Showing 42001 words to 45000 words out of 150413 words
Chapter 15 - Kwarya Tabi Kwarya Book Complet by Binta Umar Abbale .txt
wannan number
*07084563262*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
53&54
Wai shin da wane ma'auni zan auna irin wulakancin da guy nan yake min? me nayi masa kullum yake wulakanta ni yake cin zarafina yana tozartani! a ganina ban cancanci haka daga gurinsa ba, ina ruwansa da alaqata da Haruna da har zai dauki zafi! ya kiramu fasikai wannan kalma daya kiran mu da ita tafi damuna akan watsa min fruit salad din da yayi.
Hannu nasa na share hawayen daya kasa daina zuba, na mike jikina a sanyaye na shiga gyara gurin ina jin wani irin zafi a zuciyata tsaf na gyara gurin na nufi kofa da niyar fita, kicibus mukayi da Haruna kallona ya shiga yi yana nazari, nayi saurin sunkuyar da kaina ina kokarin magana yace."Sumayya me ya 'bata miki jikinki."? Ji nayi zuciyata ta karye hawaye suka zubo min, murya na rawa nace"Haruna muje kada ya sauko ya same mu a tsaye."
A sanyaye ya bude min kofa na fita ya biyo bayana, sai da mukayi nisa sosai na sheda masa abinda ya faru Haruna shuru yay yana girgiza kansa yace."Sumayya ni dai banga abinda mukayi wanda ya kaucewa sharia ba amma zan kiyaye shige miki idan kina gurin kada wata maganar ta sake biyo baya.
Nace"Nima haka na gani amma wannan shawarar daka yanke itace tafi amfani idan kana so muyi hira ka bari idan na gama abinda nakeyi na fito sai muyi hirar." Yace."Babu damuwa anjima zan sanar da mahaifina maganar auramu sai ya samu baba Lawi su tattauna." Murmushi nayi nace"To shikkenan hakan yayi.'
Haruna har sashenmu ya rakani na sanjo kaya na fito ya rakani sashen Ciroma domin amsa kiran da Gimbiya Lawisa keyi min.
Samun ta nayi a hakimce bayin ta sun kewaye ta sai fadanci sukeyi durkusawa nayi ina gaisheta, a wulakance ta amsa, ta dubesu tare da basu umarnin tashi. da sauri suka bar gurin.
Minti biyar a tsakani naji muryarta." Sai yanzu ki kaga damar zuwa."? cikin nutsuwa nace"Afuwa ranki ya dade aiki nake a lokacin da kika aika kirana ki gafarce ni."
Shuru tayi tana watsa min kallon banza tace"Sumayya anya kuwa kina aikata aikin da nake sanya ki kuwa nifa bana ganin canjin komai a gurin Yarima kullum iskanci yake min ya'ki ya dinga nuna min so da kulawa.
Nace"Haba ranki ya dade ba zan ci amanarki ba ina aikata aikin ki akan tsari kin san komai sai a hankali insha Allah zaki shawo kansa zai soki ya kaunaceki tamkar ransa.
Murmushi tayi tace"Sumayya shiyasa nake sonki domin kina kwantar min da hankalina amma al'amarin Yarima Ali ya soma bani tsoro wallahi.'"
Murmushi nayi nace"Ranki ya dade ki yawaita addua kina rokon Allah ya janyo miki hankalinsa kanki gefe guda kuma kina 'yan daburu irin namu na mata.
Gyara zamanta tayi tace"Sumayya duk dabaru na sun kare wallahi kullum na kai masa ziyara da fada muke rabuwa gabadaya ma ni gani nake kamar tunaninsa na wani guri bana gabansa.
Shuru nayi ina nazarin abinda zance mata naji tace"Ko kina ganin na bashi kaina ne."? na kalleta da sauri inayi mata kallon mara hankali .....Tace"To Sumayya duk wasu dabaru nayi ya'ki karkato da hankalinsa kaina.
Nace"Ranki ya dade idan kika bashi kanki ya sanki a matsayin mace ai kin cutar da kanki ko kunyi aure ba zakiyi daraja ba kuma wulakancin da zaiyi miki sai yafi nada, kada kiyi wannan gangancin ki cigaba da dayin 'yan dabaru insha Allah za'a dace."
