Showing 24001 words to 27000 words out of 115850 words

Chapter 9 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

5650

mata da shi ďinne na gaske, ga kuma pictures ďinsa dake kai, da wasu family members.
Dawowa tayi baya ta danna accept sannan ta cigaba da duba profile ďinsa,


Tana Haka massage ya shigo mata,


``` Thanks for accepting my request Kaiyrat```


Yanayin yadda ya rubuta sunanta nata ya kara tabbatar mata da lallai shi ďinne.


```Your welcome```


Ta rubuta masa as reply, tana taunar hakoranta,
Nan take taga Video call. Ya kirata. Tsayawa tayi tana tunani miyasa ya danno mata videocall.? Oh maybe yana son ya tabbatar da idan ita ďince, hakan yasa ta amsa masa kiran.


Dimm! gabanta ya faďi saboda kwarjinin, murmushinsa da kuma yadda kyakkayawar fuskarsa ta cika mata screen ďin computer.

“Kece ko gumkinki.?”


Ganin yadda ta ke kallonsa ba ko motsi. A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta ďan saki murmushi,


“Nice mana kai ma kai ne ko gunkin ka.?”


Dariya yayi,


“Rama wa kikayi.? Ykike ya gida?”


“Lafiya kalau na gode da zuwan da kayi ka bawa Minal hakuri”


Tsoke fuska yayi ya ďan turo hanci gwanin sha'awa,


“Oh never mind Dear it's my pleasure”


“Thanks too”


Ta faďa tana murmushi. Da tunanin abunda zata ce,dan duk ya ďaure mata jiki da sarka da bazan iya cewa ga kalar ta ba!




Shima idon ya tsura mata yana kallon beautifull face nata, da kuma yadda take kunnar kallonsa, duk sai yaji ta kara burgeshi. Wani zillo zuciyarsa take akansa duk da har yanzu bai gama tabbatar da sonta yake ba,
Saidai kuma jinta yake duk ta make ko ina na ilahirin zuciyarsa, dan ta tara komai da yake so a mace. Suturce jiki, tunani, sanin ya kamata ga kuma uwa uba kunya.


“Hy are you still there!”


Ido ya kara sakar mata da murmushin da ke kayar mata da gaba,


“Yes pretty anything for me.?”


Dariya abun ya bata daga ita har shi, basu da wani abun cewa sai magana suke kamar wayanďa aka saka dole,


“Laugh huh? What is funny.?”


“Nothing naga kawai kaki kashe laptop ďin bayan baka da wani abun cewa”


“So glad to know that you’re having fun, especially With me”


“Lol Saif I...-”


Bata karasa maganar ba ta rufe loptop ďin da sauri. Tana kallon Minal data shigo yanzu, tana kallon laptop ďin.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!


NA


KHADEEJA CANDY


Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy




BABI NA GOMA SHA TAKWAS___18




A hankali ta ɗo ta kalli kwayar idonshi, suna haɗa ido gashin jikinta ya tashi, a hankali ta kawarda nata idon tace,


“Saif mi yasa kayi ma Minal haka? Mummy ta faďa min komai ita ma Minal ďin ta faďa min”


Yawu dake bakinsa ya haďe. ita kuma tayi masa kallon jiran amsa.


“Kaiyrat abunda Minal take yayi yawa abun ne ya dame ni shiyasa har nayi unkurin yi mata magana, abunda take ya tsa6a ma addini bata da wta rayuwa sai ta turawa ni kum sam bana jindaďin hakan”


“Saif ba kai kaďai ya dama ba dukan mu ya dame mu badan muna jindaďin abunda take muka saka mata ido ba,sai dan idan akan mata magana ko kuma kayi unkurin chanja mata rayuwa da karfin tuwo zai iya haifar mata da matsala, Saif da ba kai bane babu wadda ya isa ya tsaya gaban Mummy ya faďa ma Minal bakar magana. kai kaďai ka kai ka faďa ma Minal maganar da zata saka ta kuka ta kyale ka”


“Amman kinsan haramun ne a zuba mata ido tana yadda take so ko? kenan koda Sallah tace ba zatayi ba babu wadda zai iya yi mata magana ko?”


