Showing 99001 words to 102000 words out of 150413 words
Chapter 34 - Kwarya Tabi Kwarya Book Complet by Binta Umar Abbale .txt
babu wanda ya nuna sha'awar zuwa a cikinsu Iyalin Uwar gida Huwaila irinsu aunty Safiyya suka dinga zare ido a gurin gaskiya sunji dadi sosai da Muddibo ya rufa musu asiri suma sunyi nasu sai dai kuma bai ka nasa muni ba!! Maimartaba yace kowa ya tafi gurinsa tunda gaskiya tayi halinta sai a jira hukuncin da al'kali zai yanke a kansa, jiki a sanyaye kowa ya fita daga gurin taron..........Ciroma na daf da shiga sashen sa ya yanke jiki ya fad'i!! Hadiman dake aikace aikace a gurin suka rufu a kansa suna ihu!!!! kafin kice kwabo tawagar 'ya'yansa dake cikin gidan sun fito, mazan ne suka daukeshi suka shiga dashi ciki dakinsa suka shiga dashi su kwantar dashi a gado sun kewaye shi suna yi masa firfita! Ciroma bakinsa ya murgud'e sai zubar da yawu yake! magana yake so yayi amma ya kasa, Hankalin iyalinsa ya tashi, Wali shine me bin Muddibo da sauri yace."Bari naje na kira Magajin sarki yazo ya dubashi." Hajiya Karima cikin tsawa! Tace."Wali ka sake ka kira Magajin sarki ya shigo sashen nan sai na d'aga maka nono wallahi sai na tsine maka albarka."!!! Khalisat tace."To Yanzu hajiya muna ji muna gani zamu barshi ya mutu i duba da ki ga yanda yake haki! jininsa ne ya hau da karfi."
Cikin karaji!! Lawisa tace"Khalisat ba za'a kira Yarima ba ai bashi kad'ai ne likita a duniya ba! saboda haka kawai kai Wali ku daukeshi kusa a mota mu nufi babban asibiti a dubashi." Wali yace." me zai hana a kira Dr Sa'adu ya dubashi a gida."?
Hajiya karima tace"Aa shawarar Lawisa zamu dauka ku daukeshi kusa a mota muje babban asibiti." Manniru yayi saurin fita domin bada umarnin fito da mota...
*Na kudi ne!*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya! keda kika futa da book din keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake.....Vip group #600 normal group #300....account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKAWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
89
Sai bayan fitarsu daga gidan tukkuna Maimartaba ya samu labarin abinda ke faruwa ransa ya 'baci sosai da abinda iyalin d'an uwansa suka zartar ba tare da saninsa ba, ace akwai babban likita a gida amma su daukeshi su kaishi wani asibiti domin su nunawa duniya halin da suke ciki, sosai ya dinga jajanta al'amarin a cikin zuciyarsa, Waziri ganin yanda ya damu da a'lamarin yasa ya dinga tausar sa da kalamai masu sanyi Sarki ya dan samu sassauci a zuciyarsa sakamakon rarrashinsa da 'yan uwansa ke masa amma dai duk da haka zuciyarsa na can tunanin halin da Ciroma yake ciki dalilin da yasa kenan gari na waye wa suka shirya zuwa asibitin domin duba jikin nasa.
Yanda suka tarar dashi cikin halin ciwo ya firgitasu dan gabadaya komai na jikin Ciroma ya daina aiki yana kwance sai dai ayi masa komai, Likitan dake tsaye a kansa ya sheda musu ciwar jininsa ne ya hau sosai sanadiyar tashin hankalin daya shiga amma insha Allah zai cigaba da kwanciya a asibiti su kuma zasu cigaba da kula dashi har ya samu lafiya."
Maimartaba girgiza kansa kawai yayi yana mamakin kudirar ubangiji Tabbas ya yarda da cewa d'an adam ba'a bakin komai yake ba duba dai lafiya lau suka yini da Ciroma amma lokaci guda Allah ya sauya masa hallita, babu shakka idan suka rasa dan uwansu ta sanadiyar bacin ran Muddibo ba zasu yafe masa ba........Umartar Wali yayi akan ya kira Magajin sarki a waya ya sheda masa cewa ya turo motar asibitinsa tazo ta dauki Ciroman yana ganin kamar haka yafi mutunci.
