Showing 78001 words to 81000 words out of 150413 words

Chapter 27 - Kwarya Tabi Kwarya Book Complet by Binta Umar Abbale .txt

abinqi.'' Ya amsa da ameen yana goge gumin dake goshinsa.....Acp yay rubutu jikin takardar ya d'ago a nutse yace."Ranka ya dad'e afuwa shin ya akayi kasan abincin ka na dauke da guba mai karfi ka bawa hadimanka suka ci muna so muji yanda akayi haka ta faru."


Murmushi yayi ya girgiza kansa yace."Acp kasan Allah ban san abincin nan na dauke da mugun abu ba, yanda al'amarin ya faru shine........Na sauko cikin shiri domin zuwa gurin aiki na samu Amintacciyar hadimata tana aikace-aikace muka gaisa da juna nan take sheda min cewa ta kammala breakfast lokacin na duba time naga idan na tsaya break zan 'bata lokaci dalili kuwa shine akwai marasa lafiyan da zan duba sai nace ta bari kawai bana bukata, ta biyo ni da magana akan na daure naci abinci saboda yanayin aikina....still na sake duba agogon hannuna na kalleta naga ta nuna yanayi na damuwa, nace ba zan tsaya ba amma ta had'a abincin ta bayar a kawo min ofis. da wannan na fita na barta a sashen nawa. ina zuwa ofis na samu coffee nasha na cigaba da gudanar da aikina misalin sha biyu shaura na rana sai ga Hadimi na Haruna marigayi ya shigo ofis d'ina da kayan abinci a hannunsa, muka gaisa yake sheda min abunda yake tafe dashi, time na duba naga idan naci abinci a lokacin zan samu matsala kai tsaye nace ya koma dashi bana bukata idan kuma yana so to ya samu wani ya taya shi ci." daga wannan magana sai na sallameshi na cigaba da aikina. to daf da zan tashi d'aya daga cikin masu kula da hospital din yaga gawarwarkin wad'annan bayin Allah a can gurin shukoki a guje yazo yana sheda mana abinda ke faruwa, Acp wannan shine cikakken bayanin da zan iya yi maka dangane da faruwar wannan al'amari.


Acp Mahmud girigza kanshi yay yayi rubuce rubuce a jikin takardar kafin ya d'ago kansa yana kallonsa Yace.'' Ranka ya d'ade tilas mu aika yanzu yanzu azo da wannan yarinyar domin alamu na nuna mana cewa akwai sa hannunta a cikin faruwar wannan al'amari."
Kallonsa yayi yana girgiza kansa yace."Acp ba wai zanyi maka katsalandan a cikin aikin ba amma kasan Allah yarinyar nan ta gari ce, ni zan bada shaida a kanta ba zata ta'ba yarda a had'a baki da ita a kashe ni ba, ni nasan ta ciki da waje nasan wacece ita Sumayya ba zata iya kashe kishayi ba ballanatana mutum mai rai."


Acp yayi murmushi yana kallonsa a nutse yace."Ranka ya dade kai da kanka kace itace ta girka abincin nan to amma me yasa kake 'kokarin kare ta."? Girgiza kansa yayi yay shuru yana kallon kasan gurun....Acp yace."Kayi hakuri ba zamu yi mata komai ba kawai zamu tsoratar da ita ta fad'a mana gaskiyar lamari."


Ajiyar zuciya ya sauke yace."Okey to babu damuwa." Acp ya dauki waya ya kira daya daga cikin ma'aikata, ya shigo sanye da kayan aiki qamewa yayi yana miqa gaisuwarsa, Acp yace."Kuje da Merry gidan Sarki zaku dauko wannan yarinyar Sumayya zamuyi binkice akanta." qamewa yayi da fadin"Okey sir.'' da sauri ya juya ya fita...........










