Showing 3001 words to 6000 words out of 118783 words
nak sannan na dawo gida, baki ga dukan dana sha ba yau a makaranta, amma yayi ta banzar tinda na ci abincn gidan masu kuɗi, ya Allah ka nuna min na shiga daula irin ta su Umaimah,"
"Ameeen yarinyar kirki in Allah ya yarda maqiyan ki sai sun zama fadawan ki, har shi malam Isyakun dake dukar min ke kamar nace masa jaka na aika masa, ko kallon kalar fatar jikin ki ba zai yi ba ya san ke ba kalar duka bace,so ya ke wataran na wanke qafa na je na masa rashin mutunci, amma ya ci gaba kar ya fasa, watarana ko da miliyoyi aka bashi bulala aka ce ya dungure maki kai ma ba zai iya ba, wuce ki shirya abin ki,"
Ɗan qaramin towel ɗin ta ta dakko ta daura sannan ta saka wani dan qaramin hijab daya manne mata a jiki, ta dauki soson wankan ta da ruwa a bokiti ta fito tsakar gida nan ta wuce mazan dake diban abinci da abubuwan da suke saidawa a kasuwanni sai bin ta suke yi da kallo wasu ma har leqowa suke yi dan su qare mata kallo da kyau.
Ba ta wani dad'e ba a band'akin ta fito, tana ta mita da surutu akan qazantar bandakin nasu na gidan yawa tare da roqon Allah ya nuna mata ta bar wannan gidan gandun ta huta da bala'i.Tana addu'ar Ramai na amsa mata da Ameen.
Kwalliyar da ake yayi a wannan zamani ta sheqa ta yi masifar kyau kamar ba 'yar talla ba, daga bisani ta samu wani riga da skirt masu kyau na wani yadin material kalar sky blue, ta daura dankwalin ta a gaban goshi ya zauna dasss kamar hula,skirt d'in da ta sanya kuwa ya matse mata qugu da kyau irin yanda take so ya zauna das a jikin ta ko alamar space babu, ga rigar qarama ce sosai itama a d'ame da fatar jikin ta,qirjin ta kamar zasu fasa ihu su fashe saboda yanda ta matso su, turaren ta ta dauka ta hau fesawa kamar bata so,sai tauna cingam take yi yana qara, yar qaramar lalitar ta ta d'aura wadda ta samo a gwanjo mai hoton biri a jiki mai laushi ta na kammala shirin ta ta fito tsakar gida ta na hura hanci sai ka rantse wani wajen zata mai mahimmanci ba wai tallan abinci ba, ta na fitowa kuwa nan da nan kallo ya dawo kan ta, tin tana fesa turare kowa ke Allah-Allah ta fito, mazan zauren can waje har leqowa suke saboda sun san ta kusan fitowa.
Da wani irin taku dai-dai ta qarasa fitowa tsakiyar tsakar gidan, sabon takalmin roba daya dace da kayan ta Ramai ta cire a leda ta watsa mata gaban ta ta na murmushin jin daɗi tare da alfaharin wannan kyakkyawar 'yar ta ta ce, aiko cike da murna Jameelah ta saka takalman tana murmushi Itama.
Abincin da take saidawa a soro na biyu an riga an girke mata shi ita kawai ake jira, maza kuwa sai layi suke yi suna ta yi wa junan su rashin mutunci duk saboda ita, masu hankalin su wanda da gaske siyan abinci ke kawo su ci su tafi ne ke masu nasiha akan su bar yin faɗa kowa zai samu tunda ba su kaɗai ke saida abinci a gidan ba.
Tana zuwa ta wani d'aure fuska ta zauna a kujerar da in ta zauna akai take jin kan ta kamar a office take, nan take ta kalli Babawo ta sakar masa murmushi, shima murmushi ya sakar mata da kyakkyawan haqoran shi da suka rine da hayaqin sigari,gira ya daga mata ta sake sakin wani sabon murmushin.
