Showing 18001 words to 21000 words out of 150413 words
Chapter 7 - Kwarya Tabi Kwarya Book Complet by Binta Umar Abbale .txt
a had'e.
kan kafet din ya zauna gami da tankwashe kafafunsa, a nutse ya tsiyaya bak'in tea a cup ya shiga kur'ba a hankali a hankali yana sauraran hirarrakin dasu Shatima keyi mafi akasari hiran ta 'yan mata ne, cup din tea ya ajiye a nutse ya bude wata silver farfesun zallan naman rago da dankali ne a ciki yayi kyau sosai sai 'kamshi yake Yaji yana sha'awar shan farfesun ya hada da bread a nutse ya zuba a plate ya kallesu da fadin"Bisimillah." Moddibo ya girgiza kanshi da fad'in" Ni dai Alhamdullhi ban san Shatima ba." Shatima dake duba wayarsa yace."Nima a koshe nake wallahi." Ba tare da yace komai ba ya fara shan farfesun yana had'ashi da bread....Modibbo ajiyar zuciya ya sauke ganin yana shan farfesun wani farin ciki ya cika masa zuciyarsa, dauke kansa yay suka cigaba da magana da Shatima.
Wani irin tari ne ya sarqe shi ya ajiye bread din hannunsa yana riqe kirjinsa tari yake sosai idanunsa sun cika da ruwa. Shatima ne yay saurin miqa masa ruwa ya kar'ba yana kokarin sawa a bakinsa ruwan na dawowa, sai kawai ya ajiye goran ruwan ya danne kirjinsa yana cigaba da tarin cikin galabaita ya mi'ke tsaye! sai suma suka miqe cikin tashin hankali suna rirri'keshi ya fadi a gurin, jini ne ya biyo bayan tarin da yake.......A gigice suka rufu a kansa suna k'okarin mikar dashi zaune.
Fitowa ta kenan daga gurin Dawakai Haruna ya karaso inda nake hankali a tashe yace."Sumayya Yarima Ali bashi da lafiya bayan fitarki daga sashen Tari ya sarqeshi ya dinga aman jini."
Kirjina na dafe cikin tashin hankali nace"Haruna wane irin aman jini kuma."? Yace."Aman jini dai da kika sani Sumayya yanzu haka sashen nasa a cike yake da 'yan uwa dan har maimartaba ma yana gurin ana bunkice akan abincin da yaci wallahi ke kadai nake tausayawa."
Kallonsa na shiga yi a tsorace nace"Haruna ni kuma meye laifina da kake tausaya min." Yana kokarin magana Hamza ya karaso gurin yace."Ke! Sumayya kizo ana neman ki a sashen Yarima." Naji gabana ya fad'i! Magana nake so nayi amma bakina yayi min nauyi, dakyar na iya furta kalmar innalillahi wa'ina ilaihi raji'un." nabi bayansu domin zuwa jin kiran da ake min......
*BINTA UMAR ABBALE*
*Kuyi sharing��*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE�_ *bintaumarabbale@gmail.com*
*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
25&26
Cikin tararrabi gami da fargaba muka shiga falon, gimbiya Lawisa ce a zaune akan kujera muna shiga ta mike tsaye da sauri tana watsa min mugun kallo! sunkuyar da kaina qasa nayi nace"Ranki ya dade barka da safiya." Hannu ta daga min cikin tuhuma tace"Me kika zubawa Yarima acikin farfesu wanda ya janyo masa aman jini."?
Gabana na faduwa nace"Ban zuba masa komai ba ranki ya dade." Marina tayi tana huci! tace"Zaki fad'a ko sai kin fuskanci hukunci mai tsauri."! Hannu na dafe da kuncina nace"Iya gaskiyata na fada wallahi ban sa masa komai ba." Za tayi magana Haruna ya katseta da fadin"Sumayya ki hau sama Maimartaba na bukatar ganinki." naji jinin jikina ya tsinke gabad'aya neman yawu nayi na rasa a bakina, salo salo na nufi saman ina adduar akan Allah ya fitar dani.
Lokacin dana shiga dakin sai naji na sare da al'amarin dan ganin yanda dakin ke ciki da jama'a gabad'ayan su suna tsaye a kansa yana kwance a bed kansa a cinyar mahaifiyarsa bakinsa rufe da wani abu da ya nuna alamun an tare jini likita ne a tsaye a kansa.