Ajiyar zuciya mai zafi ta sauke tace"Shikkenan Sumayya zan cigaba da bin shawararki." Nace"Yawwa ranki ya dade......Akushin dake gabanta tace"Ki dauka wannan ki kai masa farfesun kifi ne nayi masa ki tabbatar yasha farfesun dan na zuba sinadarai a ciki kuma ina saka ran zanci galaba."
Nace"Angama ranki ya dade yanzu kuwa zanje na aikata aikin ki." Akushin na dauka na rike hannu biyu nai mata sallama na bar gurun......Lantana dake la'be tana ganin fitowar Sumayya a hankali tabi bayanta
Ina isa inda nake zubar da kayan asirin na waiwaya ko'ina sai dana na tabbatar da babu kowa a gurin na watsar da farfesun da sauri na rufe akushin na bar gurin ina jin takaicin abinda ke faruwa.
Ko zaman minti goma banyi ba sakon kiran Lawisa ya iskeni, Cike da mamaki nake kallon 'Yar aiken, inaso nayi magana Babana ya katseni da fadin na tashi naje....jikina ya bani akwai wani abu mikewa nayi nasa takalmana nabi bayan 'Yar aiken.
Tsaye muka sameta tana kaiwa da kawowa a gurin, fuskarta kawai ta isa ta nuna min akwai matsala "Ranki ya dade gan......Kafin na karasa ta wanka min mari! tana huci tace" Sumayya ashe dama munafurta kikeyi ? ashe duk abinda nake baki zuwa kike kina zubarwa.''
Gabana ya yanke ya fadi baki na rawa nace"Ranki ya dade waye ya fada miki haka? wallahi karya ne ina bin umarninki.'' Wani marin ta sake kawo min nayi saurin kaucewa ina binsu Lantana da kallo sai 'kus-'kus sukeyi tabbas a cikinsu wata ta kawo gulmar.
"Bazan yarda da rantsuwarki ba Sumayya sai kin tabbatar min da gaskiyar magana daga bakin ki kana kuma ki nuna min inda kike zubar min da kaya.''
Shuru nayi zufa na keto min.
" Ke nake saurare 'yar iska munafuka kawai."
Naji ciwon zagin da tayi min amma sabida nasan nice bani da gaskiya yasa na cije nace"Ranki ya dade dik wacce ta kawo miki gulma gaskiya ne duk wani kayan asiri da zaki bani nasawa Yarima abinci da ruwan sha zubarwa nake a wani kebantacen guri idan baki manta ba ko dazu sai dana sake tunasar dake cewa asiri ba zai janyo miki kauna da so ba nace miki ki dage da addua sannan kuma ki canza salo, wannan dalilin yasa nake zubarwa saboda ba zan jefa kaina a halaka ba."
Huci! ta dinga yi tana kallona tace"Shin kin san irin mak'udan kudin da ake fitarwa kafin a 'karbo maganin nan kuwa."? shuru nayi mata tace"Lallai Sumayya baki da mutunci kuma wallahi sai na dauki tsatstsauran mataki a kanki ki shige muje ki nuna min inda kike watsar min da kaya."
Nace"Ranki ya dade ki gafarce ni banyi hakan dan na bata miki rai ba ina guje miki fushin Alla....Hannu tasa ta gwabe min baki! rufe min baki munafuka kawai wallahi sai naci mutuncinki a gidan nan." shuru nayi ina kallonta tasa takalmanta tayi gaba suka rufa mata baya, sai da sukayi nisa kana nabi bayansu..
a gurin na same su Lantana tana nuna mata ramin da nake zubawa. juyowa tayi tana kallona na sunkuyar da kaina kasa, rai a bace ta juya suka rufa mata baya.....wata rumfar bukka na samesu sai zurga zurga take tana magana dasu.
Ina karasowa gurin tace nasa gwiwata a kasa, nayi yanda tace kallonsu tayi tace su biyo layi kowacce ta mare ni hagu da dama.
Mikewa nayi ina kallonta nace"Ranki ya dade ke nayi wa laifi dan haka ke zaki hukunta ni basu ba.''
"Sumayya so nake ki 'kask'anta yanda kika sa raina baci kema naki sai ya 'baci."!
" Ranki ya dade ki gafarce ni ba zan zauna wanda muke matsayi daya dasu su mare ni ba gaskiyar magana kenan."