*Na kudi ne!*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya, keda kika futa da littafin keda Allah! idan kina so ki biya ga yanda abin yake....Vip group #600 normal group #300 account... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
82
"Dan Allah kar kaqara." nafada ina sake janye jikina. Lumshe idonsa yayi ya bude a take na sunkuyar da kaina gabana na wani irin faduwa ganin yanda lokaci guda idanunsa suka jirkice."
"Idan bakya so na ta'ba ki to tashi muje mu kwanta." Hannuwana nasa na rufe kirjina hawaye na zubo min nace"Nifa ba zan yarda na kwanta daki d'aya da kai ba tunda dai kai ba muharrami na bane." Tsira min ido yayi babu yabo babu fallasa yace."Nace dake babu abinda zan miki kin tsaya taurin kai ko tom zaki janyo na kwanta a kanki yanzu."


Kallonsa nayi ina girgiza kaina hawaye na sake zubo min, ni dai ban san da wane nataccan mutum Allah ya had'ani ba."




''Ki daina zubar min hawaye bakya gajiya da kuka Sumayya kina dani bai kamata ki dinga zubar da hawaye ba."


Cikin zuciyata nace "Zubar da hawaye dole ne tunda Allah yasa ka sauka kasar nan nake kuka har yanzu na kasa samun sassauci."




A zahiri kuwa shuru nayi ina kallonsa tare da kare kirjina da hannuwana, murmushi yay ya kawo hannu zai ta'ba ni zabura nayi da sauri na matsa ina girgixa masa kaina.


Dariya yasa yana kallona, na dinga watsa masa harara hawaye na zubo min, matsowa ya sakeyi sai kawai na mike da sauri zan bar gurin.


'kuguna ya ri'ko kawai ya janyo ni na zauna a cinyarsa, kansa ya d'ora a kafadata, naji ya sauke zazzafar ajiyar zuciya, hucin numfashinsa ne yake nema ya kassara ni! kafad'ata na gotar ya sake mayar da kansa yana shanshana wuya na, kafin nayi wani yun'kuri naji yana sumbatar wuyana sai goga fuskarsa yake a gurin, cikin tashin hankali nace"Dan Allah ka bari na yarda zan bika dakin."


Shuru yayi yana cigaba da abinda yake, gabad'aya jikina ya mutu kasala duk ta baibayeni tuntuni hawaye ya daina fita tsoro da fargaba duk sun dabaibaye ni.




Hannuwansa yake kokarin 'dorawa a kirjina na rike katamau! muryana na rawa nace"Ka bari."!!! Girgiza kansa yayi a kasalance yace."Ki bari na ragewa kaina damuwa." cikin takaici nace"Ranka ya dade wani lokacin kaine kake janyowa ina maka abinda be dace ba yanzu dan Allah meye amfanin wannan iskancin da kake min."! a kufule nake maganar.


girgiza kansa yayi saitin kunnena yace."Ni ba d'an iska bane.'' fuzgewa nayi na mike ina kallonsa dik ya koma wata kala nace"To idan ba d'an iska bane menene kawai ka matseni a jikinka kana wani abu."


Hannu ya miko min da fadin "Zo my love ina cikin mayen sonki." Naji kamar na kwad'a masa mari! girgiza kaina nayi nace"Ba sona kake ba dan inda kana sona ba zakayi kokarin yin wani abu dani ba har sai na zama mallakinka." Hannu ya miko zai rike nawa na kauce! ina watsa masa harara, mikewa yayi tsaye, abinda nagani yasa ni saurin kautar da kaina, gabansa ya mi'ke sosai har ya nuna ta gaban rigarsa, gabana na faduwa nayi yun'kurin barin gurin, hannuna ya rike ya juyo da fuskata yana kallona, na dinga kauda kaina dan bana so naga abinda yake firgitani!




"Sumayya." sunana ya kira can cikin ma'koshi!! kasa amsawa nayi gabana sai faduwa yake yace."Kinga abinda kika janyo min ko."? k'in kallonsa nayi kawai naji ya dauki hannuna ya d'ora a gurin, ihu! mai karfi na kurma! na tunkud'eshi ya fadi saman kujera! fita nayi daga tsakanin kujerun na dinga nuna shi da hannu ina girgiza kaina, ganin ya yun'kura zai mike yasa a guje na bude kofar kicin na shiga na kulle ina haki! da kiran sunan Allah!


