Showing 99001 words to 102000 words out of 115850 words

Chapter 34 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

5652

ɗora cup da plate ɗin sama sannan ta kalleshi.


“Ka fara shan tea sai kaci fruits ɗin zaka fi jindaɗi idan baka ci abu mai nauyi ba”


Murmushi yayi mata as respon ya ɗauki tea ya fara sha, kallonsa take a sake tana karantar wasu abubuwan game da shi. Daga shigowarsa zuwa yanzu ta fahimci yana cikin damuwa, sai kuma ta samu kanta da jin ba daɗi ganin halin da yake ciki, yanayin yadda yake shan tea sai ya saka ga ganin kamar baya jindaɗi sa, ba kuma daɗin sa ne baya jin ba tun da tasan mijinta ma'aboci shan tea ne da kuma coffee akwai dai abunda ya ɓata masa rai. Bayan ya shanye tea ɗin ta karɓi kofin tana faɗin


“Faɗa min yau da ina da ina kaje bayan gidan Momy?”


“Ban je ko ina ba a gidan kawai na wuni, Na manta ban tambaye ko yadda Mummy tayi da Mutumen ta ba”


“Zan faɗa maka gobe yanzu faɗa min abunda yake damun ka”


“Ni..?”


Ya ɗan zaro ido sai kuma yayi murmushi ya cigaba da cin Apple ɗin dake gaban sa, nan tasa hannu ta ɗauke plate ɗin fuskarta babu alamun wasa tace


“Faɗa min abunda yake damun ka Saif Please”


“Ya kamata sunana ya canja launi a bakin ki fa yanzu”


Ya faɗa yana son basar da wacan tambayar. Murmushi mai sauti


“Toh wane suna kake so?”


“Ke ce zaki sa min da kanki”


“Fine Abbah lil Minal”


Dariya yayi


“Sunan yayi tsawo kuma bai min ba”


“Toh faɗa min sunan da kake so mana”


“Ba xan faɗa ba kece dai zaki zaɓa min”


“Hubby”


Kai ya girgiza,


“honey”


“Nop”


Shiru tayi tana nazari dan duk sunan da ta kawo masa cewa yake a a, can ta kalleshi


“K'albee yayi maka?”


Kai ya ɗaga mata cike da jindaɗi ya janyo ta zuwa jikinsa ya rungume,


“Zan ji daɗi idan kika kira ni haka”


Murmushi tayi


“Haka zan rika kiran ka har sai kace na daina”


“Aiko ba rana”


Ya faɗa da dariya, yana ɗan shafa bayanta shiru ne ya biyo baya shi dai yana abunda yake ita kuma tana saurare sa kamar ɗalibar da ake yima darasi, ta natsu sosai tana saurarensa, har sai da taga yayi nisa sannan ta kira sunan sa a hankali


“K'albee......”


Kamar ba zai amsa ba zuwa can kuma ya amsa mata a wahale can cikin makon shin shi


“Umhm”


“Faɗa min mi yake damun ka?”


Bai yi magana ba sai kawai dai cigaba yake da abunda yake mata, ganin hakan yasa ta janye jikinta ta matsa gefe tana gyara rigarta tana ganin ya matso sai ta kara matsawa,


“Dan Allah karki min haka Kairat yana ɗaya daga cikin abunda yake sani damuwa ki daina hana min abunda Allah ya halitta min wallahi wahala nake”


Cikin walallaliyar murya yayi maganar idonsa a rine.
Ita kanta da san da hakan dan tana lura da irin halin da yake shiga idan suka kwana tare, tsayawa tayi kamar mai tunani tana haka taji ya rika ta bata unkurin hana shi ba, ya ci gaba da abunda yake mata ita kuma tayi shiru tana sauraren karatun nasa, ganin ya wuce gona da iri yasa ta rik'a kokarin kwace kanta a nan ya nuna mata karfi ba ɗaya ba, kiransa ta rika yi amman ina yayi kisa baya jin kira. Rawa jikinta yake ta ko ina kan kace kabo sai gata tana kuka da hawayen ta.
Daren ranar daga ita har shi basu yi bachi mai tsawo ba balle ita da sam bachin bai mata daɗi ba. Washe gari shi ya taimaka mata tayi wanka tare da alwala ya shinfiɗa carpet tayi Sallah, tana sallamewa ko addu'a bata tsaya yi ba ta kwanta a gurin sai bachi.