Sunkuyar da kaina kasa nayi na zube gwiwata a kasa nace"Barkan ku da wannan lokaci." Gabad'aya suka juyo suna kallona.......muryar Moddibo naji cikin tsawa yace."K'araso ciki munufaka." Na yun'kura da sauri na karasa gabansu na tsuguna! Moddibo zai sake magana maimartaba ya katse shi.
Shuru dakin yayi kafin maimartaba ya fara magana kamar haka.
"Sumayya wace irin guba kika sakawa Yarima a cikin abincinsa inaso ki fada min wanda ya saki zuba masa guba a cikin masarautar nan."! hawaye suka k'wace min nace" Na rantse da wanda raina ke hannunsa ban zuba masa komai ba, lafiya lau na gama abinci na bashi kafin na tafi gurin mu."
" 'Karya kike munufuka akwai abinda kika zuba masa wato kina so ki kashe ki ko."? Moddibo ne ke wannan maganar kamar zai kai min duka
Waziri ne yayi masa tsawa yayi shuru yana huci......Uwargida wato mai babban daki tace"Wato ba zaki fadi gaskiya ba kenan musu zakiyi akan binkicen da likita yayi akan farfesun da kika bashi yasha, to shikkenan tunda kina gardama ki dauki farfesun kisha mu gani."
Ina kuka nace"Ranki ya dade wallahi kiyashi ban ta'ba kashewa ballantana mutum, ni kuwa me Yarima yayi min da zan kasheshi dan Allah ku duba maganata kuyi binkice sosai akan al'amarin wallahi ban sa masa guba a acikin abinci ba."
Ciroma yace."Zaki rufe mana baki ko kuwa." Shuru nayi ina kallon qasan gurin nace"Ku gafarce ni na fada muku iya gaskiyata ne."
Dakin shuru yayi kowa yana jira yaji ta bakin Sarki, wanda yay shuru yana nazari tabbas al'amarin na bukatar bunkice kamar yanda yarinyar ta fada.
Itama Mamma tunanin da take kenan ba zai zama dole ace yarinyar ce ta zuba masa guba ba mybe akwai dai wata mak'arkashiyar shiyasa tayi shuru ba tace komai ba.
Sarki gyaran murya yay yace."Sumayya kin san girman Allah da Annabin Allah." Da sauri nace"Eh ranka ya dad'e." Yace."To magana ta k'are tunda har kinyi rantsuwa da Allah da annabi baki zubawa Yarima guba ba ki tashi ki tafi." Da sauri na kaskantar da kaina kasa nace"Godiya nake ranka ya dad'e.
Yunk'urawa nayi na miqe da fadi "Na barku lafiya." Babu wanda ya tanka min har na fita daga dakin.
Maimartaba ya kallesu a nutse yace."Ina ganin zamu tsananta binkice akan wannan al'amarin dan alamu sun nuna cewa yarinyar nan bata da alhaki akan wannan al'amarin saboda haka zamu bar maganar tunda Allah ya kiyaye gubar ba tayi tasiri a tare dashi ba ammafa hakan ba zai sa mu kasa d'aukar mataki akan duk wanda muka samu da alhakin faruwan wannan al'amarin ba." Waziri yace."Hakane ranka ya dad'e tabbas yanayin yarinyar ya nuna gaskiyarta sai a 'kara saka matakan tsaro a sashen nasa saboda gujewa faruwar wani abu makamancin wannan." Galadima da Ciroma shuru sukayi dan al'amarin gabad'aya bai musu dad'i ba sun so ace gubar ta kashe yaron kowa ya huta....... .
Ko kallonta banyi ba na nufi kofa da niyyar fita daga dakin. cikin tsawa tace"Ke! mai baqi kamar bakin tukunya tsaya anan gurin." kamar kada na tsaya sai dai na yanke shawarar tsayawa amma ban juyo ba.