Hajiya Karima ita da zuriar ta babu yanda suka iya suna ji suna gani Magajin sarki ya turo da mota a kasa Mara lafiyan a ciki a ka tafi dashi asibitin, Tsabar bacin rai yasa hajiya Karima buge zaninta ta koma gida tare da fadin"Ba zata zauna zaman jinya ba mutukar ba sanja wa mijinta asibiti ba.
Maimartaba yace kowa ya kyaleta! dama asibitin basa bukatar 'yan jinya akwai ma'aikatan da suka san aikinsu sai kawai ya basu umarnin tafiya gida bayan ya kwantar musu da hankali akan rashin lafiyar mahaifin nasu............Koda suka koma cikin tsananin damuwa suka samu mahaifiyar tasu sai zubar da hawaye take, Lawisa da khalisat suka zauna suna taya ta kukan. abun duniya ya taru yayi musu yawa Muddibo ya jefa su a cikin tsaka mai wuya ga rayuwar mahaifinsu na tangal tangal.....Hajiya karima hawayenta ta share ta kalli 'ya'yanta cikin rawar murya tace"Yanzu haka zaku zauna ku zuba min ido ina kuka kuna kuka ba zamu zauna mu nemawa kanmu mafita ba."
Wali yace."Hajiya wace irin mafita kike so mu nemawa kanmu? duk fa abinda kika ga ya faru to da sanin Allah saboda haka dan ki kada kice zaki dauki fansa saboda nasan halinki da ri'ko! Muddibo shine ya janyowa kansa masifa muma gashinan ya jefa mu a cikinta a yau da kwanan mahaifinmu ya kare da tuni sai dai labari."
A harkuqe! tace"Dallah malami rufe min baki mai matacciyar zuciya! ayiwa dan uwanka sharri amma ka dinga cewa shine ya janyowa kansa wato kana nufin kaima ka yarda da sharrin da'aka liqa masa."
Cike da mamaki! yake kallonta kafin yace."Hajiya dan Allah ki nutsu ki shiga hankali ki daina wannan abinda kikeyi mutane zasu dauka kin samu ta'bin hankali! wannan fa al'amarin da gaske ne Muddibo ne ya aikata ba sharri akeyi masa Kin saurari muryarsa a lokacin da yake shedawa hukuma gaskiyar lamari amma saboda san zuciya kina cewa sharri a kayi masa."
Lawisa na kuka tace"A gaskiya Yaya Wali ka bani mamaki wallahi wato kai ba zaka iya rufa asirin dan uwanka ba ko kenan yanzu ranar litinin din ba zakaje kuto ka bada sheda a kansa ba."
Dafe kansa yayi cikin tsantsar damuwa yace."Wace irin sheda zan bayar a kansa bayan da bakinsa ya fadi gaskiyar magana, dole zanje kuto domin jin irin hukuncin da sharia zata yanke a kansa."
Munniru yace."Ni wallahi na rasa ma abinda keyi min dadi a rayuwata nayi nadama nayi dana sani dana fito a cikin wannan masarauta gabad'aya bamu da power a masarautar nan komai mune a baya ai dole 'bacin rai yasa hawan jini ya kama babanmu.
Hajiya Karima ta share hawaye cikin takaici tace"Ai Munniru ba kuga komai ba a yanda babanku yake bani labarin yanda mahaifinsa yasha wuya a cikin masarautar nan sai kunyi mamaki mutuka! zuri'ar Abdullahi Adamu ta riga ta kwace sarauta ta kafa kanta ta hana kowa ya kar'ba daga hannunta ni wallahi har yanzu banga laifin Muddibo ba dan yayi yunk'urin kwatar hakkinsa, bari na fad'a muku abinda baku sani ba zuri'ar Abdullahi Adamu sune suka kashe kakanku da bakin ciki sai wayar gari akayi da gawarsa ya mutu da bakin ciki!
