Showing 63001 words to 66000 words out of 150413 words

Chapter 22 - Kwarya Tabi Kwarya Book Complet by Binta Umar Abbale .txt

kiga yanda kudaje ke bin gurin ba.''
Da sauri na shiga binsu da kallo naga yanda kudaje ke binsu suna tashi sai kakari suke suna yunkuri idanunsu yayi jajawur! kuka na fashe dashi nace"Wallahi tallahi bani bace." Buba ya kawo min mari a fusace yace idan baki rufe bakin ki ba yanzu zaki sha duka anan gurin." Gum! nayi ina zazzare ido hade da kallonsu Haruna dake durkushe a gurun.......Jakadan maimartana ne ya iso gurin shida wasu fadawa suka saka su Haruna a mota suka nufi asibiti, hankalina ya tashi sosai na juya domin shiga gurinmu, Jakada yace."Kece Sumayya ko."? da sauri na daga kaina. Yace."Muje Maimartaba nasan ganinki." gabad'aya gwiwata tayi sanyi jin abinda yace bani da yanda zanyi dole nabi bayansa zuwa fadar Maimartaba nasan dai zai tuhume ni ne akan abinda ya faru dasu Haruna........




*Na kudi ne!*
Allah ya isa idan kika karanta! idan kina so ki biya ga yanda abin yake vip group #600 normal group #300 account.. 0542382124...Binta umar gtbank idan kati zaku turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number.
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
73&74
Da 'kyar na iya cin abinci na mik'e domin wanko hannuna dakin na dawo na same su suna magana shigowata yasa suka tsira min ido, a nutse nace"Zanje sashen Yarima koda abinda yake bukata nayi masa, cike da tausayi da kulawa sukace "To sai kin dawo." Fitowa nayi daga dakin nasa takalma na fita.


Koda na shiga falon shuru babu kowa da alama yana sama ko kuma be shigo ba, juyawa nayi da niyyar shiga kicin naji motsinsa, a hankali na juyo ina kallonsa yana sakkowa, kaina na sunkuyar har ya sauko ya zauna kan kujera gaishe shi nayi hade da fadin"Ko kana da bukatar wani abu.'' Kai ya girgiza kafin yace.''Bana bukatar komai kije ki huta." Tsira masa ido nayi......ganin inaso nayi magana yasa yay saurin katse ni da fadin"Sarkin zargi da rashin yarda nace kije ki huta naci abinci a gurin Mamma.




Sarkin zargi da rashin yarda maganar nayi ta nanatawa a cikin raina wato duk abinda nake nunawa a kansa bai dameshi ba tunga gashinan yayi min wata fassarar tunda nake kula dashi dayi masa hidima bai ta'ba yi min godiya ba ko kuma ya nuna min jin dadinsa kullum cikin fada min bakar magana yake, kaina na girgiza ba tare dana sake magana ba na juya da niyar fita daga dakin.




"Sumayya." a kasalance naji ya kira sunana, juyowa nayi muka hada ido dashi, yace."Idan hankali ya kwanta inaso muyi magana dake." ajiyar zuciya na sauke ina kallonsa ido da ido nace"Ko wace irin magana ce take bakin ka zaka iya fada min a yanzu ina sauraronka."


Girgiza kansa yayi yana lumshe ido yace.''Sai kin samu nutsuwa tukkuna dan na fahimci yanzu bakya cikin hayyacinki." Kaina na girgiza tare da fadin"Babu damuwa Allah yasa naji alkairi." Murmushi yay had'e da shafa sajensa yace ."Alkairi ne insha Allah.'' Ganin yana munafikin murmushi yasa na tsargu babu shakka har yanzu akwai mugun abu a cikin zuciyarsa, sallama nayi masa na kama hanya na fita ina mamakin al'amarin