Kamshin turaranta ne ya tabbatar min da cewa tazo inda nake na dago kaina ina kallonta tana yi min kallon kaskanci tace." Da izinin wa kike shige da fice a sashen Yarima." Wani kallo nai mata nace"Da izinin mahaifiyarsa." Girgiza kanta tayi tace"Itace ta baki guba kisa masa a abinci ko kuma wa." wani irin kallo nai mata nace'' Uwa ta haifi d'anta ta kashe shi anya kina da hankali kuwa."? Rai a bace ta kalleni tace"Ni kike fadawa wannan maganar."? Nace"To ai ji nayi maganar taki tayi kama data mahaukata."
Shuru tayi na minti biyu, kafin tace"Tunda kin zama mai kula dashi ta fannin abinci inaso nayi amfani dake domin cimma munufata."! Kallonta nayi babu walwala a tare dani nace"Wace irin manufa ce."?
Murmushi tayi tace"Kije zan neme ki gobe zamu tattauna." Girgiza kaina nayi na wuce daga gurin ina mamakin maganar ta
Gurinmu na koma a gurguje nayi wanka na sauya kaya kana na zauna domun karyawa hira muke da Tambaya amma koda wasa ban fada mata abinda ya faru ba, Tace"Sumayya babu abinda zamu cewa Yarima Ali kinga maganin nan da kika kawo jiya yana da kyau dan jiya gabad'aya babanki bai kwana da zazzabi ba kinga jikinsa ma gumi yake alamu na nuna lafiya ta samu." Nace"To Alhamdulilahi idan na koma sashen zanyi masa bayanin yanayin jikin nasa." Tace"Hakan yana da kyau ki 'karayi masa godiya." Nace "Insha Allah."
A gurguje na kammala karin kummalo na dauki jakar litattafaina sallama nayi mata na nufi gurin karatu.
'Karfe d'aya da rabi mun fito daga karatu hira muke da Lahira ina tunanin fada mata abinda ya faru, Lantana ta k'araso gurin. "Sumayya kije b'angaran Mamma Fulani tana son ganinki."
Gabana ya fadi ido na tsirawa Lantana ina so nayi magana amma bakina yayi nauyi ina kallo Lanatana ta bar gurin na garara cewa komai..........."Lahira dan Allah zoki rakani." A sanyaye nayi mata maganar. Tace"Muje Allah dai yasa ba laifi kikayi ba." Nace" Bana tsammanin hakan." Tafiya muke ni da ita kowa na sa'ke sa'ke a ransa. Lahira guri ta samu ta zauna a harabar gurin ni kuma na nufi kofar shiga falon masu gadin kofar ne suka bude min na shiga a nutse sallama nayi cikin nutsuwa na 'karasa inda suke zaune ita da yaron nata.
Gwiwa a kasa kaina a sunkuye nace"Ranki ya dade barkanku da wannan lokaci." Amsa min tayi a nutse tana gyara zamanta shi kuwa ko kallona baiye ba kanshi yana dukufe yana kallon kasan kafet kamar yanda ya saba.
"Sumayya." Sunana data kira yasa na dawo cikin hankalina. a nutse na amsa "Na'am ranki ya dad'e. " Inaso ki nutsu da kyau zamuyi magana dake." Ciki da tsantsar ladabi Nace"To ranki ya dade ina sauraranki."
"Sumayya kiji tsoron Allah kiji tsoron mahallicin ki ki fad'a min gaskiyar lamari shin waye ya saki zubawa Magajin sarki guba a cikin abinci? inaso ki fad'a min gaskiya akan al'amarin nan daya faru babu abinda za'ayi miki idan kin fad'i wanda yasa ki aikata wannan mugun aikin gaskiyar magana nake jira ta fito daga bakin ki.
Zuciyata ce ta karye hawaye na kokarin zubo min ina kokarin mayar dashi sai da ya zuba a raunane nace" Ranki ya dade wallahi tallahi Allah d'aya ne daga shi babu wani, babu wanda ya sani na zubawa Yarima guba a farfesu wallahi ban san yanda al'amarin nan ya faru ba." ina kuka na kare maganar.
Shuru falon yay na minti biyu kafin tace"Yi shuru ki daina kuka nayi miki wata tambaya." Hannu nasa na goge hawaye nace"Ranki ya dade ina sauraranki." tace"Bayan kin kammala aikin ki babu wanda ya shigo gurin."? Shuru nayi ina tunanin maganar.......