Nan da nan ta fara zuba masa abincin sa, wanda baya bata kud'in a wajen sai da dare in ya zo zance a nan ya cake mata kudin ta,banza tayi ma masu kiran sunan ta ta je har gaban shi ta aje masa, sannan ta juya tana kad'a mazaunan ta Babawo ji yayi kamar ya ture mutanen dake wajen ya riqe ta tsam a jikin shi,wani ihu ya kurma sannan ya ce,
"Allah ya kaimu dare,bu.....ub....nan kayyasa"
Abincin ya ja gaban shi ya dau spoon yana ci yana santi tare da kallon ta, haka tai ta zuba abinci tare da masu taimaka mata tana masifa kamar wadda take basu kyauta,wasu kuma da ta san suna bar mata canji in sun sai abinci sai ta washe masu baki har da fari, su na sane suke bada dubu ɗaya su ce a yi masu had'in ɗari biyu ko uku su bar mata canji, wasu ma dubu biyu zasu dunqule su bayar ta zuba masu na dari uku suce ta riqe sauran tsabar rashin sanin ciwon kai dan kuwa da damar su ma masu aure ne sun baro gida ba na cefane amma suna kashe wa wadda bata da lokacin su kuɗi.
(Sun baro halal din su sun taho su na yaba haramun,matan su da yara a gida kuwa ko za su wanke kan su a inji ba sa burge su, wannan ta wajen da ba halalin su bace shaid'an ya qawata masu ita su na ganin ta ma fi matan su na aure kyau,sannan ita ta fi cancanta su yi wa kyautar kud'in da zai iya ci da iyalan su.)
Baban ta ne ya zo zai shige gida yana takaicin yanda d'iyar cikin shi ke wannan sana'a da ya hana ya hana amma anqi ji, ya tabbata tinda ya ganta da wuri haka, ko dai bata je makaranta ba ko kuma ta gudo, dole dai akwai dalilin dawowar ta ta da wuri.
Rasa hanyar wucewa ya yi dan kuwa cikin gidan ma kan shi maza da mata ne a cakud'e ana ta hada-hada, ji yayi ba zai iya zaman awa ɗaya bama a gidan, dan haka sai ya fidda dubu ɗaya ya bawa Ramai yace ta qulle masa abincin sa a leda zai koma can wajen aikin shi yaci, aiko ba godi bare na gode ta amshe,haka rayuwar ta take sam bata san meye godiya ba ita, dan haka baya ganewa idan ya kyautata mata shin ta ji daɗin abu ko akasin hakan
Zuba masa tayi a ledar ko arziqin kwano bai samu ba a matsayin sa na mai gidan ta miqa masa, ya ko sa kai ya bar gidan yana zuwa soron ya jiyo muryar Jameelah ta na ihun sai an cake mata kudin ta casss ba za ta yarda ba,sai wani fari take yi tana zaro idanu waje.
Ganin yanda ta cukuikuye ɗan barno yasa Baban ta daka mata tsawa, sannan yace masa ya tafi ba tare da ya biya kuɗin ba,
Cike da rashin kunya haɗe da tsoro-tsoro tace wa Ɗan borno,
"Zaka dawo zaka ga ni indai a waje na ne ba zaka sake cin abinci ba, kuma dik inda na ga kuɗi a wajen ka sai na k'wace,"
"Allah ya shirya min ke jameela,"
Shi ne kawai abinda Malam Jameel ya iya furtawa cikin takaici ya wuce wajen sana'ar shi, ita kuwa haka ta ci gaba da banbamin faɗa tana bada abincin ta.
Sai wajen huɗu na yamma suka tashi daga wajen saida abincin, da wuri abincin ta ya ke qarewa amma bata shiga gida da wuri anan zata zauna har huɗun ko biyar na yamma,zama take su yi ta wasa da mazan wajen da ita da Mamalo da sauran yaran matan gidan da sunan amso kwanuka da kud'in abincin su.
