganin kaman rinto nake mata."
Hararansa Raleeya tayi tare da cewa.
"Faɗawa wanda baisan waye kai ba yaro,kowa ya sanka da rinto."
Nan dai dukansu suka ɗanyi murmushi, daga haka kuma suka shiga ɗan taɓa hira.


Acan ɓangaren Saifuddeen kuwa, yana isa part ɗinsa, kai tsaye bedroom ya wuce, yana shiga ya soma rage kayan jikinsa, cikin nutsuwa ya cire riga haɗi da wandon dake jikinsa, wani farin towel ya zaro daga cikin wani ɗan ƙaramin drawer, tare da ɗaurawa akan waist ɗinsa, ahankali yake tura wheelchair ɗin nasa, har ya kawo bakin ƙofar shiga bathroom, hannunsa ya ɗaura ajikin handle ɗin ƙofar sannan ya tura kansa ciki, komai na cikin toilet ɗin nasa tsab yake, ƙamshi ne kawai ke tashi, sanin cewa kwata kwata bayason ƙazanta yasanya Ameena ke ƙoƙarin gyara masa toilet ɗin nasa kullum dan Ameena akwai tsabta, cikin nutsuwa ya haɗawa kansa ruwan wanka me ɗan ɗumi, tare da zuba wani irin turaren wanka me daɗin ƙamshi acikin ruwan, kunce towel ɗin jikinnasa yayi, ahankali yaɗan matso da kekensa kusa da bathtube ɗin, kamar yanda ya saba, cikin nutsuwa yake komansa, koda ya shiga cikin bathtube ɗin, ɗan zamewa yayi ya kwanta, tare da jingina kansa da jikin saman bathtube ɗin, hakanne yabawa ruwan ɗumin daman ratsa ko ina najikinsa, ɗan lumshe idanunsa yayi tare da sakin wata irin ajiyar zuciya me ƙarfi. Ahankali moment ɗinsu da Zaleehan ke dawowa cikin tunaninsa, wani irin sabon yanayi ya samu kansa aciki, laɓɓansa ya ɗan lasa, saboda tunawa da sweet mood ɗinsu da yayi, musamman ma yanda ɗazun bakinta ke gogan ƙirjinsa, samun kansa yayi cikin wani irin shauƙi, baisan wani irin so yakewa Zaleeha, da har yakejin wani irin feelings na musamman akanta ba, Ameena ce ta fara faɗo masa arai, hakanan yaji gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, sam bai taɓajin abun dayaji ayau dangane da Zaleeha, akan Ameena'n ba, saidai kuma koma miye itama tana da nata matsayin acikin rayuwarsa, saboda itace mace ta farko daya fara sani acikin rayuwarsa, itace kuma wacce ta fara haifa masa ɗa, sannan tasoshi amatsayinsa na nakasashshe, nakasarsa baisa taƙisa ba, ta kuma rungumesa amatsayin miji, duk da tasan cewar baya sonta, amma hakan baisa taƙi yi masa biyayya ba, ko yaushe so take ta faranta masa, saboda haka ko kusa Ameena bata cancanci wulaƙanci daga garesa ba, koba komai tayi masa halacci, haƙiƙa Zaleeha itace mace ta farko daya fara so, kuma yakejin soyayyarta acikin jininsa, sannan itace zaɓinsa, Saɓanin Ameena da ta kasance zaɓin Ummi, sai-dai kuma duk da haka tana da nata matsayin awajensa, wulaƙanta ta kuma tamkar budulci ne ga Umminshi.
Sake gyara kwanciyansa yayi, yana mejin kasala nasake sauƙar masa, gaba ɗaya abun da Zaleehan tayi masa, ya hautsuna tunaninsa, haka yayi wanka jikinsa duk amace, koda ya fito acikin bathtube ɗin wata rubber bathrobe yasanya, saida ya ɗauro al'wala kafun ya fito daga cikin toilet ɗin.
Nan ya kimtsa kansa cikin wasu riga da wandon jeans masu kyau da tsada, feshe jikinsa yayi da turarensa me dadin ƙamshi,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login