Yarima a jigace! ya haura sama ya zube kan bed yana jan numfashi, hannu ya dora saman joystick d'inshi tana nan a mike tana harbawa, a raunane yace."Kaico! kaicon ki da kai kanki inda bai dace ba! kaicon ki da sha'awar abinda ke karkashin ki!!! jijjigata yayi yaji kamar ya murd'eta ya huta da takaici! mikewa yayi zaune yasa hannu ya dafe goshinsa zufa ce kawai take keto masa, idanu yasa kan agogon dake kan bedside Uku shaura na dare, mikewa yayi yana rangaji ya shiga toilet ruwan sanyi ya dinga kuzawa kansa yana kiran sunan Allah a zuciyarsa.




Jingina nayi jikin kofar na dinga wani irin kuka abubuwa biyu sun dame ni Mutuwar Haruna ta tsaya min a rai! sai kuma masifar wannan taqadirin da Allah ya jarrabeni dashi hakika da ina da inda zanje bayan masarautar nan to dana gudu na huta da masifar wannan bawan Allah.




Zamewa nayi na zauna kasan ties had'a kaina nayi da gwiwa ina takure jikina sosai nake addua a zuciyata akan Allah ya kawo min mafita.




Tsakanin Magajin sarki da Sumayya babu wanda ya rintsa yanda suka ga rana haka suka dare!




Asubah nayi na bude kicin din na fito, lokacin yana kokarin saukowa ko kallonsa banyi ba na karasa bakin kofa, hannu nasa naji ta a rufe gefe na matsa sakamakon karasowarsa gurin
Daf dani ya tsaya yana sanye da jallabiya ash color sai kamshin turare yake, na dauka zai min magana sai naga shima ya dauke kansa, kofar ya bude ya fita, da sauri nabi bayansa.........Hadimansa na ganin fitowarsa suka karaso gurin ganina yasa sukayi sak!! yace."Sumayya ta kwana a sashena dalili jiya ni da ita bamu shigo da wuri ba sai bayan sha biyu na dare wannan dalilin yasa na hanata tafiya sashensu." yafadi hakane domin kada su zargi wani abu.


Sunkuyar da kansu sukayi suna masa barka da fitowa, gaba yayi ba tare daya amsa musu ba da sauri suka rufa masa baya domin shiga massalaci.




Ina kokarin shiga gurin mu babana ya fito daure da alwala, ganina yasa ya zube a gurin yana godewa Allah! mikewa yayi ya rike hannuna cikin murna yace."Sumayya ina fata ba suyi miki komai ba."? Nace"Ba suyi min komai ba baba amma dai basu gama binkicensu ba." A sanyaye yace."Ni da mahaifiyar ki bamu rintsa ba saboda fargaba kwana mukayi muna addua akan Allah ubangiji ya kubutar dake." Hawaye na share ina jin tausayinsu na ratsa ni nace."Baba insha Allahu Gaskiya tana tare da mai gaskiya in Allah ya yarda Allah zai wanke ni." ya amsa da ameeen da fadin" Ki shiga ciki mahaifiyarki ta ganki ko hankalinta ya kwanta." Da sauri nace"To baba." Lawi sai da yaga shigewarta cikin gidan sannan ya nufi massalaci domin gabatar da sallar asubahi.




Tambaya rungume ni tayi ta dinga kuka da kyar na rarrasheta tayi shuru ta dinga duba jikina wai ko sun dake ni. nace"Tambaya ki kwantar da hankalin ki babu abunda akeyi min sai tambayoyi."


A jiyar zuciya ta sauke tace."Sumayya jiya na shiga tashin hankali da damuwa sakamakon zuwan 'yan sanda da tafiyarki na dinga addua ina rokon Allah akan kada ya basu dama su cutar dake ina jin tsoron kada wani mara imanin ya keta miki alfarmarki."