Bayan ya gama haɗa breakfast ya shigo ɗakin tsaye yayi kanta tana kallonta fuskarta ciki da annuri sai murmushi yake, can kuma risina ya kai hannu ya shafa fuskarta. Juya tayi ta ci gaba da bachin, murmushi yayi bai yi unkurin tashin ta ba ya juya gurin Lil Minal yasa hannu ya ɗauke ta ya fice.
Sai sha ɗaya har da kwata ta farka koshi ba dan ta gaji da bachin ba sai dan yunwa da ta tashe ta. Ba dan dole ba da ba zata fita daga ɗakin ba, sai dai kuma babu yadda ta iya tun da ba kiransa zatayi ba, daker ta tashi tsaye ta nufi kofar ɗakin tana wata tafiya. Yau kan sai taji sauka stairs yayi mata wahala kamar ba kowace ta saba ba,
Saman kujera ta gansa zaune rike da lil Minal yana ɗaukar ta hoto, har kasa ta duka ta gaishe shi cike da kunya


“Ina kwana”


Bai amsa ba sai kawai yasa ɗayan hannunsa ya rika.ta suka tashi tsaye tare,


"Sai yanzu kika tashi"


Ya faɗa kamar mai raɗa kai kawai ta daga masa tana kokarin zame jikinta, lil Minal ya aje yasa hannyensa ya zagaye kugumta yana murmushi


"Dan Allah ka sake ni yunwa nake ji"


Bai yarda ya sake ta ba ɗin sai ya ɗauke ta cak ya nufi gurin cin abincin da ita. sai da ya tabbatar da ta koshi sannan ya zuba ya ci kaɗan ya sake ɗauko ta a dawo da ita saman kujera ya rumgume ta yana sauke ajiyar zuciya.

“I'm not baby dan Allah ka kyale ni”


“of course you are”


Duk yadda taso ya sake ta kiyawa yayi har sai da tayi kamar zata masa kuka sannan ya sake ta ta tashi da sauri ta nufi ɗakinta.
Wanka ne kawai ya zame mata dole tana yinsa ta ɗauko lil Minal ta bata nono sai da ta tabbatar ta koshi sannan ya kwatar da ita gabanta ita ma ta kwanta sai bachi.


Da dare takeaway yayi masu dan wuni tayi tana bachi shi kuma yana ganin tayi bachin ya sa kafa ya fita bai dawo ba sai bayan Sallah isha i,
Bayan ya shiga ɗakinsa yayi wanka ya dauko abinci ya nufo ɗakinta a bakin kofa ya tsaya ya sauke ajiyar xuciya sannan ya shiga da sallama,
Duk yadda yaso ya ɓoye damuwarsa dai ta gano dan idonsa take karantar halin da yake ciki ita kaɗai ta ci abincin sho bai ciba sai saka da yayi gaba yana kallo kamar tv,
Bayan ta kare cin abincin ya janye abubuwan dake gabanta ya matso kusa da ita ya rumgume ta, a nan ta kara fahimtar halin da yake ciki.

Haka suka kwashe kwana biyu ita da shi, ita ta kasa ta tambayeshi damuwarsa shi kuma ya kasa faɗa mata, sai dai kuma duk tsawon kwana biyu nan bai barta ta huta ba, kullum da salon da yake zo mata.
Yau ma bayan sun gama breakfast ya tashi kamar jiya ya nufi ɗakinsa, har yayi abunda zaiyi ya fito tana zaune a inda ya barta ganin yanayin shigarsa ya tabbatar mata da fita zaiyi. sai da ya kawo bakinsa daidai kumatunta zai mata kiss tayi saurin jayewa ya sake dawowa ɗayan gefen ta sake kauda fuskarta,


“Lafiya?”


