Showing 9001 words to 12000 words out of 118783 words
maqoshin ta Jameela ta amsa ta, tana tafiya Babawo ya maida kan shi inda ya fito.
Sai da ya kai wajen minti goma sannan ya fito suna ta dariyar jin daɗi, kudi ya debo canji-canji kimanin dubu biyu, ta tsaya tana kallon shi a ranta tace,
'matsiyacin banza kawai kullum sai dai ya zo ya ji daɗi dani amma ba wani kudin arziqi da yake bani'
A zahiri kuwa sai ta kyab'e baki ta ce,
"Nawa ne nan kuma? Kasan na tsani canji-canjin nan ko?"
"Sorry babyna dubu biyu ne fa shine kike bata rai? canjin ne kawai amma ai yafi na kullum yawa yau ko?"
Ɗan sake fuska tayi ta zaci yauma dubun ce, ahhh lallai dole ne ta d'agawa Mamalo kai dan a da kullum ya zo dubu ce ko dubu da dari biyar, to yau gashi an samu ci gaba.
Haske ne ya bayyana ya haske masu idanu daga ita har Babawon,daga baya hasken ya tsaya akan Jameela, mahaifin ta baya son ya daga murya aji yana magana da d'iyar ta shi,dan haka sai ya dinga haska ta yana kada fitilar.
Cike da zumb'ura baki ta tashi tana doka qafa, Babawo kuwa da sauri ya bar wajen yana kare fuskar shi.
Kewaye baban ta tayi ta shige gidan nasu wanda Soron cike yake da yaran gidan samari, suna ta bacci, haskawa yayi ko zai ga Bukar a wajen kwanciyar shi amma ba Bukar ba labarin shi, kad'a kai yayi yana nemawa yaran shi shiriya a wajen Allah, baya taba zagin su ko tsine masu, shi dai fatan shi su shiryu.
Har ya sa qafa zai shige dakin su, yaji hayaniya, ana fad'in,
"Dalla kar ka fad'o min a ka ni, kayi can ga shimfidar ka can Ramai ta yi maka,"
Bukar kuwa sai hayaniya yake yi irin na 'yan shaye-shaye, dan kuwa ba mai gane me yake faɗa, fari tasss aka haife shi kamar Jameela, amma saboda shaye-shaye ya koma baqi, musamman bakin shi da hannayen shi.
Dika-dika shekarar Bukar sha Uku amma ba irin iskanci da dabar su basu saka shi yi, dan yana qarami da shi suke amfani ya je ya masu 'yan qananun sata,sannan ya yi masu aiken siyan kayan maye, daga nan har ya fara sha shima.
Kad'a kai Baban su jameela yayi ya qarasa shigewa d'akin su dan kuwa ba zai je kallon takaici ba, tinda ya dawo gida to Alhamdu lilLAAH.
Ya na shiga ya doki qafar ta ta tashi tana gantsaro girji tare da yin hamma,
"Malam lafiya ka ke tashi na da wannan tsohon daren? Kasan nayi aiki na gaji fa gashi gobe ma zan ci gaba da aiki kamar kullum, in ban bacci da wuri ba kasan bana samun jin daɗin yin aiki na,"
"Yi hakuri dan tashi ki duban lokaci a agogon nan,"
Wani haushi ne ya kama ta, agogon ne bai iya ba ko me?
Cikin fushi ta kalla tace.
"Qarfe sha daya da rabi na dare mana baka iya agogon bane ko me?"
"Yauwaaa alhamdulillah kema kin faɗa da tsohon daren nan, sannan kin ce qarshe 11 na dare,to a tsohon daren sai yanzu yaran ki ke dawowa daga waje daga macen har namijin, ya kamata kenan? Haba Ramai, yarannan fa amana ce Allah ya bamu a hannun mu fa, Allah ya aminta damu fa kenan tunda har ya azurta mu da yara dan mu kula da su mu basu tarbiyya mai kyau, amma shine ke kike sakaci da basu tarbiyyar,ni dai Allah ya sani ina yin iya bakin qoqari na amma ba ki bani had'in kai, kin kyauta min kenan tsakani da Allah,"
Tin da ya fara maganar ta ji farkon amma qarshen bata san me yake faɗa ba, dan kuwa baccin ta ta koma a zaunen, dan indai ta shi ne kar suyi bacci ayi ta magana akan yaran wanda ita kuwa bata ga abinda suke yi mara kyau ba,ba zata iya matsawa yaran ta ba ta hana su sakewa sammm.