“Tana Sallah Saif Minal bata ta6a fashin sallah ba sai dai wani lokacin bata yinta a cikin lokaci duk wani aikin na ibada baya wuce Minal matsalar ta ďaya share share da kuma tufafin da take sakawa sai kuma rayuwar turawa da ta ďauka ta makalawa kanta kuma hkan ba zai rasa nasaba da zaman da tayi can kasashen turawan ba.
Saif idan kana son ka chanja Minal dole ne ka fara nuna mata son duk abunda takeyi kamin ka nuna mata kin shi kai tsaye dole na ka jta jikinka ka nuna mata muhimmanci abunda kake so tayi kamin ka nuna mata illar wadda take yi a yanzu ki tsaye,
zaka iya janta jikinka da kalamai masu daďi da kuma kulawa”


Wani murmushi yayi wadda ya fitar masa da beaut point.


“Taya kike ganin zan iya hawo kan Minal har ta daina abunda take bayan ke da kike da dangantaka da ita baki iya jan hankalinta ta daina?”


“Zata daina Saif just trust me and try zata iya canjawa a kanka bata bata canja a kaina ba saboda ni da kai a kwai babbanci kai Namiji ne ni kuma Mace ce zata iya daina akanka bata daina akaina ba”


“Ban fahimta ba toh miye banbanci n dake a gurinta.?”


“Zaka fahimta nan gaba. na gode da lokacinka da ka bani na barka lafiya”


Tana kaiwai nan ta tashi ta gyara yafin mafinta ta nufi kofa. Shima tashi yayi ya rufa mata baya suka fice tare. a bakin kofa ya tsaya yana kallonta har ta buďe motarta tana kokarin shiga ya kira ta,


“Kaiyrat”


A hankalin ta juyo ta kalleshi. Wani kyakkyawan Murmushi ya sakar mata,


“Thank you”


Itama murmushin ta mayar masa tana kaďa kai,


“Welcom.”


ido ya tsura mata har ta zauna cikin motar, ta saka mata key tayi ribas tabar gidan. sai da mai gadi ya rufe gate ďin sannan ya juyo ya dawo cikin falon.
Huda na ganinsa ta tashi ta nufi Upstairs, shikan bai ma kula da da kishi take ko wani abun ba dan hankalinshi baya gurinta. Kairat yake tunani da kalamanta, shi kan ta burge shi.
_Gaskiya tana da hankali da tunani tunda har ta iya yin wannan maganar da wannan tunanin ai ita ma yar mai kuďin ce amman bata hali irin na minal kuma tayi karatun a waje itama, amman bata ďauki halinsu ba da yake tana da hankali kalli ko shigarta shigar musulmai koda yaushe zaka ganta cikin kamala gata black beauty_

Yana kokarin Zama yake wannan tunanin. (Ni kan nace Saif kodai an kamu🤔)


Huda kan tunda ta shiga ďaki ta kasa zaune ta kasa tsaye, sam hankalinta yake ya kwanta da ganin Kairat ďin da tayi. _toh miye tsakaninsu ? ina yasanta? miyasa yaje da sauri ya tarbeta ? miyasa ya koma can gefe suna magana ? ta lura da irin kallon da yake mata da kuma wadda ita ďin take masa kardai ace sonshi take! shin mima suka tattauna? _
Goshinta take bugu da karfi tana safa da marwa. daker ta samu ta zauna gefen gado still tana tunani.
Kardai ace Saif sonta yake! kai bazai ta6a yiyuwa ba sai dai idan ita ďince take son jan hankalinsa dan ita bata yarda a kwai mace da mijinta zai iya so ba. toh mima ta rasa da har mijinta xai iya hango wata ? amman da yake mata yan iska ne aun iya jan ra'ayin mutun zasu iya bin ko wace hanya ganin sunja hankalin mijin ko dan mulki da kuďi da yake tattare dashi uwa uba kuma ga kyau. kai dole na ta gano abunda yake tsakaninsu dan daga ganin idon wannan Kairat ďin irin gogaggin karuwan nan ne na turai kai zama ba gannin ba dole ne nayi musu tsakani. tun kar tafiya tayi girma.


Tashi tayi zuciyar ta na bugawa da karfi ta nufi hanyar falo.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.