Cikin kwanaki bakwai da rasuwar Isa al'amura sun d'anyi sauk'i masarautar ta samu nutsuwa kowa ya fawwalawa Allah ya cigaba da harkokinsa 'bangaran basawan masarautar kuwa kullum cikin shirya kitumurmura da ma'kar'kashiya sukeyi har yanzu sunqi saduda burinsa bai wuce ace sunga bayan Yarima Ali ba inda shi kuma nashi bangaran kullum zuciyarsa fes take a kansu baya ta'ba yarda da cewa sharrinsu da makircinsu zaiyi tasiri a kansa tunda ya riga ya kad'aita Allah yayi ya'kini da cewar babu abunda zai sameshi sai abinda Ya hukunta, ko a fuska bai ta'ba nunawa kowa ba duk bayan kwana biyu sai ya shiga kowane sashe na gidan sun gaisa inda su kuma suke nuna masa kauna a fili a bad'ini kuwa su kadai suka san irin 'kiyayyar da suke masa


Magajin Sarki ya turke Suwaiba ita dashi ya tsoratar da ita mutuka Suwaiba na kuka gami da nadamar abinda tayi ta sheda masa yanda al'amarin ya faru, wato Muddibo ne ya tursasata kan lallai sai tabi umarninsa tayi amfani da wani igur'bataccan ruwa mai wari daya kawo mata cikin wata jarka yace lallai tayi dahuwar abinci da ruwan kuma ta tabbatar Abinda ta dafa Yarima yaci, babu yanda ta iya haka ta dinga mu'ku-mu'ku da ruwan guban har dai ta yanke shawarar dafa doya dashi, bayan ta tsame doyar ne tana tsaka da soyawa a ranar da al'amarin zai faru ya shigo kicin din ya sallameta daga aiki ita kuma Sumayya ta dauka ta kaiwa su Haruna suka ciki.


Magajin Sarki beyi mamaki ba dan yaji ta ambaci sunan Muddibo dama tuntuni yake zargin akwai sa hannunsa a cikin faruwar al'marin, nasiha mai ratsa jiki yayi mata ya tsoratar da ita sannan ya nuna mata illar abinda ta aikata wato ta amince an hada baki da ita anyi kisan kai. Suwaiba kuka kawai take tana neman gafararsa, yace."Bani zaki nema gafara ba Allahn daya hallice ki shi zaki nema gafara ki tuba ki nemi gafararsa sai ya yafe miki."
Tace."Insha Allah na tuba nabi Allah da manzon Allah ba zan sake yarda wani ya tursasani ga aikata sa'bon Allah ba.'' Magajin sarki yaji dadi sosai da tuban ta, sallamarta yayi ta tafi tana addua akan Allah yasa kada ya fad'awa mahaifinsa harda saka hannunta a cikin faruwar al'amarin, bangaran Yarima kuwa baya tsammanin zai fad'awa kowa maganar domin fitar da ita yana nufin abubuwa da yawa barin ta shine yafi kwanciyar hankali.




******


Yau asabar duk ranakun weakened baya fita da wuri yana gida yana hutawa wani sa'in har na gama abinda nake na fita yana sama yana bacci abunsa abin mamaki yau dana shiga samun sa nayi a falo a zaune yana kallon kwallon kafa. gaishe shi nayi babu yabo babu fallasa ya amsa, kicin na nufa ya kira sunana


Tsayawa nayi ina kallonsa, kusa dashi ya nuna min. "Zo ki zauna yau ranar taki ce zamu tattauna maganar dana jima ina fada miki."




Gabana ne ya fadi ni sam na manta da wata magana, cike da rashin tsoro nace"Yallabai wace irin magana zamu tattauna wacce har sai nazo na zauna kusa da kai."




remot din hannunsa ya ajiye yace."Magana ce ta mussaman wacce take bukatar sirri."


Ajiyar zuciya na sauke nace"Ni da kaine kadai a dakin nan ina ganin ba sai na zauna kusa da kai ba babu wanda zaiji ko ya gani kawai ka fadi maganarka ."




'Kure ni yayi da ido yana kallona, nima nawa idon nasa masa dan gabadaya yanzu na daina jin tsoransa, "Kinga ni ba wani abu zanyi miki ba naga kina min kallon rashin yarda maganar da zanyi miki nafi bukatar na ganki a kusa dani shine dalilin daya sa nace kizo ki zauna?"


Shuru nayi ina naxarin maganarsa a sanyaye yace."Ki yarda dani da maganata ba zanyi miki komai ba." kallonsa nayi naga yana marairaicewa, ajiyar zuciya na sauke naje na zauna kusa dashi.