Malam Jameel yaji haushi kuwa matuqa amma haka ya danne, ya bi gadon nasu tare da yin addu'ar bacci ya kwanta sannan ya tofa mata itama, dan bai taba gani tayi ba shi kuma baya gajiya wajen yi mata kafin ya kwanta, cikin dakiya da jure ɓacin ran da yake ji ya ce wa Jameelah,
"Ki rama sallolin da ake bin ki kan ki kwanta dan bana jin ko azahar kin yi, in Allah ya so ya amsa, in bai so ba ya barki da abun ki, Allah ya shirye ku, kuma kiyi addu'ar bacci kafin ki kwanta,"
Cike da zumbura baki ta amsa shi.Fita tayi tayo alwala ta yi zaman ta a kan sallaya tana ta tinanin abin da ya faru ɗazu da Babawo yazo sai murmushi ta ke ta zabgawa tanashafo dik wani sashe na jikin ta daya taba.
'Gaskiya Babawo ya iya soyayya sai kace a indiyan fim'
Sai da ta dad'e a wajen sannan ta miqe ta ninke abin sallan, ta sauya kayan jikin ta zuwa na baccin data siyo a gwanjo, dan ita tana son harkar hutu, ta yi kwanciyar ta a dan bargon da take shimfidawa kalar pink, a rayuwar ta tana son ya zamana tana da d'akin ta na kan ta, ta yi masa ado irin yanda take gani a wayar Babawo a films.
Tsaki ta doka ta sake gyara filon ta mai mugun tauri sannan ta juya wa dakin baya, nan da nan kuwa bacci ya dauke ta......
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 5:
Da sauri Jameelah ta ja Umaimah baya cike da in-ina take magana tare da yin nuni da yatsan hannun ta tana Kyafkyafta ido tace,
"Wwaaa... nnee... ne wan can???"
Murmushi Umaimah tayi mai kyau kafin ta bata amsa da cewa,
"Yah Umar kenan dama ina son na nuna masa babbar qawa ta, muje na gabatar dake wajen shi,"
Cikin sauri Jameelah ta hau goge fuskar ta da bayan hijab dinta ta gyara sosai dik Umaimah na kallon ta bata ce komai ba sai murmushi da take yi,cikin wani sabon ladabi daya matuqar bawa Umaimah mamaki suka jera suna tafiya.
"Me yasa kuka koma ne? Ku fa ake jira"
"Mum wai...."
"Na yi fitsari ne,"
Jameelah ta yi saurin katse Umaimah dan kar ta faɗi gaskiyar abinda ya faru,kallon Jameela Umaimah ta yi da sauri itama dan kuwa a gidan nan ba ta tab'a tina sanda taji wani ya yi qarya ba, waje suka samu a saman jerin kujerun dinning table ɗin nasu, kan Jameela a qasa ta sake gaida iyayen Umaimah, cikin jin daɗin tarbiyyar da take da ita suka amsa, Umar sai zabgawa qanwarshi murmushi yake yi, tare da langab'ar da kai gefe irin na masu shagwab'a Umar ya ce,
"Lallai ma Umynaa wato kin yi sabuwar qawa ne ashe shi yasa ki ka dai na so na ko? Ta kwace min ke,"
Sunkuyar da kai Jameela tayi tare da lumshe kyawawan idon ta dan jin daɗin muryar Umar,cikin ran ta ta ayyana,
'Wayyooo Allah na yau gani ga jarumin maza kenan,Allah kasa sanadin haduwa da wannan gwarzon ne ya kawo ni gidannan'
Ɗan taba ta Umaimah tayi dan kwata-kwata bama ta san me ake yi ba ta tafi duniyar tinani.
