Showing 6001 words to 9000 words out of 118783 words
shiru, ko kuna bitar karatun dazu ne,"
Wata harara Mamalo ta watsa wa Umaimah da ta matsa kusa da su, Mamalo na jin kishin yanda yanzu Jameela ke qawance da Umaimah sosai,cikin washe baki Jameelah ta ce wa Umaimah,
"Babu komai zauna muyi hirar dake,"
Bayan sun gama hirar su suka hau cin abincin su Umaimah, daga nan suka je wajen yin break suka dinga siye-siyen kayan kwalama da abinci, a wannan ranar sai da suka ci suka yi nak sannan suka koma aji.
Lokacin da aka tashi kowa sai ya tafi gida,cike da zumud'in zuwa gidan su Umaimah Jameelah ta koma gida, dan haka tin a ranar ta ware kayan da zata saka dik randa zata je gidan su Umaimahn, kaya ne masu kyau da tsada ta ɗauka ta ajiye a saman jakar kayan ta,dama ita ta na tanadin irin kayan fita unguwa na ba raini ɗin nan da kud'in talla ko na samari take siyan irin kayayyakin, tare da taimakon Ramai za a mata dinkin na garari dan kuwa watarana ma Ramai ce da kan ta zata kai mata tace wa tela ayi mata dinkin 'yammata da ake yayi dan kuwa 'yar ta ta 'yar zamani ce, haka za a yi mata dinki ko a auna ta dik Ramai na gani, matsattsen dinki daya bayyana kowacce surar ta amma sai Ramai tana jin daɗi har cikin ran ta ta na jin cewar diyar ta kyakkyawa ce da ba kamar ta a layin har ma da layin dake kusa dasu.
Cikin ja da baya ta ke kallon kayan da ta fitar dan zuwa gidan su Umaimah Jameelah ta ce,
"Toooo yanzuuuu ina zan samu hijab babba, mai dan kyau da zai shiga da kayan nan, ina da takalmi da jakar da zan saka 'yar qaramar can dana siyo a gwanjo, kaiii Allah yayiwa gwanjo albarka, gaba daya sai ka siya kai luf a bayan shi, a zaci dama abu na ka ne tin fil azal,Allah dai ya biya masu gwanjoooo, Ramaiiii!"
Ta k'wala wa mahaifiyar ta kira da ke tsakar gida, babu b'ata lokaci kuwa ta amsa kamar ita ce 'yar ba uwa ba.
"Na'ammm 'ya guda ɗaya tamkar zinare ya aka yi?"
Cikin shagwaba da bubbuga qafa da wani yauqi da tasan yana qara mata kyau ta burge dik mai kallon ta take maganar, hakan kuwa na tasiri a zuciyar Ramai sai tana ganin ohhhh ni nake da wannan kyakkyawar d'iya, domin Ramai in ba fari ba gaskiya sai a hankali ce, amma kyau da hasken fata na wajen Baban Jameelah, dik da dai yanayin aikinsa ya sa ya yi duhu.