Girgiza kaina nayi nace"Tambaya Allah ya kare ni kuma zai cigaba da bani kariya albarkacin adduarku insha Allahu wani mummunan abu ba zai faru dani ba."
Zazzafar ajiyar zuciya ta sauke ta cigaba da kallona kai kana ganinta zaka san tana cikin tashin hankali mai tsanani, sai da na tabbatar hankalinta ya kwanta tukkuna naje na dauro alwala, na dawo kuryar dakin na shiga nasa hijabi kana na tsaya kan dadduma a nutse na tayar da sallah.


Ganinsa a massalacin yasa jikin Ciroma da mu'karrabansa yayi sanyi ikon Allah yaushe ya dawo gidan? kai amma ba suji dadin ganinsa ba. Maimartaba da Waziri kuwa babu wanda ya kaisu farin cikin ganinsa ko bayan da'aka idar da sallar Liman ya dade yana addua akan abubuwan dake faruwa a masarautar Liman yayi zafafan adduoi akan Allah ya tuni asirin masu aikata mugun 'kulli a masaraura, Ciroma da galadima jikinsu ne yayi sanyi ganin yanda Liman ya dage yana addua jama'a na amsawa da ameeen ya Allah! duk sai suka tsargi kansu da kansu suna ganin kamar asirinsu na daf da tonowa.......Muddibo kuwa dama ana idarwa ba tare da kowa ya ankara ba ya silale daga massalacin, can sashen Uwargida ya nufa ya sheda mata abinda ke faruwa, Uwargida Huwaila ranta yayi mugun b'aci! jin cewa ai Yarima ya dawo gida su duk a tunaninsu hukuma zata ri'keshi akan abinda ya faru sai kuma suka ga sa'banin haka, jiki a sanyaye ta koma ta zauna kan kujera tana tunanin mafita.




Tare suka fito da Shatima daga massalaci, kai tsaye sashen fulani suka nufa suna tafiya suna tattauna al'amarin, karo suka ci da Muddibo ya fito daga sashen uwargida ganinsu a tare yasa gabansa faduwa amma da yake 'kwaro ne nan da nan ya dake! ya karasa inda suke a nutse ya basu hannu suka gaisa, yace."Yanzu nan nake tunanin zuwa sashen ka ashe ka dawo gida."? Yarima yace."Eh Allah ya takaita na dawo jiya misalin sha biyu na dare." Cikin alhini yace."To Ubangiji Allah ya kiyaye a gaba amma yana da kyau kasa ido sosai a sashen ka abubuwan dake faruwa da kai sunyi yawa." Yace."Insha Allah yau din nan zan zauna dasu saboda jiya bayan dawowata na samu abun hannun wani daga cikinsu hakan ya sake tabbatar min da cewa akwai sa hannunsu a cikin al'amarin."
Muddibo cikin faduwar gaba yace."Ka samu sheda kenan."? Yace."Kwarai kuwa." Muddibo girgiza kansa yayi yace."To babu damuwa Muje mu gaisa da Mamma sai mu zauna dasu din." tare suka shiga falon, tana zaune kan dadduma da carbi a hannunta, ganin gudan jininta lafiya lau yasa taji wani sanyi ya sauka a zuciyarta, lallai addua bata faduwa kasa banza, a nutse suka zauna gabanta suna gaisheta, ta dinga amasawa tana shafa kansu, tace''Ina rokon Allah yayi muku albarka ya kareku daga dukkanin sharrin abinqi dukkanin mai nufin ku da sharri ina rokon Allah ya mayar dashi kansa, babana hakika naji dadin ganinka cikin nutsuwa ina rokon Allah ya kiyaye gaba su kuma wad'annan bayin Allah da suka rigamu gidan gaskiya ina rokon Allah ya jikansu ya gafarta musu."
Suka amsa da ameeen suma ameeen."