NA


KHADEEJA CANDY


Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy




BABI NA GOMA SHA TARA___19


Zaune ta tararda shi jingine da kujerar, ga duk kan alama tunani yake dan baiji saukowar taba,
Sai kawai ganinta yayi tsaye akan sa tana wani kumburi. Murmushi ya sakar mata ya Hannunta ya rik'a da niyar zaunar da ita, sai kawai ta fisge hannun ta kara haɗe fuska


“Saif wacece wannan.? Mi tazo yi?”


Ya ɗan daɗe yana kallonta kamin ya bata amsa


“Wacece ita ina ganin ita ya kamata kiyi ma wannan tambayar. Mi tazo yi kuma, tazo ne akan maganar Minal”


“Minal”


Gabanta ya faɗi,


“Kamar ya maganar Minal nifa ban gane ba”


“Naje nayi mata magana ne akan yanayin shigar ta da kuma rayuwar turawa da take”


Zama tayi kusa dashi,


“Saif har yanzu baka daina zancen Minal ɗin nan ba ina kace min ba zaka sake kula ta ba?
Mi kuma ya kaika gurinta yanzu Saif yarinya ance ba yarinyar kwarai bace ba shaye-shaye take yi kuma ance bata da Uba kai baka ma jin kunya a ganka da mace irinta.?”


Dariya, “Huddallah kenan toh ai ni sonta nake ba, kuma dan an ganni da ita ai ba wani abun bane tunda mutunci yar uwata kuma musulma.
Faɗa min waya ce miki bata da Uba kuma tana shaye-shaye.?”


“Ina zama na aka zo aka faďa min ai kasan abun duniya baya 6oya”


“Toh duk wadda ya faďa miki karya yake yi bata da Uba aka haifeta! Shaye shaye kuma a da ne tayi yanxu ta daina”


“Kare ta dai kake son yi Saif amman nasan wadda ya faďa min ba xai min karya ba, kuma ni banga abunda ta fini dashi ba da har zai ďauki hankalinka gurinka”




Hannu ya kai ya shafa fuskarta,


“Kina wahalar da kanki Huda, na faďa miki ba son Minal nake ba ni kwata kwata bata cikin tsarin rayuwa ta”


“Amman mi yasa kake kula ta?”


Duk yadda zai mata ba yarda zatayi ba dan yasan halin Huda da naci indai akan kishi ne, amman shi kan har cikin zuciyarsa Minal bata cikin tsarin rayuwarsa, Hancinta ya lakata ya tashi ya Upstairs.


Yana shiga ďaki ya cire kayan dake jikinsa ya ďaura dan karamin tawul ya shiga badroom,


Koda ya fito jikinsa da sanyi da alama wanka yayi, a gaggauce ya shirya cikin kananan kaya black jean da farar T-shirt, ya feshe jikinsa da turare, sannan ya ďauki Atm ďinsa da makullin mota ya fice.

Har lokacin Hud na zaune inda ya barta tana tunane-tunane, sam zuciyarta taki yarda da Saif ba son Minal yake ba, indai har da gaske ba sonta yake ba toh ina ruwansa da duk wata rayuwa da zata shiga.
Tana wannan tunanin ya sauko downstairs, kallo ďaya yayi mata ya ďauke kai yana murmushi, yasan har yanzu abun ne take tunani ganin yadda tayi nikin nikin da fuska babu Annuri. Baice da ita komai ba ya nufi kofar fita, itama bata ce dashi ba dan haushin sa ne ya karu ganin yadda ya ďauki wanka zai fita, har ya fice kallonsa take zuciyarta na raya mata can zaije.


Sai da taji tashin motarsa sannan ta nufi harabar gidan tana kwalama masu gadi kira, jiki na rawa suka iso suna mata gaisuwar girmamawa,
Bata amsa musu ba ta hau su da masifa.


“Wai miye aikin ku a gidan nn ba gadi ba kuna me wannan yar iskar yarinyar ta shigo min har cikin gida?”


“Hajiya tace ita yar Ibrahim Ahlam ce shiyasa muka barta ta shigo”


D'aya daga cikinsu ne ya bata amsa,


“Ina ruwana da waye ubanta nan gidana ne ba nata ba karku sake bari wata mace ta shigo min cikin gida ba tare da izinina ba duk kuka sake haka wallahi ba kin aikin ku”


Hakuri suka rika bata, ita kuma sai wani kumburi take bata sake ce musu wani abun ba ta juya ta koma cike da gadara.