"Ramaiiii ! kinga wannan qawar tawa Umaimah ce ta gayyacen gidan su ranar juma'a kuma banda hijabin sakawa, dan gidan su gidan Ustazai ne bana son zuwa da mayafi hijabi nake so na saka dan Allah ki ban kuɗi na d'inka hijabiiii, tayi tayi naje gidan su saboda rashin hijabi yasa ban je ba har yau,"
"Me yayi zafi ina da kuɗi kuma kece me nemowar muje ciki na baki"
Da murna a ran ta tabi Ramai suka koma dakin, amma a fuska sai ta nuna kalar shagwab'a da tausayi kar ace dama son amshar kuɗi kawai take yi tunda Ramai ta san halin ta sarai, ba zato babu tsammani suka ji muryar Bukar na fad'in,
"Ni ma Yasin sai an ban wani abu, kullum sai a dinga bata dik abinda take so ni ba me bani, inna sata ace min b'arawo, ai in ba a son yaro ya ɗau abin da ba na shi ba a dinga bashi abu in yace yana so,"
"Sannu ubana, nace sannu ubana, ga ta nan, dube ta daga sama har qasa wa ka taɓa gani me kyau a dik layin nan sama da ita? Amma ba talla take yi ba dan a rufa wa kai asiri? Nan take sai da abinci ta sama mana wannan kud'ad'en da ka sa wa ido, kai ruwan piyawata nace zan dinga baka kaima kana zama qofar gida,da aka yi sau ɗaya ka tattara kud'in kai gaba kasha maro abin ka,to tsoron ka nake yi da zan sake baka kid'i na? Ka fita daga ido na in rufe Bukar, ka iya faɗan min abinda ya zama wajibi iyaye su wa yaran su amma baka iya aikata wanda yara zasu ma iyaye dan suna sama masu kudi ba ko,bar nan kan na ma rotse dan uban ka,"
"Habaa Ramai ko hamsin ki bashi mana ya sai wani abun ko ɗari ce ma haka,"
Dan bata fuska ta yi kafin daga baya ta d'au wata tsohuwar ɗari ta wurga masa, da murna ya dauke yana mata kirari, sai ga baki an washe, ana cewa
"Ja'iri ! sauran a sai sigari kuma, da kudina dai aka sai sigari ban yafe ba,"
Ficewa yayi yana mata dariya, har sholi an sha da kudin ta dan sigari, yafiyar ta ba abinda zata yi masa a ganin shi.
(Ina fatan ko da ban sharhi ba kun fahimci saqon wannan kalaman nata, ta kira shi ja'iri, da damar mutane suna ce ma yara ja'irai wanda ya na nufin 'yan wuta kenan, da wasa ba a sani ba ana kiran yara 'yan wuta, sannan tace ma yaro mara jin magana bata yafe ba, ko sanin amfanin ta bai ba balle yafiyar ta a gare shi, bare har ya kiyaye me tace kar ya halaka,kenan in ya aikata abinda tace masa din Allah zai iya sawa ya qara lalacewa, tinda tace bata yafe ba? Mu kiyaye mu kula da bakunan mu akan yaran mu)
Hijabi mai kyau Jameela ta siyo kalar ja mai shiga sosai, dan kalar atampar ta kenan, so take ta burge sosai, amma dole sai ta nuna ma iyayen Umaimah su talakawa ne dan a tausaya mata, sosai.
******************************
Rana bata qarya sai dai Uwar d'iya taji kunya, yau juma'a kuma yaune ranar da Jameela zata je gidan su Umaimah, da kayan ta ta tafi a jaka, fuskar ta yau ba kwalliya, asalin kyaun ta ya bayyana, sai qamshi take zubawa, haka ta saka uniform ta tafi makaranta sai taunar cingam take yi.
Ta tinama Umaimah zancen binta gidan su da za ta yi yafi sau bakwai, Umaimah dariya tai ta yi mata, daga baya tace,
"Ina sane da wannan ranar Jameela dan kuwa na sanar ma da Mum din mu, ta san da zuwan ki, yau kina da sa'a dan kuwa Dad na nan shi ma, Yah Umar ne ban da tabbas din zaman shi a gida, amma ina fatan ya ga babbar qawa ta shima a yau,"
Tsaki mamalo ta yi dan jin ance ma Jameela itace babbar qawar, cikin jin haushi Jameelah ta kalli Mamalo ta ce,
"Dalla meye na yi wa mutane tsaki? In ba za ki ji hirar mu ba ki bar nan ba wanda ya ajiye ki,"
Washe baki Mamalo tayi ta dafa kafad'ar Jameela, Jameela ta zame hannun Mamalo da ke kafad'ar ta, umaimah kuwa ta gama gano mamalo, dan haka kawai sai ta buɗe Hadith ɗin ta tana bita ta yi masu shiru, Mamalo sai hirar gida take yi masu tana ta zuba qarya, anyi kaza da kaza a d'akin su, Jameela kuwa bata son ai ta bada labarin gida a makaranta yara su gane talaucin su, ana mata kallon babbar yarinya,cikin hasala ta sake cewa Mamalo,
"Dalla ki yi mana shiru, kamar a gidan ku ne kawai ake cin biredi da bota,"
Dariya aka dinga yi wa Mamalo ta yi abin tausayi, ta d'au jakar ta ta koma nesa da su ta fara karatu, Jameela sai kuma ta ji babu daɗi, amma haka ta basar ta ci gaba da manne ma Umaimah.