Koda suka fito daga sashen mamma kai tsaye Sashen Waziri suka nufa, iyalin Waziri ganinsa lafiya lau yasa su farin ciki suka dinga yi masa adduar kariya daga dukkanin abinqi! lafiya lau suka fito daga sashen suka nufi na Galadima, babu yabo babu fallasa suka gaisa da juna har suka fito babu wanda yayi masa jajen abinda ya faru ballantana ya samu kyakkyawar addua, sosai al'amarin ya bashi mamaki! Shatima ma yaji takaicin abinda iyayensa sukayi 'karara suke nuna hassadarsu abin da iyayensa da sauran 'yan uwansa keyi sam bayayi masa dadi, hakuri ya shiga bashi, Magajin sarki ya dakatar dashi da fad'in "Kada ya sake bashi hakuri akan abinda akayi masa shi bai dauki abin da zafi ba yana ganin duk abinda sukayi a kansa daidai ne! Shatima ganin ransa ya baci yasa ya bar maganar, Suna daf da shiga sashin Ciroma Mudibbo yace." Su shiga kawai zai dauko wayoyinsa a gurinsa, ba tare da sunce wani abuba sukayi gaba, shi kuma kamar gaske ya nufi gurinsa, tsayawa yayi na minti biyar, ya leko kansa ganin sun 'bace daga gurin yasa da sauri ya fito, kai tsaye 'bangaran bayi ya nufa.




Babu yabo babu fallasa suka gaisa da iyalin Ciroma dukkaninsu suka cika falon kowa na fadin albarkacin bakinsa akan abunda ke faruwa, shi dai jinsu kawai yake dan ya kasa cewa komai saboda hayaniyar da tayi yawa a falon sai zagin Sumayya suke suna cewa ita za'a daure tunda itace ta girka abincin dole a tsaurara binkice akanta ta fadi wanda ya bata gubar.....Gimbiya Lawisa ta zage sai cin mutuncin Sumayya takeyi, 'yan uwanta suna taya ta, ga mahaifiyarta a zaune ta kasa tsawatar musu, takaici yasa ya mike Shatima ya mike sukayi musu sallama suka fito, rai a 'bace ya kalli Shatima yace." Gabad'aya naji na tsani Lawisa wallahi bata da tarbiya ko kadan." Yace."Kasan hausawa nacewa Tarbiya daga gida take farawa Hajiya Karima sam bata da tsawatarwa shiyasa 'ya'yanta suka lalace." Yace."Allah ya kyauta hakikanin gaskiya ina fargabar auran Lawisa ta haifi min lalatattun 'ya'ya." Yace."Haba ai ba 'anan take ba kaifa tsayayyan namiji ne kai zaka tsaya akan iyalinka sosai na tabbata zaka iya sanja mata hali idan kukayi aure." Girgiza kansa yayi yace."Hakika idan ta sake tazo min da mummunar d'abia to zata sha wuya a gurina dan na tsani mace mara nutsuwa wallahi." Shatima yace."Gaskiya mace mara kintsi bata da dad'in sha'ani kamar yanda na fad'a maka da farko hakane idan kukayi aure zaka iya canzata mutukar tana kaunar zama dakai dole tabi dokokinka." shuru yayi be sake magana ba har suka isa sashen nasa,




kafin su shiga ciki ya kira Mika'il yace dashi gabad'ayansu suzo yana san ganinsu.......Suna zama Muddibo ya shigo hannunsa rike da wayoyinsa kusa da Shatima ya zauna yana duba 'karamar wayarsa Shatima kallonsa kawai yake sam be yarda dashi ba, tuntuni yake zarginsa kawai dai yayi shuru ne yana kallonsa kuma yana rokon Allah ya tona masa asiri.......Su shida suka shigo suka samu guri guda suka jeru gabad'aya sunkunyar da kansu sukayi kasa suna jiran suji kiran da ake musu.








*Na kudi ne!*
Kada ki karanta min littafi sai kin biya keda kika futa da book din keda Allah idan kina so ki biya ga yanda abin yake Vip group #600 normal group #300...account... 0542382124....Binta umar gtbabk....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:27 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(kainuwa dashan Allah✊�)
81
"Idan ba shine yayi sanadiyar mutuwar Haruna ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login