**** **** ****
A hankali taji ana buga kofar falon, tashi tayi ta nufi kofar tana tambayar waye, Ba a bata amsa ba har ta buďe kofar.
Murmushi ya sakar mata


“Kaiyrat”


“Na'am Saif”


Ita ta mayar masa da murmushin tana kara wangale kofar.


“Shigo mana Saif a gidan ba bakinka bane”
Bai shigo ba sai kawai yasa hannayensa aljihu ya sakar mata ido har sai da idanuwansu sukayi taraiya, da sauri ta sauke nata idon cike da kunya ta ɗanja baya.
Hakan da tayi sai ta burgeshi dan shikan yana son mace da kunya da kuma kamun kai, Murmushin dake fuskarsa ne ya faɗaɗa.


“A'a bazan shigo ba har sai Qawarki tayi min izini”


“Yar'uwarta zaka ce ba qawata ba tana can Garden zaune”


Ta karasa maganar tana nuna masa hanyar Garɗen ɗin, Girarsa ya haɗe akamar tambaya,


“So.?”


“Sai kaje ka bata hakuri”


Kai ya kaɗa, ya ɗga daga jikin kofar ya nufi hanyar Garɗen.Tsaye tayi tana kare masa kallo, ita kan raywarsa tana bugerta bai ɗauki kansa wani ba, kuɗi dake tare dashi basu rufe masa ido ya wulakanta kowa ba, rayuwarsa so simple gashi kyakkyawa. Ya iya zama da kowa,
Sai da ta daina hango shi sannan ta rufe kofar falon tana sauke ajiyar zuciya.




Zaune take saman doguwar kujera tana rubuce-rubuce da biro kamar wata karamar yarinya sai yage takarda take tana zubarwa,
Dariyar da taji anyi yasa ta ɗago kai ta kalli gurin da Saif yake tsaye, Kara haɗe fuska tayi ta mayarda kanta gurin rubutun da take, wai ita ala dole tana fushi,
Karawo yayi kusa da ita da fuskar zolaya,


“Har yanxu baki hakura ba kenan yanxu daga faɗar gaskiya shi kenan na zama mai laifi.?”


Bata ce dashi komai ba sai rubutunta take kamar ma bata san dashi a gurin ba, ganin hakan yasa ya fisge biron dake hannunta ya jefar,


“Zuwan nan da nayi dan ki kawai nayi shi Minal nasan na ɓata miki rai but am sorry bazan sake ba”


Tashi tayi tsaye ba tare data kalleshi ba tace,


“Na hakura”


Sai ta juya da nufin tafiya,Da sauri ya riko ta ya juyo da ita.


“Wanna hakurin ai na dole ne”


Sai a lokacin ta ɗan kallesa ta ɗauke ido,


“Toh mi kake son nace maka?


“Ba wani abun nake son kice min ba kawai hakuri nake son gani a fuskarki, Minalina son ki fahimci wani abu. duk abunda nayi miki nayi ne dan ina kishinki Minal ina bakin cikin yadda kike sakin surar jikinki ga mazan da ba muharramanki na suna kallonki, Minal bana son yadda kike kwaikwayar rayuwar turawa fan abanga abun burgewa a rayuwarsu ba Kishinki ne kai ni ga furta miki kalmomin da suka ɓata miki rai, ina fatar zaki min uzuri ki fahimce ni yanzu”


Shiru tayi kamar mai nazari, Ganin hakan yasa ya riko hannayenta yana kallon fuskarta dan ta tabbatar da gaskiyar maganar sa.
Har cikin birnin zuciyarta taji sanyin tafukan hannayensa, Nan take kanshin turarensa ya shiga kai ma hancinta hari. Bata an karaba taji faɗuwar gaba sakamakon haɗa ido da tayi dashi. Cikin taku ta kawarda nata idon, da murya mai kamar kuka kamar shagwaɓa tace,


“Amman Saif miyasa kace tirrrr dani? wanna kalamar ita tafi min zafi kuma na kasa gane dalilin furta min ita da kayi Miyasa ba zaka fahimci halin da nake ciki ba?”
Idonta cike da ruwan hawaye ta karasa maganar, fuskarta na kallon gefe. Bakimsa ya cika ma iska, dan yasan duk yadda yake son ta fahimta ba fahimta zatayi ba. Hannu ya kai ya shafa gashin kanta, yaja zuwa kirjinsa ya rugumta.