"Nanna'am"
"Yah Umr na yi miki magana,"
Kallon shi tayi ta sunkuyar da kai qasa, wani iri yaji azuciyar shi game da ita dan kuwa ta yi matuqar yi masa kyau ba kaɗan ba, a zuciyar shi ya furta,
'Masha'Allah'
Shine abinda Umar yace, a zahiri kuma ya sake maimaita mata tambayar shi inda ya ce mata,
"Cewa nayi meye sunan ki,Umaimah na son riga ki sanar dani sunan naki,"
"Jameelaahhh"
Cikin salo mai ɗaukan hankali tayi magnar, a zahiri ta nuna kamar bata san ma ta yi magana dan jan ra'ayinsa ba.
"Wooow masha Allah Jameelaah nice name, u deserve to be called Jameelaah, naji tace ajin ku daya ko? ashe kema hafiza ce kamar Umynaa....naji daɗin haɗuwa da babbar qawar Umynaa Allah ya sanya albarka a qawancen ku,"
"Ameen"
Itace kalmar da kowa ya fada a wajen, bismilla suka yi kowa ya fara cin abinci, Jameelaa a ran ta sai surutu take yi cikin mita take ayyana.
'Matsalar masu kudi kenan a tashi a hada ku cin abinci a babban teburi tsabar rowa, in ba rowa ba dan kar naci na qoshi da ba sai a bamu mu je can d'akin mu ci hankali kwance ba? ji kaji ma malam yanzu a banza zan barsu'
Ɗan juya ido tayi ta d'ibi shinkafa kadan a spoon ta kai bakin ta, tana taunawa a hankali, kowa a tinanin shi tsabar kamun kai ne ya sa take yin hakan,ganin haka sai Mum ta kiran mai aikin gidan ta ce,
"Kin ga haɗa masu abinci ki kai masu d'akin Umaimah su ci a can, baquwar tamu ta kasa sakewa ta ci abinci da mu"
'Alhamdu lilLAAH kaiii babar su Umaimah na da hangen nesa,yanzu ba sai na ci kaji acan na gyatse abuna ba? habaa da an wani hadani da wannan mai kalar mutanen boyen ta ya abinci zai shigen'
Bayan an kammala haɗa masu abincin an kai masu Umaimah ta kama hannun ta akan su shiga daki su ci, cikin jin kunya ta miqe basu qarasa shiga ba taji Umar na cewa,
"Gaskiya na ji daɗin ganin qawar Umynaa, tana da hankali da nutsuwa ga kuma kunya, "
"Gaskiya nima na yaba da hankalin yarinyar, ana fadin yaran unguwar basu da tarbiyya gaskiya naga sab'anin hakan akan ta, yarinya kintsattsiya haka? Lallai iyayen ta sun bata kykkyawar tarbiyya,"
"Kwarai kuwa, Allah ya musu albarka to,"
"Ameen dai"
Ai wato suna shiga d'akin Jameela ta yi arba da abincin nan ga lemuka kala biyu kowa da nashi ga nama ga shinkafa da miya da salad, wayyooo ji ta yi kamar bata taba cin kowanne a cikin su ba, zama ta yi ta aje hijabin ta a gefe ta duma hannu ta hau yagar naman tana ci tana santi, tasss ta tashi da abincin bayan Umaimah tace ta qoshi, wata gyatsa ta sake ta hau yi wa Umaimah surutu,
"A gaskiya kuna jin daɗin ku Umaimah, kullum wai haka kuke cin abinci mai daɗi a gidan nan?"
Murmushi kawai Umaimah tayi wa Jameelah,kafin ta yi magana kawai sai Jameela ta fara share hawaye cikin kuka ta ce,
"Allah sarki Ramai na da Babana, na zauna na cika cikina da mai daɗi irin wannan, ko su me suka samu suka ci da rana? Wataqila abincin siyarwar da Ramai ke dan dorawa dan siyarwa shi zasu ci yau, Allah kenan mai yarda ya so, mu muna nema ku kuma kun gama samu,"
Tausayin ta ne mai qarfin gaske ya kama Umaimah da sauri ta rungume ta tana lallashin ta, tare da yi mata alqawarin zata ɗebar mata abincin da taci ta kaiwa iyayen ta,
"In aka gani a gidan ku fa ba za a maki faɗa ba? ai sai su ce na zama makwadaiciya Umaimah,basshi kawai kin san soyayyar dake tsakani na da su ne ya sa na ji sha'awar na gan mu muna ci tare, amma ban fada maki dan ki debar min ba,"
"Na sani kar ki damu, inshaa Allah sai sunci nima hankali na zai kwanta, tashi muje parlour,"
"To ai ni tafiya zan yi ma, da kin barshi kawai,"
A hanyar su ta tafiya parlour suka rabu, Jameelah ta yi parlour Umaimah ta yi hanyar kitchen sanye da zumbulelen hijabi......
