Showing 42001 words to 45000 words out of 161948 words
damesa ba yace.
"Uhm! What i have done to you? Nazo garinku kun bani kulawa ok fine thank you, but please stay away for me, I'm tried! Haaaa, duka kuma kana sane ka bari aka daken ai dan mugunta, Ni kuma banyi na yafe kuje can kuci kanku"
Ya ƙare zan can yana dafe ƙirjinsa tare da sauke wata zazzafar iska daga bakinsa, ya shiga sauke ajjiyar zuciya a jajjere,
Kallonsa kawai Arɗo yayi ya fahimci cewa haushin dukan ne har yanzu bai sake sa ba, shiyasa yake son huce haushinsa akan sa,
Ba tare da damuwa ba Arɗo ya kalli Abu Maleek yace.
"Tunda har ka bari aka dake ka, ya zama dole ka rama, rashin ramar kowa yana nufin kai lusari ne, wanda bai cika jarumin Namiji ba, rashin ramar na nufin Tabbas baka amsa sunanka na Namiji sai dai mata maza, kuma zaka bar garin nan ana maka ihu ne, tare da jifan ka, idan ka aminci shikenan sai a raka ka sa jifa da duwatsu"
Ya ƙare maganar yana sakin dariya, domin yayi hakan ne domin ya tun zura Abu Maleek, babu shakka kowa haƙƙarsa ta cimma ruwa,
Abu Maleek daya ke jin maganar Arɗo kamar Almara, shi za'a ma ihu? "Uhm" kawai yace yana yin gaba domin zuwa cikin inda ake jiransa, tuni kuma jikinsa ya fara rawa.
Yana shiga ya gyara tsaiwarsa, tare da lumshe idanunsa,
Barkido dake tsaye ya ƙara gyara tsaiwarsa yana mimmiƙa hannunsa, alamar dai shima a shirye yake da karɓar dukan na Abu Maleek,
Kallon gefe Abu Maleek yayiwa Barkido yana faɗin
"zakaci gidanku, fuska kamar Salad"
Lamiɗo ne ya miƙa wa Abu Maleek wata zabgegiyyar bulala sai ƙyalli take,
Hannun damansa yasa ya amsa a cikin ransa yake faɗin
"Bisimillah Rahmanir Rahim"
Ya faɗa yana gyara zaman bulalar a hannunsa, kallon Bulalar yayi sosai, kafin ya ɗaga kansa ya kalli Barkido, nan take kuma yaji wani haushi da baƙin cikin dukan da Barkidon yayi masa,
Hakan ya sanya ya ƙara riƙe bulalar sosai, a hankali kuma ya ware bakinsa cikin sarrafa harshe yace.
"Ya Rahmanu ya Rahim!"
Ya faɗa yana mai shafe bulalar da tafin hannunsa, a hankali kuma ya ɗaga bulalar kafin cikin wani zafin nama ya saukewa Barkido bulalar a tsakiyar bayansa.
A gigice Barkido ya ware mitsi mitsi idanunsa tare da kame jikinsa waje guda, domin tashin farko Barkido idanunsa ya raina fata,
Bai dawo hayyacinsa ba yaci Abu Maleek ya sake sakar masa wata Bulalar, wacce ya sanya ya furta "Auchhhiii!"
Da ɗan ƙarfi saboda tsananin zafin shigar bulalar da yaji ya ratsa masa dukkan wata gaɓa ta jikinsa,
Abinka da cikakken namiji, kuma ƙaƙƙarfa, wanda ya saba motsa jikinsa ta hanyar yin gym kala-kala, Uwa uba kuma FOOTBALLER, shiya sanya ya zage dukkan ƙarfinsa yana laftar Barkido da dukkan ƙarfinsa, a ransa yana ambaton sunan Allah,
Barkido tuni idanunsa ya fara kawo ruwa, zufa ta wanke masa jikinsa sai tsuma yake,
Idanun Abu Maleek ne ya sauka akan wata bulala dake hannun Lamiɗo da sauri yasa hannu ya amsa, ya haɗa hannu da dama, ya shiga Laftar Barkido wanda tuni ya fara kurma Ihu yana yin baya,
Sosai Abu Maleek ya gigita sa, ya ruɗa masa jiki da duka ganin babu sarki sai Allah yasa Barkido faɗin.
"Wallahi na bar baka ita, na yafe bana sonta ka rabu dani haka"
Ina sam A.m baya gane karatun bare yayi masa hadda, duk inda Barkido yayi sai ya bisa ya daka, ganin idan bai yi da gaske ba, sai iya rasa ransa ya sanya ya ɗaga ƙafafuwansa, tare da arta ana ƙare ya nausa cikin jeji kamar yadda Labbo yayi.