“Kiyi hakuri Minal nayi miki alkawarin bazan sake ba”


Kara kamkamesa tayi ta lumshe ido tana shakar daɗadɗen kanshin dake tashi daga jikinsa, Ta hakan ya gane ta hakura daman yasan idan ba hakan yayi mata ba, baxata hakura ba.
Jikinsa ne ya bashi ana kallonsa. hakan yasa ya ɗago kai ya kalli windon dake fuskantarsu, Kairat ce tsaye jikin windo tana kallonsu fuskarta ɗauke da murmushi.
Daga inda yake tsaye ya aika mata da sakon lafiyayyen murmushi wadda zan iya cewa har cikin zuyarsa yake.
Ita kuma ta ɗago masa babban yatsanta alamar well done tana murmushi, sannan taja windon ta rufe zuciyarta a rike. Jinginawa tayi jikin windo gumɗe da baki.
Can kuma naga ta rumtse ido ta sulale kasa zaune, tana girgiza kai kamar mai magana da wani.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.


NA


KHADEEJA CANDY


Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy




BABI NA GOMA ASHIRIN DA D'AYA__21




“Miyasa kika rufe laptop ɗin.?”


“Ba komai na gama abinda zanyi ne ya akayi.?”


“Ba komai Mummy tace na tambaye ki ina kika je min Sarka.?”


Kairat ta tashi tsaye,


“A'a ba wani sarkanki ni tace ta siyo ma”


“A'a-a'a tace ni ta siyo ma ke sai ta sake zuwa”


“Dan can ji kanta aje a tambayi mummy ďin”


“Ae aje ďin”


Da gudu Minal ta fice tana arigaggan zuwa gurin mummy, Ta riga Kairat isa ďakin sai ta rika yima mummy wink da ido.


“Mummy bani kika siyo ma wannan Sarkar ba.?”


Murmuahi Mummy tayi dai-dai lokacin da Kairat ta shigo ďakin tace,


“A a Kairat na siya ma ke nace sai wani satin”


Dariya Kairat tayi mata tana mata gwalo,


“Allah na gode maka yarinya kinji kunya”


Kukan shagwa6a Minal tasa,


“Gaskiya ni mummy kina gwada min banbanci Ni barin gidan ma zanyi”


“Sai kin dawo Allah ya kiyaye Hanya”


Mummy ta faďa da fuskar zolaya tana murmushi,


Tashi tayi ta bar d'akin tana hararar Kairat, Nan Kairat ta rufa mata baya tana zolayarta,




BAYAN AWA D'AYA.......


Duk zaune suke falo suna fira suna cin Tofin da Talatu tayi musu, Kairat sai santi take wai ya ake yinsa. Duk dariya suka sama, har Mummy Minal tace


“Da madara ake yinshi”


“Dan can ji kanta kena tambaya ne sai kace iyawa tayi”


“Wallahi Mummy ta daina ce min aji kaina kona mata ďan banzan duka”


Tashi mummy tayi,


“Idan ba gurin na bar muku ba ba zaku barni na huta ba kullum faďa kuke kamar kananan yara”


“Ai itace ta fara jana”


Minal ta faďa tana hararta, Kairat taja tsaki


“Ji kanta dana jaki saina kaiki ina?”


“Kinji ko mummy baza ta daina ba”


Mummy dai bata sake ce musu komai ba da nufi ďakinta, Haushin hakan yasa Minal ta ďauki Filo ta jefe Kairat dashi, Nan Kairat ta sake ce mata


“Dan Allah can ji kanta an faďa ance ji kanta”


Banza tayi da ita ta cigaba da matsar rimot tana cin tofin,


“Idan kinji ma na sake miki magana kice min ba Minal ba”


Dariya Kairat tayi zatayi magana, Jafar ya turo kofar falon ya shigo da sallama,


“Amin wa alaikassalam”


Talatu ta amsa masa, sai da ya gaidasu sannan yace


“Wai Saif yace a kira masa Kairat”


Dimmm gaban Minal da Kairat ya faďi, suka haďa ido kamin daga bisani Minal.ta janye nata,


“Kodai Minal yace.?”


Kairat ta tambaya,


“A'a kedai yace a kira masa yana nan waje”


Rasa tayi abunda zata ce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login