Drivern su Umaimah ne yazo daukan su ta buɗe mota ta shiga, Jameela data sauya kaya a aji bayan kowa ya fita ta buɗe ɗayan side d'in ta shige, Mamalo na tsaye zuciyar ta baqqirin ji tayi dama ace itama iyayen ta na da kuɗi dan kawai ta burge Jameela, tana son ta da abota sosai, haka ma jameelan amma tafi son umaimah domin kud'in su.
Suna tafe tana ta ganin unguwannin masu kudi tana ta santin gidajen a ran ta, amma a fuska ba zaka taba gane irin son abin duniyar da qaramar yarinya irin ta take ɗauke da shi ba.
Wani qaton gida taga an nufa, iska ta shaqa mai daɗi ba mai warin kwata da sigari da hammata ba na unguwar su, wata kwallar kwad'ayi ce ta taru a idon ta a zuci take roqar Allah daya fito da su daga wancan lungun nasu ya kawo su sarari irin wannan.
"Jameela menene Ko baki son zuwa ne? Ko wani abu ke damun ki,"
Cikin sauri ta buɗe baki tace,
"Ni ce bana son zuwa nan din? Hauka nake da zan ce bana son zuwa irin wannan wajen? Shiga gaba muje ki gani,"
Da sauri ta bi Umaimah, tana sake qarewa kyakkyawan gidan Kallo.
Bayan sun shiga cikin gidan ne Jameelah ta samu qasa gefe da inda Iyayen umaimah suke ta zauna kan ta a qasa take gaida su, sun yi matuqar yabawa da tarbiyyar ta, sun ji daɗi da 'yar su ke da qawa irin Jameelah mai kamun kai da matsuwa, sunyi sunyi ta zauna a kujera amma taqi.
Kayan motsa baki aka kawo mata kala-kala dakin Umaimah saboda ta qi shan ko ruwa a gaban iyayen Umaimahn, tana shiga taga gado babba da kayan alatu irin wanda take mafarkin mallaka a d'akin ta a matsayin ta na budurwa me tashe, ji tayi kamar kar ta koma gidan su, zama ta yi a kan gado, ta yi juyi ta sake juyawa, can kuma ta kwanta ta yi lamooo, daga baya ta miqe da sauri ta sauka qasa ta hau cin abubuwan da aka kawo mata ba qaqqautawa, Umaimah na ta yi mata dariya.
Allah Allah take Umaimah ta dan fita ta kwashi lemukan ta sa a jaka, amma umaimah ta gano ta sai tace,
"Kar ki damu qawata kici wannan, in zaki tafi gida zan baki wasu,"
"Dan Allah? Yanzu kuna da irin wannan da yawa kenan? Ai kuwa zan din ga kawo maku ziyara akai akai,"
Dariya Umaimah ta dinga kwasa wajen Jameela.
Suna zaune mai aiki tayi kiran su akan suje a ci abinci cike da zukud'i Jameelah ta miqe, sai bayan ta yi gaba sai ta tsaya sai da Umaimah ta wuce sannan ta bi bayan ta, a table ta gan su zaune, kasa qarasa wa ta yi saboda sumar da tayi a tsaye a wajen, jiri ne taji yana d'iban ta, hankalin ta ya kai qololuwa wajen karkata wajen table din da abinda ke tattare da shi, Umaimah na taba ta dan su yi gaba taji ta taho mata gaba ɗaya kamar zata faɗi, da kyar ta tsaida kan ta ta samarwa kan ta natsuwa, qafa ta daga zata yi tafiya amma taji ta mata nauyi, idon ta kuwa ko qiftashi bata yi dan gani take kamar da ta qifta shikenan ta daina ganin abinda ke gaban ta da ya fi komai kyau a idanun ta da zuciyar ta............