*BINTA UMAR ABBALE*
*Kuyi sharing��*
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE�_ *bintaumarabbale@gmail.com*
*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_
*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
27&28
"Anya Shatima da Moddibo zasu iya cutar da d'an uwansu? tunanin da nakeyi kenan a cikin zuciyata. ni dai nasan babu wani 'bako daya shigo sashen bayansu sai ni dasu Haruna bana tsammanin Abokanshi kuma shaqiqan 'yan uwansa zasu iya sa masa abunda zai kashe shi a cikin abinci. shuru nayi kaina a kasa ina tararrabin fad'ar maganar dake bakina.
"Sumayya ke nake saurare." Muryarta ce ta doki dodon kunnena.
A nutse nace"Ranki ya dade babu wani bako daya shigo sashen sai 'yan uwanshi wato Shatima da Maddibo sune suka shigo bayan na jera abincin a daning na hau sama domin in sheda masa lokacin dana sakko na samesu su biyu a falon." na karasa maganar ina sake sunkuyar da kaina......Fulani na shirin magana ya katseta da fad'in "Me kike nufi da wannan maganar kina nufin Maddibo ko Shatima wani na iya samin guba a abinci."? Shuru nayi gabana na fad'uwa sabida yanayin yanda yay maganar ya nuna min 'bacin ransa."
"Sumayya." naji ta kira sunana, amsawa nayi ina kallonta, tace"Tun ganina dake na farko naji kin kwanta min a raina sosai na yaba da nutsuwarki da hankalinki ina mutukar son mutum mai gaskiya da rikon Amana, inaso ki ri'ke amanar dana dam'ka miki hannu biyu kisa idonki sosai akan masu shige da fice a sashen babana, tunda ka kan 'yan uwanshi maza da mata da kuma sauran bayin dake cikin gidan nan inaso kisa idonki sosai akan shige da ficen su a sashen sannan ki dinga lura da abincinsa gami da abin shansa ruwa ko lemo ko makamancin haka Ina neman wannan alfarmar a gurin."
Cikin sanyin jiki nace"Insha Allahu zan kula da amanar da kika bani nayi al'kawarin bin umarninki." Murmushi tayi a nutse tace"Tashi kije Allah yayi miki albarka." na amsa da ameen ina jin sanyi a cikin raina. yun'kurawa nayi a nutse nace"A tashi lafiya ranki ya dade." Hannu ta daga min alamun naje da sauri na bar gurin zuciyata tas tabbas addua bata faduwa 'kasa banza.
A nutse ta kalleshi gami da fadin"Babana me ka fahimta a maganar yarinyar nan? ni ina ganin wannan al'amarin daya faru da akwai saka hannun 'yan uwanka ina nufin Shatima da Moddibo."
Kallonta yayi mamaki tattare a fuskarsa, tace"Ko shakka bana yi akwai saka hannunsa a ciki amma inaso kasa ido sosai a kansu sannan ka kula da kanka ba komai xaka ci a gabansu ba akwai mummunar manufa a zuciyarsu."
"Mamma bana tsammanin Shatima ko Moddibo wani zai iya cutar dani a cikinsu ni nafi tunanin wani abu yarinyar nan tayi amfani dashi gurin girkin wanda ya janyo hakan bana zargin kowa akan faruwar wannan al'amari.
Murmushi me ciwo tayi tace" Nima bana zargin kowa amma dai tunda nace maka kayi takatsantsan dasu to kayi domin hausawa na cewa makashinka na gindin ka nasan baka manta irin zaman marinar da akeyi a cikin gidan nan ba, kowa ka ganshi ka kalle shi kawai mafi akasarinsu babu kyakkyawar manufa acikin zuciyarsu."
Shuru yayi yana nazarin maganar mahaifiyar tasa.
***
Lahira tace"Wai ya naga kin fito jikinki duk a sanyaye." Ajiyar zuciya na sauke nace"Lahira ina cikin tsaka mai wuya amma na roki Allah ya fitar dani cikin ruwan sanyi." Tace"me ya faru." A nutse na warware mata dukkanin abinda ke faruwa.
Lahira a jiyar zuciya ta sauke tace"Gaskiya dole ki shiga tashin hankali amma mungode Allah da ya sanya Maimartaba da amaryarsa masu fahimta ne, daba dan hakaba nasan da tuni kina fuskantar hukunci."