Tana huci! tace"Ni kikewa gardama ko."? kasa nai da kaina babu yanda xa'ayi na zauna su Lantana su mareni duk abinda za tayi sai da tayi.
"Lantana je ki kirawo min Buba kice yazo da bulalarsa." Lantana da sauri ta tafi....hannu ta goya a baya ta shiga zagaye gurin
cikin zuciyata nace wahalalliyar banza da wofi kawai.
Buba da Haruna na tare suna hira Lantana ta isa gurin ta shedawa buba kiran da ake masa, Buba yace kije ganinan zuwa...
Haruna jikinsa ne yay sanyi yace"Buba dan Allah kada ka doki Sumayya akan gaskiyarta."Buba yace."Idan tana tsaye a gurin dole nabi umarninta idan ta bar gurun zan kyaleta amma dai duk da haka zan dinga dubarar dukan kasa a madadin ita nake duka."
Yana kare maganarsa yay saurin barin gurin, Haruna jikinsa dik yayi sanyi kwata kwata baya so a ta'ba lafiyar Masoyiyarsa. yana kokarin mikewa Buba ya karaso gurin hannunsa nannade da murtukekiyar bulala mai baki biyu, ko sauraransa beyi ba yay gaba.
Haruna da sauri ya nufi sashen Yarima domin ya sheda masa abinda ke faruwa.
Sai da gabana ya fadi ganin katuwar bulalar dake hannun Buba, gumi ya dinga tsiyaya a jikina dana sani na yarda su Lantana sun mareni da tuni an wuce gurin.
"Ranki ya dade gani." Buba ya fada yana me kaskantar da kansa....
jajayen idanunta ta watsa masa tace"Buba so nake ka zane jikin Sumayya har sai rigarta ta yage wallahi idan ka sassauta mata sai ka fuskanci hukunci daga gurina."
Murmishi yayi irin na mugunta yace."Angama ranki ya dade." Bulalar ya daga da karfi gaske ya labta min a gadon bayana, kara na saki na rintse idona ina jin radadin zafi a inda ya doke ni....Gimbiya Lawisa murmushi tayi suma su Lantana suka soma dariya, ido jawur nake kallonsu....Buba na dariyar shakiyanci ya sake daga bulalar zai labta min "Kai kar ka daketa." da sauri na bude idona! yana tsaye a gurin haruna na gefansa gani nayi kowa ya shiga hankalinsa har ita Lawisan ta sunkuyar da kanta.
Hannu nasa na sharce gumin goshina ina godewa Allah da zuwansa gurin........'"Kai buba me tayi maka kake mata irin wannan dukan."? yana watsa masa harara yake maganar. Buba yace"Ranka ya dade umarnim gimbiya lawisa ne amma ni Sumayya ba tayi min komai ba."
Yace."To duk ku bar gurin nan." Buba dasu Lantana suka bar gurin...yunkurawa nayi zan tafi yace."Ke! ku sameni a gurina domin naji ta bakin kowa dan na fahimci akwai rashin jituwa a tsakaninku.'' gurin ya bari haruna yabi bayansa.