Ɓoyayyiyar ajjiyar zuciya A.m ya sauke yana jin zuciyarsa wasai, bashi da wata damuwa wacce ta shafi wannan dukan domin sai da yayiwa Barkido duka wajan hamsin,
Fesar da numfashi yay yana ɗan cusa hannunsa tare da hargitsa gashin kansa wanda ya kejin yayi masa nauyi sosai, saboda rashin saloon da bai ba.
Mutane da yawa sai da suka yi mamakin yadda Abu Maleek ya iya dukan Barkido, Arɗo wani lafiyayyan murmushi ya sauke kafin a hankali yace.
"Lamiɗo kirawo min Jon wuro, domin ya zama wakilin Wannan baƙon, kai kuma ka zama wakilin Julde"
Jinjina kai Lamiɗo yayi kafin ya miƙe ya nufi bukkar Jon wuro,
Babu jimawa suka dawo a tare fuskar Jon wuro ta faɗaɗa da Murmushi.
Jalaluldeen can ya nema ƙasan wata bishiyoyi wacce ƙasanta yake ɗauke da yashi mai sanyi ga ruwa na ɗan tsastsafo wa ta ƙasan wajan,
Yana zama Sweet tazu ya shige jikinsa, kwaɓe fuska yay yana ɗura haɓarsa a jikin sweet,
Kafin cikin ƙasa da murya yace.
"I'm tried sweet, ina son gida, i need to hug my Grandma, Oumuu, And my world my everything Dadyna, nayi kewar su sweet"
Ya ƙare maganar yana shafa gashin sweet ɗin wanda ya ɗan hargitse, saboda yawon da suka sha.
Gyara zama Jon wuro yayi tare da kallon Arɗo yace.
"A matsayi na, na Uba a wajan Wannan baƙo, ina nemawa ɗana Auran ƴar ka Hawwa'u (Julde), ina fatan zaku bani wannan aure cikin girma da mutun ci haɗi da karramawa?"
Jinjina kai Arɗo yayi yana mai sakin murmushi yace.
"Ni kuma a matsayi na, na uba a wajan Hawwa'u, ina mai farin ciki sanar dakai cewa na bawa ɗan ka auranta halak kuma malak"
"Allahamdulillah"
Lamiɗo ya fara kafin Jon wuro ya ɗauki kuɗi ya bawa Arɗo yasa hannu ya amsa, nan suka shaida auran Hawwa'u Julde, da kuma Jalaluldeen Tunde Muhammad Jalal, akan shaidu wajan mutum goma.
Tsakanin Julde da Abu Maleek babu wanda ya san abinda yake faruwa, sai da su Arɗo suka gama komai, sannan Arɗo da Jon wuro suka nufi inda Abu Maleek yake zaune shida sweet yana mata surutu ita kuma sai jela take ɗagawa.
Suna zuwa suka nemi waje suka zauna, Jon wuro da yafi shekaru akan Arɗo ya fuskanci Abu Maleek sosai, tare da faɗin.
"Yaro na, Allahamdulillah! Kayi na sara akan abokin adawarka, ka shiga neman aure ba tare daka san komai ba, amma cikin ikon Allah gashi ka samu damar samun Yarinyar da ka shiga Shaɗi a kanta"
With much surprise Abu Maleek yake binsu da kallo, Shaɗi? Yaushe ya shiga shaɗi? Wacce yarinyar suke magana? Wannan sune tarin tambayoyi da suke danƙare a cikin zuciyarsa,
Jon wuro ne ya ƙare zama sosai ya fuskanci Abu Maleek cikin nutsuwa da kuma halin daddako yace.
"Tabbas wasan da Arɗo ya faɗa maka ba wasa bane haka kawai, shaɗi ne wanda ake yinsa yayin neman aure, Barkido da Labbo sune suka shiga shiga cikin shaɗin, kafin kai kuma ka shiga daga baya, shigarka kuma ya sanya Labbo fita, gashi kuma kayi nasara duk da cewa baka san, dalilin yin hakan ba, to Allahamdulillah a yanzu haka Hawwa'u ta zama matarka bisa jagoranci mu gaba ɗaya, na zama wakilinka wanda na amsar maka auran a wajan Arɗo na bada Sadaki kuma da hannu na, Julde ta zama Matarka halak malak, kuma a yanzu zaka tafi da ita zuwa ƙasar ku"
Wata zabura Abu Maleek yayi, jikinsa na rawa ya shiga nuna Jon wuro da hannu cikin tsantsar ɓacin rai da kuma tarin talaucin abinda sukai masa yace.