Ya kai minti biyar yana kallon k'asan gurin kafin ya dago kansa ya kalleni, kauda kaina nayi gefe, hannuwana ya ri'ke nayi saurin kallonsa! a sanyaye yace."Sorry.'' ajiyar zuciya na sauke nace"Ka sakar min hannuwa ka kuma fadi maganar dake bakinka."


Murmushi yayi yace."Yarinyar nan watarana idan kina bani umarni har mamaki kike bani gaskiya kina da karfin hali kina kuma burgeni wani lokacin kuma kina 'kuntata min"


Zum'bura bakina nayi na kauda kaina gefe hannuwana na cire daga nasa.
Hannu yasa ya juyo da fuskata naga yana min wani irin kallo wanda ya sani faduwar gaba, da sauri nace"Wai baka zaka fadi maganarka ba." Ba zato naji saukar hannunsa a le'bena yana shafawa.'' doke hannun nayi ido jawur nace"Ai dama nasan sai ka gwada halin ka." mikewa nayi da sauri yay gaggawar mayar dani na zauna
Fuska a hade yace."Ni kike dokewa hannu.'' hanci na hura ina ji tamkar na doki bakinsa dan haushi fitinannan mutum ne shi mai 'ketare iyakokin ubangiji.


Ajiyar zuciyarsa naji na kalleshi naga ya shiga hankalinsa sosai, kasa nayi da kaina ina jiran naji ta bakinsa




"Kin san abinda yasa nace kizo kusa dani muttauna." ? girgiza kaina nayi nace"Sai ka fada." Yace."Na dauki d'amarar auranki kamar yanda kika kwad'aita min zan aureki insha Allahu ina bukatar amincerki."




Kai tsaye nace"Yallabai ai ka makara me yasa tun lokacin da nayi maka maganar baka amsa ba a yanzu iyaye sun riga sun shiga cikin lamarina da Haruna an tsayar da maganar auranmu wata hudu masu zuwa maganar auranmu ma maimartaba ya san da ita




Wani irin shan kunu yayi yana kallona yace."Karya kikeyi kizo min da wannan maganar baku isa ba keda Harunan naki aure ni zan aureki shi yaje can ya nemi daidai dashi.'"


Cike da mamaki nake kallonsa nace"Haruna nice daidai dashi kamar yanda yake daidai dani kaine zakaje ka nemi daidai da kai tunda ka fada cewa ni ba tsaran auranka bace.''




Shuru yayi gumi na yanko masa. nace"Idan ka gama maganarka ni zanje nayi aikina." Ido jajawur ya dago yana kallona yace."Na fada miki fa baku isa ba wallahi sai an warware maganar auranki da Haruna ko kuma naga bayansa."


Gabana ya fad'i jin abinda yace nace."Ranka ya dad'e kana musulmi kake fad'ar wannan maganar zaka ga bayan Haruna me zakayi masa to."?
Ido yasa yana kallona nace"Ashe kaima zuciyarka irin ta 'yan uwanka ce gashinan kana mummunan lafazi akan wanda be maka komai ba."


Ajiyar zuciya ya sauke ya kama hannuwana duk biyun ya rike a raunane yace."Kada kiyi min wata fassara ta daban raina ne ya 'baci na fad'i wannan maganar Please Sumayya muyi maganar da zata amfane mu ni dake a yanda nake jin ki a zuciyata bana tsammanin zan iya bari Haruna ya aure ki."


Nace"Ranka ya dad'e Haruna shike sona tsakani da Allah kai kuma sha'awata kake zaka aureni domin ka kawar da sha'awarka shikkenan idan bukatarka ta biya sai ka sake ni, Haruna kuma zai aureni saboda yana sona tsakani da Allah badan wani abu na jikina ba kai kanka ka zauna kayi nazari da tunani akan al'amarin nan Yallabai kasowa kanka abinda zakasowa d'an uwanka yanzu babu wata sauran magana a tsakanina da kai tunda maganar aurena da Haruna ta shiga tsakani."


"Kin san dai Haruna bai isa ya had'a neman aure dani ba ko."? kallonsa nayi inaso nayi magana ya katseni a harzuqe yace.''Kije ki kira min Harunan naji ta bakinsa."