Munniru ya buga bango(garu) da hannunsa yana huci! yace."Tur! da zuria'r Abdullahi Adamu wallahi sun kasance azzalimai masu san kansu da yawa meye amfanin mu a masarautar nan da mu zauna muna ganin bacin rai a gwara mu tattara kayanmu mu fita daga cikinta..
Wali yace."Baka da hankali ko Munniru idan mun bar masarauta kana inda zakaje."? shuru yayi yana huci! Wali ya cigaba da cewa"Ka nutsu ka zauna kayi tunani malam komai kaga na faruwa to da yardar Allah idan Yayi nufin mulki ya cigaba da tabbata a hannun zuri'ar Abdullahi Adamu to babu yanda zamuyi idan kuma yayi niyyar k'wace mulkinsa ya kwace ya dawo dashi hannunmu kuma abunda nake so kuyi la'akari dashi anan shine Waziri da Galadima me yasa basa tayar da hankalinsu akan mu! kada ku manta suma fa suna da hakki amma sunyi shiru sun zubawa sarautar Allah ido ba wai dan basa sha'awar mulkin ba dukkaninsu suna so suna sha'awa sai dai babu yanda za suyi da abinda Allah ya hukunta saboda haka dan Allah kuma inaso ku hakura ku barwa Allah ikonsa kuma insha Allah idan baba ya samu sauki zan zauna na fahimtar dashi cewa shi mulki na Allah ne sai wanda ya za'ba yake bawa ba'a yiwa Allah dole akan ikonsa kowane irin hukunci ya zartar daidai ne."
Jikinsu ne yayi sanyi da nasihar da d'an uwan nasu, da alama dai duk cikinsu shine mai kyakkyawar zuciya tunda gashi nan ya zaunar dasu yana nuna musu abinda ya dace Ubangiji Allah yasa zasu dauki nasiharsa su hakura su barwa Allah ikon sa.
Bayan kwana biyu jikin Ciroma yayi sauki dan Magajin sarki ya tsaya a kansa sosai da sosai ya bashi dukkanin kulawar da ake bukata, alhamdullhi yanzu an samu yana iya sarrafa hannuwansa sai dai har yanzu idan yana magana ba'a fahimta sosai saboda yanda bakinsa ya karkace yana zubar da yawu....Ganin yanda hankali Maimartaba ya tashi akan hakan yasa ya zauna sosai ya kwantar masa da hankali yace."Insha Allah zai samu sauki ya dawo normal kamar yanda yake, jin haka yasa Maimartaba da 'yan uwansa hankalinsh ya kwanta, Suma su Lawisa suka kwantar da hankalinsu dan ganin yanda jikin mahaifin nasu yayi sauki sai dai har yayi kwana hudu a asibiti Hajiya Karima ba taje ba tana nan har yanzu da mugun nufi a cikin zuciyarta, cikin masarautar babu wanda bai je ya duba Ciroma ba amma ita da take a matsayin matarsa uwar 'ya'yansa ba taje ba tana zaune a gida tana sa'ka mugun abu a cikin zuciyarta.
*RANAR LITININ*
Kuto ta cika ma'kil da jama'a ana ta gabatar da shari'a yanda addinin musulunci ya tanada mai girma mai shari'a malam Umaru Musa ya d'auki takardar dake gabansa a nutse yake duba takardar yana girgiza kai! farin gilashin dake idonsa ya zare a nutse yace." Insha Allahu zamu kamanta adalci kuma zamu yankewa mai laifi hukuncin da addinin musulunci ya tanada muna rokon Allah yasa hakan ya zama izina ga masu hali irin na *Al'amin AbdulJabbar wanda akafi sani da Muddibo* Hukuncin da addinin musulunci ya tanadarwa dukkanin wani musulmin daya aikata kisa yana sane to shima akashe shi! Alhamdullahi wanda ake zargi da aikata laifin kashe masu rai guda uku ya amsa laifinsa ba tare daya wahalar da sharia ba saboda haka kuto tana bukatar ta saurari muryar wannan yaro a lokacin da yake wa hukuma bayanin yanda akayi yake aikata wannan 'barna kuto da jama'ar dake cikinta na bukatar su saurari jawabin da yayi domin kowa ya tabbatar da hukuncin da zamu yanke a kansa daidai yake da addinin musulunci."