"What? Aure? Haaaa! Dawa ɗin ni dai? Goodness saboda kun rasa yadda za kuyi da ƙaramar yarinyar ku shine zaku liƙa min ita? Uhm wallahi za kuyi dana sani bana sonta ko ɗaya kamar yadda kuka liƙa min ita haka Nima zan mayar da ita baiwa, daman ai ba ƙaunar ta kuke ba, Wheel Nima haka kunga anyi 50% kenan"
Ya faɗa yana sakin wani zazzafan huci daga cikin bakinsa idanunsa ya kaɗa yayi jaa, kana kallonsa zaka fahimci how sad he is,
Gaba ɗaya ya birkice gargasa jikinsa duk ta mimmiƙe, Jon wuro kallonsa yayi domin yasan za'a rina,
Kuma tun yanzu ya fara tausaya Rayuwar Julde zata shiga hannun wanda baya sonta, amma zamanta a wajan zaifi daɗi fiye da zamanta a wannan rugar,
Arɗo kam ko a jikinsa domin shi ko Abu Maleek zai tafi da ita ya yankata ya zubar da gawarta ko a jikinsa,
"Zuwa yanzu da Julde amana take a wajan ka, kasan duk wanda yaci amana Shida Ubangijinsa, bazan maka dole ka sota ba saboda so halitta ne, amma ina fatan wata rana ka zame mata garkuwa, bangon da zata jingina taji daɗi, duk abinda ya samu da rayuwarta a yanzu kuma KAI NE SANADI, kayi haƙuri ka zame mata Tubalin da zai gida rayuwarta, ko ba zaka so ta ba, ka kula da rayuwarta"
Yakai ƙarshen maganar cikin sigar rarrashi da kuma ban baki,
Abu Maleek huci kawai yake saukewa jikinsa duk rawa yake.
Da kallo kawai suke binsa ganin yadda naman jikinsa yake rawa, ga yadda jijiyar kansa ta fito sosai, hannunsa ya sanya ya ɗauki Sweet tare da kallonsu yace.
"Bazan ce a'a ba, amma duk abinda ya faru kune kuka ja mata, bani da lokaci Ni tafiya zanyi"
Ya ƙare maganar cikin ɗacin rai, Arɗo ya miƙe babu jimawa ya dawo tare da Julde, da kuma wani kuttu guda biya ɗaya ya cika masu Kindirmo, ɗaya kuma ruwa ne mai kyau,
Bawa Abu Maleek yayi ganin da gaske Tabbas zai iya neman abu a hanya ya sanya ya amsa, ba tare da yace komai ba ya nufi cikin jejin da zai fitar dashi daga cikin garin baki ɗaya,
Yana tafe tana biye dashi a hanya jama'ar garin na ɗaga masu hannu,
A haka suka fara nausawa cikin jejin ita dai Julde katari sahunsa kawai take bi,
Tsayawa yayi tare da juyawa ya ganta can nesa ga yamma nayi shi kuma a yau yake son barin wannan gantalallan garin wanda bai masa amfanin komai ba,
Gajeren tsaki yaja da wani irin sauri kuma ya nufi inda take yana zuwa yasa hannunsa yay cilli da sandar haɗe Jikinta tayi waje guda hawaye ya shiga sakko bata,
Kafin tayi wani motsi taji ya sanya hannunsa ya ɗauke ta cak tare da sanyata a tsakiyar bayansa kana ya goyata a faffaɗan bayan nasa....
Sai mun haɗu a book 2
Gobe akwai tattaunawa akan book 1 kowa yayi joining na comment section.
*Abu Maleek na kuɗi ne, biya 500 domin yin karatu cikin nutsuwa 08119237616*
*BY*
*SARAUTA*
*HADEEYATULLAH*
BONUS kuma kuji ɗan abinda ƴan PAID suka gani😆
*LITTAFIN KUƊI NE KI BIYA KI KARANTA HANKALI KWANCE,DUK WACCE TA KARANTA MIN BOOK KYAUTA DA WACCE TA TURO DA WADDA TA GAN SHI A WANI GROUP ITA MA TAYI SHARING IN KUN YI DAIDAI KUN SANI🤷🏻♀️ mai son biyan kuɗin karatu sai ta tuntuɓe ni ta WhatsApp* +22795045822
*Page 33-34*
Sai da mu sha hira sosai sannan Abbas ya baiwa Haidar biscuit da chocolat da ya sawo mashi,haka kawai naji kamar nayi zamana a can tare da ɗan uwana.