Ya tambaya yana fuskantar ta, kallonsa tayi


“Bai kamata ace kana ɓoye min damuwar ka ba a tunani na yanzu ni da kai mun zama ɗaya”


shiru yayi sai kuma yaja kujera ya xauna ya kama hannunta,


“Matsalar Safiyyah ce take damu na saboda Momy da Gwaggo sun ce nine silar shigarta wannan halin hakan yasa yanzu Daddy shi ma ya kasa fahimta na”


Tasan me yake nufi tun da ta daɗe da sanin babu wanda Safiyyah take kauna irin Mijinta. sai dai kuma me su suke nufi har ya kai suna ganin laifinsa? ko aurenta suke so yayi? dan ta samu wannan amsar yasa tayi masa wata maganar.


“Toh ka aure mata sai ka wanke kanka”


Rumgume yayi yana dariya


“Funny girl ina ni ina Safiyyah bana mata kallon matar da zan iya aure ba zan iya zaman aure da Safiyyah ba sai dai kuma nima kai na tana bani tausayi sosai”


Wani sanyi taji ya tsara zuciyarta kara lafewa tayi jikinsa,


“To yanzu ya zakayi?”


“Oho gani ga Allah ni dai fata na kawai ta samu lafiya”


“Toh miyasa ba zaku sata under medication ba?”


“Gwaggo ce bata yarda ba wai kara firgita mata kwakwalwa za'ayi sai dai a nema mata na hausa”


“Ka barta ta nema mata na hausan wata kila a dace”


Sun daɗe a haka manne da junna sannan ya sake ta ya fice.



*** *** ****



Abu kamar wasa sai ga Safiyyah ta kwashe wata biyar da wannan lalurar tun ana ganin kamar sauki sauki yanzu abun ya fara wuce gona da iri, kuma duk da hakan Gwaggo taki yarda a kaita wajen maganin turawan ma sai an saci idonta ake bata,
Sannu sannu ake sabo yanzu kan Kairat ta san kan gidanta da kuma mijinta, ga kula da lil Minal da take sosai da sosai itama yanzu tayi kyau tayi wayo dan yanzu tana cikin wata na bakwai, in ka ganta kamar ka sace ka gudu.





Tana cikin kicin tana aiki taji an danna bell lil minal kuma ta kwala ihu saboda tsoro, da gudu ta fito tazo ta ɗauke ta,


“Ya akayi mi ya faru?”


Shiru tayi ta kalli kofar falo jin an sake danna bell ɗin, ɗauke da ita taje ta buɗe kofar, Da sauri ta rumgume Mummy ta welcomin ɗin ta.

“Ashe ma kinji sauki ce min akayi ɓaki da lafiya”


Mummy ta faɗa tana kunno kai cikin parlour,


“Naji sauki Mummy waya faɗa miki?”


“A shanun talla naji ina mai gidan naki?”


“Ya fita tun ɗazu Mummy ina Abbah na”


“Abbah ki? ai kinsan inda yake”


Murmushi tayi


“Haba Mummy ya kamata ace kun wuce wannan gurin tuni tun yaushe ake abu ɗaya dan Allah! haba Mummy ki amince masa mana Mummy yanzu ko dan karamcin da Abbah yayi miki ba zaki yarda ki aure shi ba”


“Yayi min ne saboda Allah dan Allah ki rufe min baki ko ruwa baki kawo min ba zaka ɗauko min wani shirme”


“Haba Mummy Abbah fa ko ke ko bake ba ya riga ya shirya aure a yanzu da aje a ɗauko mana wanda bamu sam halinta ba fa ao kara ke kuma kinga Hajiya ma da kanta ta roke ki miyasa kike son watsa musu kasa a ido ne? wallahi mummy sam bana jindaɗi in kina cewa Dr. Isma'il zaki aura ko dai dan yafi Abbah kuruciya ne?”


Mummy ta zaro ido


“Kairat zaki tashi ki kawo min ruwa ko sai na bar miki gidan ki?”