Wata ma direct a mazaunan ta namiji zai d'aka mata duka sannan a bata kud'in tana dariya tana fad'in "kaaabaaariiii" wanda bai kai zuci ba.
Bayan sun gama sai su ka shiga wajen iyayen nasu suka miqa kudin da su ka yo a ranar,gidan ya yi dan dama duk an tattafi sai masu naci da masu siyan kwantan abinci wajen wanda suka yi kwantai, Mamalo da Jameela ne zaune suna tatauna yanda za su yi wankan yau.
"Kin san me? Yau mu qure wa wanka laya, yaran layin can wai har damu suke takara, atampar da kika saka rannan ta wajen Babawo shi wai Saudatun qasan layi ta sa itama shekaran jiya,ya kamata mu shiga kasuwa fa saboda gaskiya kayan mu sunyi qasa.
"Dan Allah fa? Rabu da 'yan wahala kin ji Mamalo duk abin su ba za su taɓa kamo ni gayu ba sai na wuce su biyo baya na ni ce zan dinga raba wa 'yan hassada aiki ba biyan albashi, amma rabu da ita yau zata sha mamaki ,dan kuwa kayan da zan saka kowa bai sanni da su ba ma, zata san dani take gasa a layin nan, sai na gasa ta sosai kamar aya,"
"Shi yasa kike burgeni tawan, ni kam ko aramin wanda ki ka saka waccan juma'ar kiyi dan Allah, sai na shirya a d'akin ku, kin san Lantai matsala ne da ita ba zata barni ba(kun ji 'yar zamani mai zamammiyar qeya ko?)
"Kar ki damu Mamalo kema leshi zan ara maki ki saka yau,ni wannan da zan saka yau kuɗi na tara na siya na kai ɗinki jiya na amso, yau kuma zan buga abuna na ji shegiyar da zata faɗan maganar banza,"
Su na gama tattaunawa suka sallami juna kowa ta wuce d'akin su, ta na shiga ta cire kayan jikin ta dan ta na so ta huta kafin magariba a yi shirin fita zance kuma,ta na nan kwance ba tare da ta tuna bata yi azahar ko la'asar ba ta hau rera dik wata waqa da ta zo mata a kan ta, (kanta baya ja wajen hadda amma yana ja wajen waqa Jameelah ta daban ce)
A haka bacci mai daɗin gaske ya sace ta, kamar wadda aka kwad'awa mari haka ta miqe a firgice a zato na ma tunawa ta yi da bata yi sallah ba sai na ga ta miqe tsaye ta hau sauya doguwar rigar da ta saka kafin ta kwanta zuwa wani lace ruwan zuma farar saqa mai guntun hannu da fad'in qirji, rigar guntuwa ce dan kuwa da zata ɗan d'aga hannun ta sama ba abinda zai hana a ga cibiyar ta,skirt ɗin rigar ta saka matsattse sosai,sai ta qasa ya bude sosai,ta kafe kan nan da d'auri mai kyau,ga kwalliyar ta nan bata goge ba, Jameelah saboda son gayu na musamman ta sai kayan kwalliya masu tsada irin wanda ake amfani da su a saloon,ta yi hakan ne dan ta nuna wa sa'annin ta ba ɗaya suke ba, da ta yi kwalliya za ka gane da kayan kwalliya masu tsada ta ke amfani, lokuta da dama idan za a yi aure ma har baiwa qawaye aro take yi dan ta nuna masu sune a qasan ta ita ta wuce ajin su.
Mayafi siriri ta yafa a kafad'a ɗaya ta saka takalmin ta kalar mayafin, tana wani shan qamshi tare da tauna mutumin nata wato cingam, kudi ta Karb'a wajen Ramai tace zata siyo abinda zata ci yunwa take ji, cike da washe baki Ramai ta ce,
"Ga shi, mai nemowa ai in baya ci yana qoshi wataran sai an nemo shi, sai kin dawo,"
Jameelah na fita tsakar gida ta ɗauki buta ta kurkure bakin ta sannan ta hau kwala wa Mamalo kira,
"MAMALOOO ! idan baki fito ba zan wucewa ta fa,"
Karkad'a jiki take yi ita a dole ta makara kamar wata wadda zata je wata ma'aikatar.