*A yi hakuri da wannan na yi busy ne thank you mutanen kwarai da hakuri da ni.*
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 7:
Sosa kai tayi sannan tace,
"Baba na jima ina so in gyara dik wani halayen da nake yi marasa kyau malamin mu ya yi mana wa'azin daya shigi jikina kuma ya tsoratar dani, sannan Allah ya amsa addu'ar ka akan nema mana shiriya da ka ke yi a kullum ba ka gajiyawa,ana haka shine na nemi izinin Ramai na je gidan wata qawata dan muyi karatun qur'ani ina so na gyara hadda ta,dayake ita qawar tawa tana da hadda sosai dan kuwa ita ke yin na ɗaya cikin mu arba'in da wani abu a ajin mu, muna zuwa sai na ga ashe masu kuɗi ne, shine mukai karatu da zan tafi iyayen ta da ita kan ta suka haɗa min abin arziqi, na qi Karb'a maman ta tace ai dik abokiyar d'iyar ta d'iyar ta ce, shine na amsa yayan ta ya dawo dani gida, kuma maman ta ta qara mana k'warin guiwar yin karatu tare"
Nazari sosai Baban nata yayi ma maganar ta, amma sam bai gano qarya a ciki ba, dan haka fara'a ta bayyana a kyakkyawar fuskar dattijon har ya samu kan shi da fad'in,
"Alhamdu lilLAAH, na gode Allah dana ga wannan rana,Allah ya shirya min dan uwan ki shima ya gyara rayuwar daya tsindima kan shi a ciki yaro qarami amma haka za ki ga yana layi a titi dan lalacewa, Allah ya dawwamar dake cikin farin ciki da kuma shiriya,"
"Ameeen Babana,"
A haka suka kashe bakin shi, ta dage ta dinga yin duk wani abu da zai tabbatar masa da cewa ta shiryu da gaske kamar yanda ta ce ɗin, shi kuwa baba haka ya saka mata ido dan ya ga ko wani makircin suke qullawa amma har dare bai ga ta je zance ba, dik kuwa da naci irin na Babawo da ya zo har leqawa tsakar gidan ya yi ya hau kiran ta, tana nan rungume da qur'ani ta na jin shi amma ta qi fita.
Washegari da assuba bayan tayi sallahta sai ta d'auki qur'anin ta ta hau karatunta ta nata muraji'a, Baba kam daɗi kamar ya d'aga shi sama haka ya dinga sakin murmushi.
Bayan ta gama karatun ta ta shirya dan zuwa wanka sai ta saka hijab daya rufe mata jiki gaba ɗaya taje tayi yi wankan ta ta dawo tayi shirin zuwa makaranta,a hanya suka hadu da Mamalo,cikin ɗauke kai irin na masu kishin qawancen nan Mamalo ta ce,
"Wai ina ki ka shiga jiya daga zuwa gidan su Umaimah kamar wadda ta yi tafiya wani gari?"
"Ba zaki gane baaa yarinya,nace ba zaki gane baaaaa, amma nan da wani lokaci kaɗan zaki gane komai, yah kin tara kud'in anko muje mu siyo ko ki na nan ba ki da ko sisi?"
"Eh na tara dubu uku da dari biyu,"
"Ba laifi in an tashi muje.mu siya,ke ni har na sai takalmin da zan saka ma jiya,"
"Habaa dai ! lallai ke babba ce qawata,"
Murmushi tayi saboda ita wannan yabon da take samu daga qawayen ta na lungun su yana mugun d'aga mata aji ainun, sai ta dinga jin kamar ita ɗin wata Zahrah Buhari ce.