[11/09, 2:28 pm] asiyahabibu93: 💅🏻 MAZAUNA GIDA 💅🏻
WRITTEN BY HAERMEEBRAERH
PAGE 3:
Wasu 'yan matan tabarmi na ga suna shimfidawa wasu kuma sallaya, wasu kuwa kujerun zaman gida('yar tsugunno) suka dasa guda biyu su ka zauna da samarin nasu, Mamalo na ɗaya daga cikin wanda suka shimfid'a tabarmi domin kuwa saurayin ta Sadeeq mutumin kirki ne yana matuqar son ta auren ta yake son yi, dan ma iyayen ta sun tsaya masu wala-wala da tini ya turo, daya sako maganar aure sai Lantai tace nawa ma Mamalon take? dika-dika shekarar ta sha biyar, me zai tsinta a wajen ta? Dole haka Sadeeq ke hakura ya bar maganar ya yi ta fata da addu'ar Allah ya kai su lokacin da zata qara girma ta kai aure ya aure ta su yi zaman aure.
Qarfe 9: 45 na dare baka jin maganar kowa sai mutsu-mutsu da 'yan dareraiku sama-sama a wajen 'yan mata da samarin layin su Jameelah, soyayyar shan minti kawai ake zubawa a lungun nasu, Jameela da Babawo kamar zasu shige cikin junan su tsabar mannuwa da suka yi da juna,ba qaramin jin daɗin rigar da tasaka mai faɗi wadda ake kira da ziro hannun ka masoyi Babawo ya ji ba, hannun sa ya zura ya na ta zare idanu kamar ya biya sadakin ta.
Mamalo kuwa ran ta in yayi dubu ya baci saboda Sadeeq ba abinda yake yi mata da ya wuce wa'azi akan abubuwan da ya ke ganin matan layin na su na aikatawa, juya kai tayi ta yi fari farrr da ido sannan ta murguda baki tare da sakin siririn tsaki sannan ta ce,
"Wai kai dan Allah Sadeeq yaushe zaka waye ne? Ka duba fa ka gani kowa sai jin daɗin shi yake yi, amma kai ka wani qame a gefe wai kai ustaz, ka mori quriciyar ka tin kafin tsufa ya riske ka,haba malam ! A yi mutum gaba ɗaya shi bai san mene ne soyayya ba? ko dan kalaman nan na soyayya ni baka jiqa ni da su, ko irin yanda saurayi ke fad'awa budurwa yanda yake ji game da ita da yanda zai mata bayan sunyi aure kai baka iya ba, gaskiya ni da sake,ba zan dauka ba, ka waye kawai mu mori rayuwar mu,"
Sadeeq baki sake yake kallon ta a qalla ya bata kyawawan shekaru takwas amma yarinyar nan bata ji nauyin sa ba ta rufe ido tana fada masa yanda zai gudanar da soyayya, lallai wannan zamanin namu na cikin rud'ani, wa'azi ake yi akan yanda lamura suka tab'arb'are, fadakarwa ake yi amma kamar ba a yi.
"Yanzu dan Allah Fateema abinda kika faɗa bai maki nauyi a bakin ki ba? Ko kunyar faɗa min waɗannan kalaman baki yi ba? Iyayen ki cewa fa suka yi na basu nan da shekara biyu ko uku, ke har yanzu yarinya ce amma shine....."
"A ganin su ba ! ni fa da ka ganni nan ba abinda ban sani ba, in zaka sake jiki muci soyayya ka sake, ba dan ma ina son ka ba ko bi ta kan ka zan yi ne? ina son ka fiye da yanda nake son kaina, kuma bazan iya rayuwa ba kai ba, shi yasa ma kaji ina fada maka me nake so a yanzu, banda haka aje ka zan yi a gefe na nemi wani,"
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un ! me kk ce Fateemah ? Kamar ke ki ka iya fad'in zaki aje ni ki nemi wani saboda ba na yi maki muguwar soyayya? Yo muguwar soyayya mana wannan ai ba soyayyar gaskiya ake gudanarwa ba sam,Wai me ki ka dau soyayya ne ma tukunna? Soyayya fa shine na kare maki mutuncin ki ba na zubda maki mutunci ba kafin aure, inna gama tattabe ki a waje me na tanadarwa kai na a gidan? In muka gama soyayya a waje in mun je gidan meye sabo da za mu yi dan debewa kan mu kewar shekarun rayuwar mu da zamu yi a tare? Kiyi tinani, ni kam anyaaaa Fateema.... anyaaaaa?"