Can sai ga Mamalo ta fito sanye da wata shadda da ta ɗan sha wanki, amma ta amshe ta ba laifi tayi kyau sosai itama dai-dai kyaun ta,
"Kin ari kaya a waje na me yasa baki saka su ba? ko 'yan baqin cikin iyayen naki sun hana ki sakawa ne? Dama ni dan ki kankaro wa kan ki mutunci ne yasa nake ara maki, ki qure wanka kema a gan mu ba raini amma tunda sun hana sai mu jera kowa ya kalle ki kamar wata mai aiki na,muje ya na iya,"
Mamalo ta muzanta sosai dan bata ji daɗin abinda Jameelah ta yi mata a tsakar gida ba kowa na ji da gani, amma haka suka ɗauki hanyar zuwa shagunan da ake saida kayan kwalama irin su shawarma da gasasshen kifi da meat pie da sauran su.
Su na isa Jameelah ta shiga wani sanannen shago a wajen haka ta hau nuna abinci kala-kala sai ta yi wani fariiii farrrr da idanu tare da lanqwasa harshe tana kad'a qirjin da ba ta gama rufewa dika ba tare da yatsina ta tambayi farashi,a haka suka gama siyayyar su a wajen suka faɗa wani shago da ake saida qananan kaya nan ma ta sai abinda za ta siya suka ɗauki hanyar komawa gida mai nisa, dan bata so su isa gida da wuri,ta hanyar makarantar su suka bi har an tashi yara kowa ya wuce gidan su sai qalilan da ɗaukan su ake yi su na zaune a waje ɗaya su na jiran iyayen su dan kuwa magariba ta gabato, su na isa layin su ta qarasa cire siririn mayafin da ke kafadar ta ta hau jujjuya shi a hannun ta ta na wani juyi da jikin ta ta na lilo da ledar hannun ta,a dai-dai inda suke zama su yi zance ta ga Babawo babu b'ata lokaci kuwa ta tsaya a wajen suka zauna, Baban ta kuwa na tsaye a qofar gida dan bai jima da dawowa ba ya ga qofar gidan da duhu wanda ya san ya saka k'wan fitila shekaran jiya da safe amma gashi yau ma har an samu wanda ya fashe shi, sai duba wajen k'wan lantarkin gidan yake yi yana mamakin kusan koda yaushe in ya saka k'wai a wajen sai an samu mai fashe shi, amma har yau ba a kama me aikatawa ba ya na gama dubawa ya shige gida ba tare da ya san ya baro 'yar shi a bayan shi ba.
Zaune suke su na ta hirar soyayya abun su Mamalo ma na tsaye tana masu hira itama, anan suka cinye abinda suka siyo ta duba sabuwar shimi da panties ɗin da ta siyo a gaban Babawo ko kunya bata ji shi kuwa sai yabawa yake yi tare da fatan watarana ya siyo mata wanda suka fisu kyau ta saka a gaban shi ya gani,suna gama ganin kayan Babawo ya fiddo naman daya siyo mata suka hau ci.
Kafin a kira sallar isha'i naga 'yan mata na ta fitowa cikin wanka da kwalliya kamar ana wani kwarya-kwaryan biki a layin cike da mamaki na buɗe baki ina bin su da kallo..........