Kallona Abbas yayi yace "ko ke ma a mayar da ke boarding ɗin ba ki san je ka ka dawo?"baki na turo na girgiza kaina,stop yayi gun mai gasa masara ya na mai fiddo waya ya kira Alhaji amman sam layin yaƙi shiga.
Kuɗi ya miƙa a zuba mashi masarar a leda,miƙo min ɗaya nayi da murna na karɓa na fara ci ina mamakin yadda aka yi su ke sayar da masara kamar wasu Hausawa.
Mu na shigowa gida na tsinkayi Raliya zaune kusan flowers ta na sunsunar su,baki na ɗan taɓe haka kawai naji matar ta fita raina sai ma haushinta da ni ke ji.
Fita nayi na kama hanyar da za ta sada ni da ƙofar shiga falo yayinda shi kuma Abbas ya zarce gun sanyin idaniyar shi,a Shagwaɓe ta faɗa jikin shi ta na shafar gemun shi "miss You dear"sai da yayi mata kiss a lips sannan "moi aussi tu me manques"masarar da ya sawo mata ya miƙa mata ta karɓa haɗi da komawa ta zauna.
Abbas na ƙoƙarin shiga falo appel d'urgence ya shigo mashi,a kiɗime ya nufi mota yayi mata key mai gadi ya buɗe mashi ko da ya hau titi gudu ya kawai ya ke shararawa.
Zuwan shi asibiti sai da ya girgiza,aiki suka fara yi mata sai dai abu ya cuttura doli ya fito ya kira number Noor ta Niger sai da ta kusa tsinkewa ya ɗaga bai bashi damar yin magana ya shiga ce mashi "urgence dan Allah in akwai jirgi mai zuwa ka dawo Innalillahi wa'inna iley raji'un Noor marâtre ce...."sai kuma ya kasa ƙarasawa saboda kuka a doli ya yanke kiran.
Ana shirin kiran sallah jirgin su Noor ya sauka ,direct asibitin ya wuce shi ma sai da ya girgiza yadda ya ga lokaci ɗaya yadda marâtre (uwar rainon su Abbas a gidan marayu)ta koma lokaci guda rabin fuskarta ya yashe yayinda ƙashin ƙafarta ya tsage zafin ciwon kuma ya so taɓa zuciyarta.
Cike da ƙwarewa Noor ya shiga yi mata aiki yayinda a doli aka canzawa fuskarta fasali,naman kanta kuma da ya fita a cinyar ta aka yanka aka yi ma dashe.
Ƙarfe biyun dare har da wasu mintinan sannan aka kammala yi mata aiki duka,cike da gajiya Noor ya shiga ɗakin da aka kwantar da Abbas tausayin abokin na shi ne ya ɗarsa ma shi doli ne ya girgiza domin marâtre tamkar uwa ta ke gare su tun tasowar su ba su san kowa ba sai ita.
Wanka yayi a nan cikin asibitin sannan ya samu tea ya sha,zugum yayi ya na tunanin Tirday irin borin da ta hau a kan zai tawo haka kawai yaji kukanta ya tsaya masa rai.
Ƙoƙarin hakiceta ya ke amman ina tayi katutu cikin zuciyar shi da kwanyar shi, da wannan tunanin barci ya ɗauke shi.
Washegari bayan ya dawo daga sallah asuba ya shiga ya duba Abbas ,jikin nashi kuwa yayi garas dama fargaba ce ta haifar mashi da ciwon.
Har ɗakin da aka kwantar da marâtre Noor ya kai shi,sharrr sai hawaye ganin yadda duk rabin jikinta ya ke naɗe da bandeji.
Ko da suka fito kallon shi Noor yayi yace "please kar ku bari Raliya ta san da haka saboda cikin jikinta"kai Abbas ɗin ya girgiza yace "in shaa Allah ba zan sanar da ita ba kuma zan gayawa abokanan ta kar su sanar da ita"
Wuraren tara na safe asibiti ta cika da marayu wai sun zo ganin marâtre ,haƙuri Abbas ya fara basu sannan ya kwantar masu da hankali,sauran marâtres ɗin ne kawai aka bari suka shiga su ma ta glass ne suka hangeta na'ura sai aiki ta ke a jikinta doli suka zubar da ƙwalla.
Abbas kuwa ya na zuwa gida ya tarar da Raliya na sharɓar barci a falo yayinda Hadeeyatullah ke kitchen ta na girki, murmurshi yayi lokacin da ya leƙa ya ga ta dafe ƙugu ta na kallon yadda wanke ke tsuuu cikin mai.