Kawai sai na tsinci kaina da watsa mata kallon banza a fusace na bar gurin....Gimbiya lawisa a sanyaye ta nufi sashen Yarima saboda tana tsoron abinda zai biyo baya tana tsoron ya tozarta irin na kwanakin baya
*Na kudi ne...*
Allah ya isa kika karanta baki biya ba idan kina so ki biya ga yanda abin yake......Vip group #600 normal #300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank....idan kati zaki turo kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa Dashan Allah✊�)
51&52
Shara na samu Tambaya nayo shigowata yasa ta dakata ta tsaya tana kallona. kasa cewa nayi da ita komai nayi saurin shigewa daki, Tambaya kasa nutsuwa tayi ta ajiye tsintsiyar hannunta a sanyaye tabi bayanta, samuna tayi a zaune na zabga tagumi, shigowarta tasa nayi gaggawar cire tagumin ina kallonta xama tayi gefena a nutse tace"Sumayya lafiya na ganki kin shigo jikin ki a sanyaye ina fatan ba wata matsala bace."? shuru nayi ina kallon kasan gurin, shawarwari nake da zuciyata yana da kyau na sanar da mahaifiyata abubuwan da suke faruwa saboda ina jin tsoron wani mummunan abu ya faru nasan nida iyayena zamu shiga uku, ni sam ban san me yasa baya so mahaifiyarsa tasan abinda yake faruwa ba, kuma idan akace za'a cigaba da tafiya a haka to babu shakka ni dashi rayuwarmu na cikin matsala domun 'yan uwansa basa kaunarsa zasuyi amfani da yardar da yake musu su cutar dashi babban burinsu suga baya motsi a duniya inda shi kuma ya kasa ganewa kullum gani yake ba zasu ta'ba cutar dashi ba.....A sanyaye na warware mata abunda ke faruwa babu abinda na rage mata, yanda na lura itama jikinta yayi sanyi amma domin ta kwantar min da hankali yasa ta dafa kafad'ata tace"Sumayya ki nutsu kinji ko ki daina sa wasiwahsi a cikin zuciyarki insha Allah ba zasuyi tasiri a kansa ba duk sharrin da suke shiryawa zai koma kansu, kamar yanda yace baya bukatar mahaifiyarsa tasan abinda ke faruwa to kiyi shuru kada ki sheda mata, shawarar da zan baki shine ki tsananta gurin kula da shige da ficen masu shiga sashensa, sannan ki kula da duk wani abu naci da zasu kawo masa insha Allah duk sharrinsu sai ya koma kansu, ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai faru sai ikon Allah."
Ajiyar zuciya na sauke ina kallonta hakika naji sanyi a zuciyata sakamakon kwantar min da hankali da tayi nace"Insha Allahu zan kula kuma ba zan fada Mamma Fulani maganar ba, zan cigaba da kula dashi ina addua kema a matsayinki na mahaifiyata ina rokon ki ki taya ni addua Allah ya kareni daga fad'awa cikin mugun hali."
Tambaya tace"Kada ki damu Sumayya kullum cikin yi miki addua muke insha Allahu kuma adduarmu ba zata fad'i kasa ba.
Nace"Nagode sosai ina fatan kin bude akwatin kin duba kyautukan dake ciki. Da murmushi a fuskarta tace"Ban bude ba kada ki manta da zaki fita cewa kikayi sai kin dawo sai mu bude."
Mikewa nayi ina yar dariya nace"Da kin sani kin bude kin rigani gani ai kina da iko akan duk abinda ya dangance ni." Tambaya mirmushi tayi ba tace komai ba tabi ta da kallon kauna da tausayi.
Cikin nutsuwa na bude akwati nasa hannu ina fito da kayan ciki. Manya manyan lifayu ne guda uku sunyi kyau sosai sun kuma birgeni mutuka sai na dinga hango kaina a ciki nasan zasuyi min kyau kasancewa ta doguwa....sauran kayan na cigaba da dubawa, d'inkakkun atampa guda biyu supar da ingila anyi musu dinkin mutanan Nijar rigunan har gwiwa anyi musu ado da bakin leshi mai tsada... mayafai da takalma biyu sai turare biyu sai set din mayukan shafawa, Tambaya bakinta kasa rufuwa yayi ta kasa daina duba kayan sai farin ciki take tana godiya, ina mirmushi na dauki 'yar karamar akwatin da zoben gold din ke ciki na bude a nutse na fito da zoben ina duba shi sai kyalkyali yake yanda nake jin nauyinsa a hannuna nasan zaiyi kudi sosai Tambaya tace"Kai amma wannnan zoben yana da kyau sosai duba sai kyalli yake."
Nace"Tambaya gold ne Mamma ta bani wai nasa a hannuna nayi ado dashi." Tambaya ta kar'bi zoben tana dubawa, kawai sai hawaye ya shiga zobowa a fuskarta, da sauri na kalleta ina mamakin kukan da take.
Girgixa kanta tayi tace"Sumayya dole nayi kuka nayi mamaki! yanzu kece zaki saka zoben gold a hannunki tinda nake a masarautar nan ban ta'ba ganin baiwar da tayi ado da gold ba sai *murjani* amma cikin ikon Allah ke anyi miki kyautar zoben gold mai dauke da tambarin masarauta babu shakka Sumayya kin kafa tarihi a cikin bayi.