Tashi tayi tana dariya ta mika mata lil minal ta shiga kicin ta ɗauko mata drinks da yan kayan ciye ciye ta dire mata.
Sunyi kusan awa biyu suna fira, Mummy na batun tashi Saif ya shigo, yaji daɗin ganinta sosai dan rabonta da gidan har ya manta duk rashin lafiyar da Kairat take yi bata leko gidan ba har taji sauki, Cikin mutumci da girmamawa suka gaisa Mummy take tambayarsa ya mai jiki


“Jiki da sauki”


“Ta warke kuwa?”


“Aa har yanzu tana nan abunda dai sai dai hamdala”


“Allah ya sauwake amman da kun gwaɗa gurin Deen ko Allah zai sa a dace”


Kairat ta mere baki


“Wallahi Mummy nayi ta masa magana yaki yarda shi har yanzu yaki ya manta abunda ya faru”


Mummy ta kalleshi,


“Saif ba a son musulmi da riko, ka amanta abunda ya faru kuma ai ba wani abun zaka je nema ba sai lafiyar yar'uwarka kuma ba kyauta zai maka ba”


Kasa kasa ya watsa ma Kairat harara,


“Shi kenan Mummy zan gwada insha Allah”


“Toh Allah ya sa a dace ni kan bari na tashi kar baki da zanyi suzo ba su tararda ni ba”


Sallama tayi ma Saif, Kairat kuma ta rakata har gurin mota tana mata maganar Abbah ta, Mummy dai bata ce masa uffan ba taja motar ta ta rufe.




YAU MA SAI NACE VOTING AND COMMENTING?




55


Sai da taga ɓacewar Motar Mummy sannan ta juyo, tana shigowa Saif ya cafkota ya wani walkato ta ta juya ta juyo ta faɗo korjinsa, hannunta ya ɗan matse fuskarsa na kan kafaɗarta yayi mata magana kamar mai raɗa


“Wa yace ki daɗe?”


“Ba kowa ba”


Ta faɗa da dariya tana son kwace hannunta dan taji zafin rikon da yayi mata, shi kuma yaki sakinta sai kanshin turaren wuyanta yake shaka, suna haka Lil Minal ta rarrafo tazo ta kama kafan babanta hakan yasa ya saki Gimbiyar ya ɗauki yarsa yana murmushi, dariya tayi ta rika zallo Kairat kuma ta nufi kicin tana ɗan turo masa baki.


Bayan sun gama cin abincin dare Kairat take kara masa maganar Safiyyah, ta damu da ita a yanzu tsaɓanin baya da ba ruwanta da ciwonta ko dan yanzu taga abun yana damun Momy da Saif ne oho! Ita kanta Safiyyah yanzu ta zama abar tausayi bata magana kuma komai bata iyawa sai idan gwaggo ce tayi mata ko kuma yar aikin da ka ɗaukar mata, wani. Lokacin kuma bata komai saikin kuka, ga magani anyi nema har an gaji har yanzu shiru. Kansa ya shafa ya ɗan gunɗe baki


“You know how much I hate him”


War tayi da ido


“Oh my dear, kar wannan ya dame ka ai ba cewa nayi ka so shi ba lafiyar Safiyyah zaka nema ba wani abun ba ko dan Gwaggo da Momy and Kalbi babu abunda zai iya mana yanzu abunda yayi maka a baya zafin son ta yasa yayi maka haka tun da yana tunani zaka iya sakinta shi ya aure,


Kuma abunda ya faru a baya ai ya zame maka darasi yanzu wani ba zai kawo maka wani abun ka rufe idonka ka cutar da kanka ba”


Iskar bakinsa ya busar


“Fine amman shine zai zo ya same ni a nan”


Dariya tayi


“Haba dai wanda keso ba shi ke biya kuma wallahi kasan Deen ba xai kawo kansa gidan nan dan matsalar Safiyyah ba, karka manta yanzo ka hana n ganshi kuma ni yanzu ko number sa bana da”


“Me kike Nufi ke nan mune zamuje?”


“Idan mun je ai ba yada kai bane, kuma ka samu Momy ku tattauna”


Tashi yayi ya rika hannunta,


“Mu rufe babi wasu muyi na mu babin zo muje mu kwanta”


Tashi tayi tana wani irin yauki da jiki ta ɗora kan ta saman kafaɗarsa, hannunsa sarke da nata suka nufi upstairs.