Jin kamar mutum a kaina yasa na waigo, murmurshi nayi tare da yi mashi alama da ya shigo ya gani.Ƙarasawa yayi wanken da cikin mai na nuna mashi wani ƙato nayi mashi alama da shi ne sai wani ɗan matashi na mashi alama da falo wato Raliya ce sai wasu ƴan ƙanana kusan biyar na taɓa cikina haɗi da nuna falo alamun yaran da Raliya za ta haifa ne.
Dariya yayi jin shirme na,sai yace min "to ke ki na ina?"shiru nayi can sai na maƙe kafaɗa na girgiza mashi kai dungure ni yayi da goshi yace "to ke yara dozin za ki haifa min"cike da Shagwaɓa na shiga bubuga ƙafafu shi kuma ya na dariyaya ta.
***Bayan wata biyu
Sosai jikin marâtre yayi sauƙi sai dai har yanzu ba'a cire bandejen ba,a lokacin kuma tuni Raliya ta sani dan dubiya mu ka tai.
Yunwa ni ke ji amman sam Abbas ya hana ni cin abinci kuma ban san dalili ba,baki kawai ni ke turowa shi kuma ya zuba min ido ya na kallo.
Mu na nan zaune Raliya ta fito ita ma cikin shirinta,mota mu ka nufa ga mamakina sai na ga Raliya ta shiga seat ɗin baya ni kuwa na shige gaba.
Ba mu zarce ko ina ba sai asibitin su,a cikin harabar asibitin na tsinkayi Dr Noor ya na saffa da marwa ya kasa zama ya kasa tsaye sai zagaye ya ke.
Tsayuwar motar mu ne ya sa shi yin tsaye cak ya ƙurawa Hadeeyatullah ido,wani irin tausayinta ya ke ji tun ɗaga ƙasan zuciyar shi.
Fuska Abbas ya tamke dan ya san dama za'a rina wai an saci zanen mahaukaciya,bai baiwa Noor damar tambaya ba gaisuwar da Raliya ta yiwa Noor ƙememe ya ƙi amsawa sai ni da ya kafe da ido.
Ciki mu ka shiga,gabana ne ya shiga bugawa da ƙarfi ganin Abbas ya fara cire min kaya yayinda Raliya ke gefe tayi zir haihuwar uwa ta ko pant babu a jikinta.
Ina ji ina gani Abbas ya cire min kaya,wani ƙyalle ya luluɓa min haka ma Raliya.
Wani ɗan matashin saurayi ya shigo ina kallo lokacin da ya yiwa Raliya allura da ƙashin baya,cikin kunne na Abbas ya raɗa min "ki kwantar da hankalin ki riga-kafi ne za'a yi maku yanzu zan maida ku gida kin ji ko?"kai na ɗaga dan har ga Allah maganar shi ta samu karɓuwa dan ba ƙaramin kwantawa hankalina yayi ba.
Ya na gama yi min allurar Abbas ya kwantar da ni sai a lokacin Noor ya shigo, dishidishi na fara gani ina jin lokacin da Noor ke cewa Raliya ta ɗaga hannunta ita kuma ta na cewa ta kasa ba ta iyawa to fah shikenan ban ƙara sanin abinda ke faruwa ba saboda barci mai kama da mutuwar da ya ɗauke ni.
Cikin ƙwarewa Noor ya fasa cikin Raliya daidai marar ta ya ciro baby ɗan wata uku da ƴan kwanaki tare da ɗaukar sa ya dasa shi cikin marar *HADEEYATULLAH*😭
Cikin mintinan da ba su wuce sha biyar ba aka gama komi tare da ɗinke cikin aka naɗe shi da bandeji,ɗankin hutu duk aka kai su.
Noor ya dubi Abbas yace "yanzu hakan da kukayi kun yi adalci ne?ta yaya yarinya ƙarama za ta iya ɗaukar cikin da ba nata ba?"shiru Abbas yayi bai ce komi ba Allah na gani wannan ce kawai hanyar da zai sa su ma su ga ɗan cikin su.
Ko kafin Sallah azahar Raliya ta farka dan allurar da aka yi mata ba ta mutuwar jiki ba ce duka, Hadeeyatullah kuwa sai washegari.
Yunƙurawa nayi in tashi sai dai mi?azaba naji ga cikina doli na koma na kwanta ina hawaye nurs ce ta fita sai ga ta sun dawo ita da Abbas ....
*_35-36_*
Wani mutumi daya kafa bakinsa a