"Anyaaa me? Nace Anyaaaa me? Kana kokwanto akaina ne? Bari ka ji ita soyayyar nan dana ke fada maka ba fa wai wani iskanci za mu yi ba,kawai dan simba da runguma ne, ka dubi yanda Jameela suke yi ita da Babawo mana abun nasu gwanin sha'awa, ji dan Allah in muka jera da ita qirjin ta taff da dukiyar fulani, amma ni sai kace allo, gaskiya ni baka kyautamin sai da safe, ba zan zauna in sha sanyin banza da sauro ba ban amfana da komai ba sai shegen wa'azi , sai da safe,"
Cikin fushi ta shige gida bazar bazar, da matuqar mamaki Sadeeq yabi bayan ta da kallo, kanshi yayi mugun d'aurewa da abinda ya faru yanzu, sai tunani yake yi anya sanda bai samu zuwa ba ba wasu samarin dake zuwa su lallatse ta kuwa?
" Aiko da sakel, daga yanzu kullum zan dinga zuwa zance dan ba zan bar wasu banzayen su lalata min ita ba tunda ta na so na kamar yanda nake son ta,"
Tina sanda suka fara haɗuwa da ita yayi, a lokacin sun taso daga islamiyya ita da Jameelah, kula da rashin kamun kai irin na Jameela ne ya sanya bai ce ita yake so ba dik kuwa da kyaun da take dashi, amma yanzu Mamalo na so ta goge masa haddar kan shi, k'wafa ya yi sannan ya ce,
"Dik laifin wannan Jameelan ne, dan komai take yi shi Fateemana take son daukewa, zan yi qoqarin raba su kuwa inshaa Allahu dan na more wa soyayya ta cikin tsafta,"
Muryar Mamalo ya ji cike da tsiwa ta na kad'a qugu a saman kan shi ta ce,
"Wai malam baka tafi bane? Ni to ka tashi zan shiga da tabarma ta,"
Tana wani jijjiga, kallon ta yayi yayi murmushi kawai, hannu ya sa a aljihun shi ya na d'akko abinda zai bata, tana ganin haka jijjigar ta koma rausaya,tana wani abu kamar mai jin kunya, kuɗi ya d'akko a aljihun shi dubu ɗaya sabuwa fill ya miqa mata,cikin sauri kamar zata haɗa da hannun shi ta amshe ta hau godiya,
"Dan Allah ki min alqawarin daina kula dik wani saurayi in ba ni ba,"
"In dai kayi alqawarin kawon kalar wannan kullumm ba wani qato da zan dinga kulawa wannan alqawarin mamalo ne, kasan kuwa bana karya alqawari inna dauke shi,"
"Indai wannan ne kin samu, sai da safe abar qauna ta,"
D'aga masa hannu tayi suka yi sallama ta nad'e tabarmar ta, zata shige gida kenan ta kalli dai-dai inda su Jameelah suke a duhun, dariya ta ji suna yi qasa-qasa, hankalin ta ta tattara gaba ɗaya tare da qura ido qurr, Jameela ce kaɗai take iya hangota, Babawo kam bata ga ina yake ba ma a wajen sai dai tabbas ta san su biyu ne a wajen,haka ta dinga gwale ido ko zata iya ganin shi amma bata gan shi ba, a zaton ta ko ya tafi ma, dan haka kawai sai ta ɗauki hanyar yin wajen Jameelan, da sauri Babawo ya miqe daga qasan Jameela daya shige, ita kuma taja skirt ɗin ta ta rufe qafar ta ta na b'ata rai,cikin masifa ta ce wa Mamalo,
"Meye zaki zo ki wani tsaya mana akai,"
"Wayyoo kuyi hakuri dama da ban ga Babawo ba na zaci ya tafi ne, sai da safe a ci soyayya lafiya, na baki labarin gobe,"
Can qasan