Cikin fad'uwar gaba nace"Bangane kaji ta bakinsa ba." Hannu ya d'aga min fuska a had'e yace."Kada ki sake harzuqani kije ki kira min shi nace."


Jikina ne yayi sanyi nace"Dan Allah ka bar wannan maganar ka fuskancin abinda ke gabanka ka auri daidai da kai nima na auri daidai dani."


"Sumayya." ya kira sunana kallonsa nayi, yace."Ba zan hakura dake ba ki rubuta wannan ki ajiye idan kin auri Haruna kin barni sai na hana ku jin dadin rayuwa gwara ku magance matsalarku keda shi Nafi karfin na nemi abu wanda yake kark'ashina ya had'a takara dani dole Haruna ya janye maganar auranki."




Nace"Ranka ya dad'e lafazan ka na nuna min cewar babu kyakkyawan nufi a cikin zuciyarka kada ka cutar da Haruna dan beyi maka laifin komai ba kuma ka daina gwada iko da mulki a kaina Allah ba'a nuna masa gadara idan Allah ya kaddara ni d'in ba matarka bace ya zakayi."?




Jajayen idanunsa ya zuba min yace."Bakya shakka kallon tsabar idona ki fada min magana ko." ? sunkuyar da kaina kasa nayi nace"Gaskiya d'aci gareta shiyasa kake gani kamar naci maka fuska."




Kwafa yayi yace."Dallah tashi ki bani guri kafin na da'uke fuskarki da mari."!! ganin yanda yake zabura yana huci! yasa nayi gaggawar tashi ina mamakin al'amarin.......kicin na nufa ba tare da naje aiken da yayi min ba.




Mikewa yay ya bude kofa ya fita, suna ganinsa suka taso daga inda suke zubewa sukayi a gabansa suna tambayarsa, babu walwala a tare dashi ya kalli Haruna da fadin"Ka shigo ina neman ka." Haruna yace."To ranka ya dade." Juyawa yayi ya koma ciki Haruna yabi bayansa.




Yana tsaye a tsakankanin kujeru Haruna ya same shi, Cike da ladabi yace."Ranka ya dade ina fata banyi laifi ba. wani irin kallo yayi masa kai kana ganin kallon kasan na kishi ne......Yace."Meye tsakaninka da yarinyar nan Sumayya."? Haruna yasha jinin jikinsa a sanyaye yace."Ranka ya dade itace matar da zan aura.'''


''Yaushe aka tsayar da ranar auran naku bani da labari."? Haruna ya sake kaskantar da kansa yace."Ranka ya dade ayi min afuwa wallahi na sha'afa shiyasa ban fada maka halin da ake ciki ba."




Ajiyar zuciya ya sauke ya zauna kan kujera yana kallonsa da wata iriyar murya yace."Inaso ka janye maganar auranka da Sumayya."!




Haruna gabansa ya buga da sauri ya dago kanshi yana kallonsa bakinsa sai rawa yake ''Ranka ya dade ban.......! Hannu ya daga masa ya hanashi karasa maganarsa, Haruna 'kasa yayi da kansa Gumi na tsiyayo masa.




"Kasan a 'karkashina kake ba zai yuwu ina neman abu kana nema ba dole ka janye maganar auranka da yarinyar nan." Wannan maganar da yayi yasa Haruna ya gane inda ya dosa.


Shuru yayi ya kasa magana yayin da gumi ya jikashi jagab ta yaya zai janye maganar auransa da Sumayya bayan ansa rana iyaye da abokanan arziki duk sun san halin da ake ciki, ta yaya zai iya cire tsananin so da kaunar da yake wa Sumayya a cikin ransa? babu shakka wannan babban al'amari ne a gare shi.




"Haruna kana jina ko."? da sauri yace." Eh Yallabai naji maganar ka nasan kai ba sa'ana bane ta kowane fanni! insha Allahu zanbi umarninka."


"Okey nagode sosai inaso ka shedawa iyayenka umarnina." Jiki a mace yace."Idan Allah ya yarda zan sheda musu." "okey kana iya tafiya." Yafada yana nuna masa hanya da hannu.