Bayan sun isa makaranta ne ta samu waje ta zauna a nutse, yi tayi kamar bata ga Umaimah ba ma dan kar ace ita take manne mata, Umaimah bata damu ba ita sai ta zira hannu ta tabo ta, murmushi suka sakar ma juna, sanan suka miqawa muna hannu suka gaisa a mutunce, Umaimah ta ce,
"Ya ki ka je gida jiya? Dik da na san lafiya qlou zaki isa tunda Yah Umar ne ya maida ki,"
"Kwarai kuwa, lafiya qlou na isa gida, dan kuwa Yah umar akwai mutunci,"
"Sosai ma kuwa, sai ma kun saba zaki ga hakan,"
Jameelah murna ce ta kama ta da jin kalmar sabo a tsakanin ta da Umar a ranta ta ke ayyana,
'Wayyyoo Allah ka matso da ranar sabawar mu nan kusa'
A zahiri kuwa sai ta dafe qirji ta zaro idanu waje ta ce,
"Ni Jameelah ni me zai kaini sabawa da namiji kamar Yah Umar? Ai ni din ba ajin shi bace, ko ke ɗin ma dan kina qanwar shi ne amma da sai nace yafi qarfin kula ki bare ni 'yar talaka jikar talakawa"
Murmushi Umaimah ta yi sannan ta ce,
"Mu ba haka muka dauki rayuwar mu ba Jameelah, kuma na tabbata a jiya kin gane hakan da idanun ki,ko Mum sai da tace na gaida ki da safen nan kafin na taho saboda kin burge su, kin shiga ran Mum sosai"
A cikin zuciyar ta ta buga ihu tare da murna ta ayyana,
'Alhamdu lilLAAH uwar mijina na sona'
A zahiri kuwa sai ta ce,
"Allah sarki Mum ba ruwan ta itama, ki gaidan ita sosai in kin koma, kinga karbi haddata kiji min,"
Mamaki ne ya kama Umaimah da Mamalo dake manne da su tana jin tattaunawar tasu,amma dole suka shanye mamakin su dan kuwa gimbiya Jameelah ko a jikin ta sai ta fara zubo karatun qur'anin da ya sake tsunduma duk wani mai sauraron ta a cikin duniyar mamaki,daga qarshe dole Umaimah ta shanye nata mamakin ta kasa kunne ta na sauraran haddar Jameelah wadda ke zubo karatun da murya mai dadin sauraro, sabon malamin su da ya shigo ya ji karatun da take zubawa nan take ya kira ta ya tambayi sunan ta saboda ta burge shi sosai.
Bayan ta sanar da shi ne ya ce ta je ta zauna sannan ya gabatar masu da kanshi a matsayin Malam Haroon, sannan ya nad'a ta matsayin Monitan ajin,nan da nan 'yan aji kuwa akai ta ihu suna kiran ba sa so, wasu daga qawayen ta gudun kar ta ce harda su aka ce ba a son ta su kai ta cewa suna so.
Ko bi ta kan su baiyi ba aka fara karatu, ganin haka yasa Jameela dagewa sosai dan kar ta ji kunya.
Malam Haroon baqi ne kyakkyawa kuma Ustaz dan kuwa wandon shi ma a dage yake ga gemu mai kyau daya kwanta a fuskar shi, yana da gira cikakkiya kamar an zana ta, yana da tsananin tsafta, da kuma ilimin addini, yayi boko amma iyakar shi secondary, daga nan ya ci gaba da maida hankali akan kasuwanci da neman ilimin islama.
Iyayen shi sun rasu daga shi sai yayan shi mai suna Ishaq,Haroon yana zaune ne a gidan yayan na shi wanda ke da mata guda ɗaya, Yah Ishaq yana da kuɗi sosai shi ɗin babban ɗan kasuwa ne, ana saida manyan laces, dogayen riguna, atampopi shaddodi da mayafai a shagunan shi, matar shi Hauwa'u mace ce irin 'yan duniyan nan masu yin abinda suka so a gidan miji ba tare da ya sani ba, Haroon ya san dik wani iskancin da take aikatawa na zuwa wajen bokaye dan mallake ɗan uwan na shi,Hauwa'u na matuqar son Haroon fiye da yanda take son mijin ta Ishaq, a cewar ta Haroon ne mai jini a jika yayan shi dik ya zama sauran basir, yanzu haka Haroon a cikin matsalar matar Yayan nashi Hauwa'u yake, dan kuwa ta ɗana