Da sauri wani dan sanda dake tsaye a gefe ya dauko wayarsa a take ya kunna rocoding din da Acp yayi wa Muddibo a lokacin da yake jawabi a ofis dinsa......tun kafin rocoding din ya kare gurin ya kaure da haniya kowa na fadar albarkacin bakinsa, Muddibo dake tsaye gurin tsayuwar masu laifi ya sunkuyar da kansa zufa sai keto masa take hakika bai ta'ba nadamar rayuwa ba sai yau, jama'a sai zaginsa suke suna ala wadai dashi.......Wali da Muniru sai girgiza kai sukeyi suma tamkar su fashe da kuka su kad'ai ne suka iya halartar kuto Hajiya Karima dasu Lawisa suna gida suna kuka saboda jikinsu ya riga yayi sanyi da jin irin kotu'n da'aka kai Muddibon kotun musulunci ce tsantsa kowa yasan Malam Umaru Musa tsayayyan al'kali ne wanda yake yanke hukunci akan doron gaskiya Kudi ko mulki na mutum basu isa susa shi ya kauce hanya ba komai muqamin mutum mutukar yayi laifi baya d'aga 'kafa sai zartar da hukuncin da addinin musulunci ya tanada
Maigirma mai shari'a ya bada umarnin akan cewa kotu ta samu nutsuwa, nan take kowa ya nutsu gurin yayi tsit! A nutse ya cigaba da cewa''Saboda haka kuto zata yankewa Al'amin Abduljabbar hukuncin kisa kamar yanda ya kashe shima za'a kashe shi!! ta hanyar rataya."!! yana gama maganarsa ya buga tevur din gabansa da wani d'an katako! hukunci ya tabbata da izinin Allah! mikewa yayi gabad'aya jama'a suka mi'ke suna kiran sunan Allah.
"Allahu Akbar! Allahu Akbar! Allahu! akbar!! 'Yan sanda kusan hudu suka kewaye Muddibo a rirrike a ka fito dashi yana kuka yana d'agawa su Wali hannu aka fita dashi y'an jarida da jamaa suka bi bayansu.......Wali da Munniru rungume juna sukayi suna kuka Wali yace." Munniru kaga irin rayuwar da nake gudu ko ka duba ka gani yanda Muddibo zaiyi mutuwar wulakanci jama'a sai tsine masa suke saboda mugun abunda suka aikata, dan Allah Munniru komai rintsi ka rike gaskiya kada kabi san zuciyarka irin na Muddibo." Munniru hawaye kawai yake sharewa yana girgiza kansa tabbas duniya abar tsoro ce shikkenan yanzu sunyi bankwana da dan uwansu.
*Allah kasa mufi karfin zuk'atan mu amin.*
Hajiya Karima faduwa tayi ta suma lokacin da ta samu labarin hukuncin da ya sauka akan d'anta koda ta farfado ma sambatun surutai ta dinga yi tamkar wata mara hankali sai alwashi take ci akan wallahi ba zata yarda ba sai ta dauki fansa! Wali ya rungumeta a jikinsa yana mata addua yana share hawaye.........A ranar Maimartaba kasa zaman fada yayi saboda tashin hankali yaje ya kwanta a sashen Fulani yana tunanin rayuwa......Magajin Sarki da Shatima yini sukayi cikin alhini da damuwa amma daga baya da suka zauna sukayi tunani sai suka ga hukuncin da mai shari'a ya zartar akan Muddibo shine daidai hausawa na cewa da kunyar lahira gwara ta duniya watakila hakan na iya janyowa Allah ya gafarta masa zunubansa, saboda haka sai dukkaninsu suka kwantar da hankalinsu su tsananta addua akan Allah yasa haka shine yafi alkairi a rayuwar d'an uwan nasu....