Yana juyowa muka had'a ido dashi, sai naga yayi wani irin murmushi kai kana ganinsa kasan na saduda ne tabbas bahaushe yayi gaskiya da yace ( bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane) ina shi ina had'a neman aure da Magajin sarki mai jiran gado tilas yanaji yana gani ya hakura da Sumayya ya bar masa, girgiza kansa yayi yana kallona nan na hango yanda idanunsa ya tara ruwan hawaye da sauri ya bude kofa ya fita.


Nima hawayen dake kokarin zubo min na mayar ina danne wani k'aton abu a mak'ogwarona, kallonsa nayi yana hard'e a kan kujera nace."Wallahi idan ka raba wannan soyayyar da k'arfin mulkin ka idan ka raba wannan k'aunar da karfin ikon ka to na tabbata Allah ba zai barka ba, kuma mutukar ka samu nasarar raba tsakanina da masoyina na gaskiya ka rubuta ka ajiye ko ka aureni ba zaka samu biyan bukatarka ba, saboda haka ka zauna kayi tunani da kyau akan maganata." Hanya na kama zan fita, da sauri na ganshi ya tari gabana zuba masa ido nayi ina kallonsa, Yace." Ni kuma nayi al'kawarin auranki ko kina so ko bakya so auranki bani na nema ba ke kika nema bayan kin kwad'aita min kuma daga baya kizo min da wata maganar banza! to na d'aura d'amarar auranki domin na kawar da sha'awata a kanki."


Cikin 'kunar zuciya na kalleshi magana nake so nayi tsabar bacin rai da takaici ya hana ni cewa komai ratse shi nayi zan wuce ya sake tare min hanya yana min wani irin kallo. girgiza kaina nayi nace "Bani hanya na wuce." Sake babbake hanyar yayi ya dogare hannusa a jikin bango....karfi nasa na doke hannun na ture shi! taga-taga yayi zai fadi baki ya bude yana kallona! tsaki mai karfi naja na bude kofa na fita. Murmushi yay yana mamakin k'arfin yarinyar har ta iya tureshi yana tsaye bai dauki mataki ba, kan kujera ya zauna yana tunanin ta yanda al'amarin zai yuwu.....










*Na kudi ne*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya ke kuma da kika futar da littafin keda Allah, idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 account.... 0542382124.....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min magana ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
71&72
Cikin kasala da mutuwar jiki yake tafiya tsirarun mutanan da suka rage a gurin suka dinga mika gaisuwarsu zuwa gareshi baya iya amsawa hannu kawai yake daga musu ya wuce.....Ya kusa isa kofar shi ya tuna da maganarsu da Maimartaba idan yake cewa idan ya fita ya bada umarnin fito da yaran, kai tsaye can ya nufa ya tarar da masu tsaron kofar suna shawagi a gurin, suna ganinsa suka zube gwiwa a kasa suke gaishe shi tare da sunkuyar da kansu kasa, a kasalance yace."Ku bude yaran nan su fito." Yana kare maganar ya juya da niyar barin gurin........."Yallabai babu lafiya." Da sauri ya juyo yana kallon mai maganar cikin rawar murya yace." 'Daya daga cikin yaran ce ta suma."
Gabansa ne ya fadi jin abinda bawan ya fada, da sauri ya dawo da baya, bawan ya matsa masa hanya ya shiga dakin, wayarsa ya kunna yana haskawa, ganinta a shema tamkar matacciya gabansa ya tsananta fad'uwa! da sauri ya tsuguna kusa da ita tare da umartar daya daga cikinsu ya kawo masa ruwa.
Ido ya tsirawa fuskarta yana mamakin tsayin lokacin data dauka a sume, hannunsa ya d'ora a kirjinta shuru babu alamun numfashi, ya sauke ajiyar zuciya tare dayin zaman durshan a gurin, kanta ya tallafo ya dora a cinyarsa, yana danna kirjinta a hankali a hankali, Bawan ne ya shigo da ruwa a hannunsa, ya kar'ba tare da umartarsa ya futa, bayan futar bawan sai ya shiga shafa mata ruwan a fuskarta da wuyanta yanayi yana kallon fuskarta, ya kai minti

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login