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻. MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 4:
kamar kullum yauwa da safe haka Jameelah ta tashi ta kammala dik wani shiri data saba yi ta shirya dan zuwa makaranta, tare da qudirin yau zata sai dik abinda take so a lokacin break,idan ya so daga baya sai ta sanar ma da Umaimah tana son ta bita gidan su ranar juma'a, so take dai sai ta ga gidan su Umaimah hankalin ta zai iya kwanciya, babbar motar da ake kawo ta ake ɗaukan ta na matuqar girgiza ma Jameela zuciya, ga irin cimar da take kawo masu makaranta kullum kala-kala na sake tabbatar mata da su Umaimah masu kuɗi ne,dan kuwa haka take zuwa musu da kaji a cikin abincin su suci har su qoshi, sannan wataran ruwan roba take zuwa da su gora biyu zuwa uku, ga kudi da bai gaza dari biyu ba ita ko hamsin in ba ta zara a na abinci ba ba mai bata.
Karatu ake ta zabgawa a ajin nasu ko da ta isa,kowa ya maida hankalin akan abinda ake koyarwa banda Umaimah wadda ta tattara hankalin ta gaba ɗaya akan qirjin Jameela, wanda a ran ta take matuqar mamakin cikar su, a iya tinanin ta shekarun su daya amma ita da tafi Jameelah girman jiki bata da cikar girji irin na Jameelan, ikon Allah kawai take ta kalla.
Kamar daga sama ta ji muryar Jameelan, cikin kare baki dan kar a gan su ta ce;
"Yaushe wai zaki kai ni gidan ku ne? Ko dai baki son naje cin arziqi nima? Lallai Umaimah ban taba sanin ke marowaciya bace sai yau, ashe dik abinda ki ke ban a iya nan ne ba zaki iya gayyata ta gidan ku ba? Himmm duniya kenan, yau da ace nima 'yar wani ce da tini kin gayyace ni, shike nan, na gane irin zaman da zan nayi dake daga yau,"
Cike da mamakin yanke hukuncin da Jameela tayi a kan ta take kallon ta,
"Kinyi kid'an ki kin yi rawar ki,kin taɓa ji nace bana son na kai ki gidan mu, Kawai daga fara magana sai ki qarasa ta da kan ki? Ni ba wai bana son kai ki gidan mu bane,halayen da kike yi ne bana so,haka kawai na je na kai ki gidan mu ki jamin faɗa, gaskiya shine dai matsala ta dake"
"Indai wannan ne matsalar ki an kauda ita,yanzu yaushe zaki kai ni?"
"Ko rannn.... wayyoo Allah malam,"
Saukar bulala ce da ihun Jameelah ya karad'e wajen, nan da nan kuwa Umaimah ta nutsu ta shiga hankalin ta saboda tasan dukan akan ta zai qare daga qarshe, dan kuwa Jameelah ta riga da ta jawo mata duka, shirun da ta ji ne ya tabbatar mata ita ba za a dake ta ba.
Qunquni Jameela take tayi ta na fad'in,
"Yarinya ba dan ina son naje gidan ku ba ko dan na bada labari kuma na ci daɗi nima da sai na fanshe dukan nan a jikin ki yau,"
Bayan an tashi break, Mamalo ta ce ma Jameela,
"Qawa zo muje ki ji, ki yi sauri akwai labari, na jira ki mu taho aka ce ai kin yi gaba,"
"Ban na sha mutuniya ta, nima ki ji nawa,"
Nan kowaccen su ta faɗa ma 'yar uwarta yanda suka yi da saurayin ta, cike da zumud'in jin qarshen yanda Babawo ke ma Jameela wasanni Mamalo ke kallon ta, sai da ta gama ji ta d'akko dubun ta ta nuna wa Jameelah, aiko Jameela na gani ta ce,
"Yauwaaa ya kamata ki fara tarin kudin ankon Furairah, kinga kar azo baki dashi, dan ke ba kullum kike samu ba,"
"Waya fada maki? Ai yanzu Sadeeq yace ina fada masa komai nake so, kuma zai dinga ban dubu daya kullum, amma kin san meke damuna? Ni nafi son muna irin soyayyar ku, amma shi kwata-kwata ya qi ya na abu kamar wani baqauye"
"Wai me kuke ta tattaunawa ne haka? Kunyi