*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi ba tare da kin biya ba! keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina bukatar biya ga yanda abin yake......Vip gruop#600 normal gruop#300 account number... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
90
Masarauta da jama'ar dake cikinta sun jima cikin alhini da damuwar abinda ya faru. mussaman 'bangarar Uwargida Huwaila ita da zuri'arta babu wanda ya kaisu shiga tashin hankali dan ganin irin hukuncin da ya sauka akan Muddibo duk sai suka tsorata kowacce ta shiga nutsuwarta dan saboda sun san koda sune suka aikata abu makamanci na Muddibo baza su tsira ba, sosai uwargida da iyalinta suke godiya ga Allah da bai nufi Muddibo ya kiran sunan d'aya daga cikinsu ba! wannan dalilin yasa kowacce ta nemi guri ta zauna a dakinta yanzu ba sosai ma suke zuwa masarautar ba saboda gudun kada asirinsu ya tonu..........Alhamdulillahi jikin Ciroma yayi sauki sosai dan yana iya komai da hannayensa sannan yana tafiya da kafafunsa sai dai rashin kuzari da bai dashi amma ya samu lafiya sosai Magajin sarki ya tabbatar musu da cewa zai warware idan an kwana biyu, Satin sa uku a asibiti ya dawo gida, duk irin kulawar da Magajin sarki keyi akan Ciroma baya burge Hajiya Karima kullum cikin zaginsa take tana kwashe masa albarka da fad'in "Yanda yayi sanadin mutuwar d'anta itama sai tayi sanadin mutuwarsa........duk sanda tayi wannan furucin sai Wali yayi mata nasiha harzuqa takeyi ta rufeshi da fad'a haka yake fita ya barta ransa a 'bace! bangaran Lawisa kuma ta dan samu sassauci kuma ta rage jin haushinsa tunda yayi sanadiyar samun lafiyar mahaifinta amma da itama ta k'ullaceshi a zuciyarta saboda yayi sanadin mutuwar dan uwanta! gabadaya idonsu ya rufe sam basa hango laifin Muddobo su dai suna nan akan bakansu na cewa sharri akayi masa, duk sanda zasuyi wannan furucin Wali hauka yake d'ora musu ya bar musu gurin dan takaici!! Ya lura Lawisa halinsu d'aya da mahaifiyarsu amma Munniru da Khalisat idan yayi musu magana suna ji kuma sun daina zagin Zuri'ar Maimartaba suna zaune lafiya da kowa a masarautar..............To Sati na uku a b'angaran Fulani gabad'aya na sanja fatar jikinta ta washe na 'kara qiba! su kansu sutturun da nake amfani dasu a jikina abin kallo da sha'awa ne duk wasu kayan kyale kyale da 'kawa na sarauta Mamma tasa an kawo min ina amfani dasu, kullum cikin ado da kwalliya nake na fito na zauna kusa da ita muyi ta hira Fulani wayayyiyar macace ta saki jikinta dani yanda na lura gabadaya bata suruktaka dani dan watarana ma idan nayi ado da irin kayan sarautar itace ke gyara min sai taga yayi daidai sannan hankalinta zai kwanta, a tsayin satikan da nayi a gurinta na koyi abubuwa da yawa na sarauta dana yau da gobe, sannan kuma sa'i da lokaci na kanje na gaisa da iyayena cikin walwala da farin ciki..............Cikin nutsuwa na fito daga daki na sameta a inda ta saba zama domin hutawa, kusa da ita na zaune a nutse nace"Mamma barka da hutawa." da murmushi a fuskarta tace"Barka kadai Sumayya yau kin wuni kina bacci baki fito da wuri." Murmushi nayi ina wasa da hannayena nace"Wallahi kuwa ni kaina nayi mamakin baccin da nayi sai da nayi tunanin ko maganin murar dana sha ne ya kashe min jiki."
Tace"Eh kwarai kuwa hakan zata iya kasancewa." Shuru nayi kaina a kasa kusan kullum idan inaso naje na duba mahaifana nakan ji kunyar fada mata, kwata-kwata bana so taga rashin kunyata.
Murmushi tayi tace"Sumayya kina so kije ku gaisa da iyayenki ko."? murmushi nayi tare dayin kasa da kaina. zamanta ta gyara tana murmushi