Nace"Hakane Lahira amma shi Yariman bai yarda da cewa 'yan uwansa zasu cutar dashi ba ban san abinda ke cikin zuciyarsa ba." Lahira shuru tayi tana tunani kafin tace"Dama ai bai za ma lallai ya yarda ba saboda ganin sun taso tare abu makamancin wannan bai ta'ba faruwa ba a tsakaninsu dole ya shiga ko kwanton cewa zasu iya cutar dashi." Nace"nima nayi kokwanto da farko daga bisani da nayi tunani sai na gane hakan zata iya faruwa tunda yanzu gabad'ayansu idanunsu ya rufe babu abinda suke so sai mulki na fahimci cewa suna masa hassada dan ganin kamar shi zai gaji mahaifinsa." Lahira tace"Dama abinda yake faruwa kenan yanzu duk wani abu da 'yan uwansa zasuyi masa a kan mulki ne saboda haka shawarar da zan baki itace ki zage damtse ki kula da amanar da kika d'auka kiyi iyakacin bakin kokarin ki gurin ganin kin kareshi daga sharrin masu sharri."
A sanyaye nace"Insha Allahu zan lura zanyi iyakacin bakin kokarina."
Da wannan maganar muka rabu da juna.
Sosai nayi farin cikin ganin babana a zaune yana cin abinci da kuzari a tattare dashi, cikin farin ciki na ajiye jakata na zauna kusa dashi ina murmushi nace"Baba nayi farin cikin ganinka a zaune kana cin abinci da hannunka hakika hankalina na tashi a duk sanda zanga Tambaya na baka abinci a baki yau naji dadi sosai dana ganka ka samu lafiya kana ciyar da kanka abinci da hannunka." Murmushi yayi a nutse ya kalleni yace."Ai tun bayan fitarku ke da mahaifiyarki naji kwari a jikina da kaina nayi wanka nayi dukk sallolin da ke kaina Sumayya hakika bamu da abinda zamuyi wa Yarima sai dai addua gami da fatan gamawa da duniya lafiya naji dad'in taimakon da yayi min Allah yayi nufin zan samu lafiya ta dalilinsa hakan yasa na yanke shawara kancewa bayan sallar isha'i zaki rakani nayi masa godiya kan alkairin da yayi min."
Ina murmushi nace"Gaskiya ne baba Yarima ya cancanci godiya daga gurinmu insha Allahu zanyi maka jagora zuwa gurinsa kamar yanda ka bukata." Yace."To masha Allah kema ki dauki abinci kici dan naga kamar da akwai yunwa a tare dake." Cike da walwala nace"Baba lokacin dana shigo ina dauke da yunwa mai tsanani amma ganinka a zaune kana cin abinci da kanka yasa naji cikina ya cika yanzu bana jin yunwa ko kadan." Yana dariya yace."Sumayya ban yarda ba dole kici abinci domin bana son ki zauna da yunwa. kwanukan dake gabansa na janyo
Cike da tsokana nace"To bari na fara cinye wanda ka rage saboda na samu albarka idan ban koshi ba sai na karo wani." Hannunsa na dama ya d'ora a saman kaina fuskarsa dauke da yalwataccen murmushi yace."Allah yayi miki albarka Sumayya." Ina kokarin kai abinci bakina Na amsa da ameeen baba."
Tsaf na gama cikin abincin na gyara gurin na gyara masa shimfid'arsa kana na shiga tattaro kayan wankin mu kwata kwata bana san zama da daud'a shiyasa kullum gurin mu zaka sameshi a tsaftace babu kazanta ko kad'an.
Wanki na fito dashi tsakar gida na ajiye a guri guda kana na koma cikin dakin, na sameshi yana duba littafin addini nace"Baba bari naje na duba dawakai bana so hankalina ya dauke gurin wanki na manta ban basu abinci ba."
Ya kalleni yana girgiza kansa nasan abinda yake ji a zuciyarsa game dani,sunkuyar da kaina kasa nayi yace."Ina alfahari da Allah ya bani ke a matsayin 'ya kin fiye min haihuwar maza goma Sumayya ina alfaharin samunki