Mirmushi nayi na girgiza kaina ina kara duba zoben ni kaina ina mamakin al'amarin dan sai da ta fada ma sannan na duba zoben sosai naga tambarin masarautar jiki, ajiyar zuciya nayi na zura zoben a ya tsana na tsakiya, sosai yay min kyau na mika mata hannuna, rikewa tayi ta goge fuskarta da fad'in "Yanda kika sa shi bana fatan duk rintsi ki cireshi inaso ya dawwama a hannunki har ranar mutuwarki."
Hannu nasa na goge mata fuska da fad'in "Ki daina hawaye rabona ne ya rantse har Mamma tayi min wannan kyautar abinda kawai nake bukata a gurin ki shine addua ki cigaba dayi min akan Allah ya cigaba da bani ikon rik'e amanarta.
Hannuna dake fuskata ta rike ta sumbata cikin kauna tace" Sumayya insha Allahu kina tare da nasara a rayuwarki ke kadai muka haifa ke muke gani muji dadi in Allah ya yarda adduarmu sai tayi tasiri a kanki." Murmushi nayi cikin jin dadi mayar da kayan cikin akwati hannu tasa tana taya ni.
Babana ma da shigo yaga abin arzikin dana samu yay ta murna yana farin ciki, yace idan anyi sallar isha'i sai na jagorance su suje suyi godiya, haka kuwa akayi muna idar da sallar muka tafi.....
Tare muka sameta da yaron nata yana kishingide a gefanta ita kuma tana zaune tana fuskantarsa da alama magana mai muhimanci sukeyi.....a nutse muka gaisa dasu, na kalleta da murmushi a tare dani nace"Ranki shi dade mahaifana sunyi farin ciki sosai da kyautar bajintar da kikayi min dalilin daya sa ma suke ce lallai sai na kawo su sunyi miki godiya bisa alkairin da kikayi min.
A nutse ta juya tana kallonsu fuskarta a sake tace"Haba Tambaya ai yarinyarku ta cancanci abinda yafi haka menena na zuwa godiya, ni wallahi Sumayya ta gama min komai data tsaya take kula da Babana babu abinda ba zan iya yi mata ba, saboda haka kada ku damu kanku akan duk wata kyauta da zanyiwa 'yarku domin ta cancani abinda yafi haka.
Cike da farin ciki sukayi kasa da kansu suna sake jaddada godiyarsu babana yace."Ranki ya dade kasa hakuri nayi nace lallai ta kawo mu mu mika godiyarmu a gurinki babu abinda zamu ce miki sai dai fatan gamawa da duniya lafiya, muna rokon ubangiji Allah ya tsare gabanki da bayanki Yarima Ali Allah ya kareshi daga sharrin abin'ki.'' Mamma Fulani cikin kulawa take amsawa, kafin ta bamu umarnin tafiya, kallon gefan da yake nayi, tun lokacin da muka shiga ya sunkuyar da kansa gashi har mun 'kare abinda ya kaimu mun mike bai dago kansa ba, hakika wannan 'bakin halin nasa na 'bata min rai! Babana ya durkusa kusa dashi da fadin"Ranka ya dade a tashi lafiya." Dukkaninmu bamuyi zaton zai amsa ba ballantana ya dago kansa, dalilin daya sa ma kenan lokacin daya dago nayi saurin sunkuyar da kaina ina mamaki! "A sauka lafiya nagode." Abinda yace kenan ya mayar da kansa kasa, Sai da mahaifana sukayi gaba sosai kana nabi bayansu, gaskiya naji dadi sosai dana ganshi rad'au dashi! sai na saki raina ina addua akan Allah ya kiyaye gaba.
****
Bayan sati biyu al'amura na tafiya sannu a hankali, yanzu ya daina ta'ba min jiki sai dai kullum cikin yi min masifa yake abu kadan idan na kuskure sai yayi min wulakancin da zanji tamkar na dora hannuwana a ka, haka dai nake ta daurewa ina kulawa dashi tare da saka idona akan dukkanin abinda zai cutarshi.....Moddibo yay tafiya shiyasa na dan samu nutsuwa, sai dai Gimbiya Lawisa dake yawan aikowa kirana idan naje zata bani lemo ko farfesu da girke girke tace lallai na bashi yaci jiki na rawa nake kar'ba kafin na fita sai na tabbatar mata da cewar zan cika aikinta, ina fitowa nake samun inda babu idanun mutane na haka rami na zuba a ciki.....haka mukeyi da ita