Washe gari bayan ya tashi daga aiki ya biya gurin Momy, sai da yayi kamar yana yi sannan Momy ta sake dashi, dan fushi take dashi wai yau kusan kwana nawa bai leko gidan ba, shi dai hak'uri kawai yake bata yana dariya yasan ba dan komai bane sai dan Safiyyah zata ce ya daina kula da ita ne,


“Ya mai jikin?”


Ya tambaya yana kallon yadda zata amsa masa,


“Jiki yana nan yadda yake jiya Gwaggon ku tazo ta ɗauke ta wai zata kai ta wani gurin a gwada a gani”


“Wai ita bata gajiya da na hausar nn ne, ni da har nace ko mu kai ta gurin wani mai kula da masu irin ciwon mu gani”


“Toh ni ai lamarin ne yanzu na rasa gane ma kansa kullum abu ɗaya”


“Jarrabawa ce idan Allah ya kawo ma bawa sai hak'uri”


“Sai ka bari idan sun dawo sai muje gurin da kace ɗin Ya Kairat da lafiyar jiki?”


“Taji sauki sosai yanzu ai”


“Allah ya kara sauki amman nace Ba zata yaye Lil Minal ba? Kar tazo tasha ciki abu ya zama biyu gata tayi jikinta”


“Toh wai Momy Lil Minal bata saba da shan komai ba banda nono kuma kinga cikin ai wata huɗu ne yanzu kin ga akwai sauran lokaci”


“Aifa sai ka yi, wato har yanzu baku fara bata komai ba ko! Ko yar madarar nan ta yara ai kwai saba mata da ita”


“Za a bata”


Ya faɗa yana ɗan sosa kai, Momy ta taɓe baki


“ku dai kuka sani, idan ba a sharar masallaci ba ayi ta kasuwa”


Shi dai dariya kawai yake. Sai kusan la'asar ya bar gidan, Yana ɗaukar hanyar gidansa gabansa ya soma faɗuwa, sai jikinsa yayi masa ba daɗi cikin wani yanayi ya isa gidan, bayan yayi parking ma sai da ya ɗan daɗe cikin motar sannan ya fito ya nufo cikin gidan,


Da sallama ya shigo jin ba'a amsa masa ba yasa ya zauna saman kujera yana


“Mom Lil Minal I'm back”


Shiru nan ya tashi ya leka kicin bai ganta ba, kai tsaye ɗakinta ya nufa yana tura kofar ɗakin da faɗin


“Madam ko bachi kike ne?”


Nan ma ba kowa a ɗakin sai Lil Minal dake bachi tana sauke ajiyar zuciya, da ala kuka tayi har ta gaji bachin ya ɗauke ta, bathroom ya buɗe nan ma bata ciki a nan ne hankalin sa ya fara tashi


_Toh ina ta shiga.?_


Ita ce tambayar da yayi ma kansa, a nan ya juya ya shiga ɗakinsa nan ma bata nan cikin sauri ya dawo parlour yana tunanin gurin da zata shiga ya dai san bata fita bata faɗa masa ba to ina ta shiga?, gurin mai gadi ya nufa yana tambayarsa, nan shima yace shi dai bai ga fitar ta ba, dawowa yayi cikin parlour ya danna mata kira sai kawai yaga wayar saman kujera tana ringing, ɗaukar wayar yayi yana dubawa can kuma ya aje ya nufi hanyar da zata sada shi da Garden,


Kwance ya hango ta kasa dafe da ciki, cikin sauri ya k'arasa yana kiran sunan ta, durkusawa yayi yana girgiza ta ganin bata motsa ba yasa ya ɗago ta ta ɗora ta saman kafafunsa,


“Lafiya mi ya same ki?”


Cikin firgice ya tambaya, hawaye ne yake mata zuba bata iya magana sai cikin da ta sa hannu ta dafe, hannu yasa gurin cikin yana dubawa


“Miya faru ciwo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login