Showing 51001 words to 54000 words out of 115850 words
Chapter 18 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
ta amsa da ‘Amin’
*** *** ***
Jingine da Mota Nasir ya tararda Saif ya kifa kai idonshi a rufe kamar marar lafiya,
Dafashi Nasir yayi cike da tausayawa,
“Saif ka daina damun kanka da yawa you are too young for that bai kamata a'ce kana samun matsalan iyali a yanzu ba”
Juyowa yayi yana sauke ajiyar zuciya ya kalli Nasir
“Nasir na rasa meke faruwa da ni al a murran nan suna kokarin rikata ni”
“Saif kar maganar Safiyyah ta shiga kanka ni gaskiya ban yarda Minal ta aikata abunda kake zaton ta dashi ba wannan cikin naka ne Saif”
Fuskarsa ya shafa
“Nasir da ace ba ni na gani da kai na da zan iya yarda kazafi akayi mata, kuma da ace ba Deen bane nan ma zan iya mata uzuri amman kasan yadda take son Deen”
Nasir ya tattara girarsa,
“Ka yarda kenan ba kicin ka ba ne? Baka kusan ceta ba ko?”
Wata bazawarar dariya yayi yana gyara tsayuwarsa yace
“Taya za a kaiwa namiji lafiyayye mace kyakkyawa kamar Minal ya kwana ɗaki ɗaya da ita gado ɗaya yace babu abunda ya shiga tsakanin su! A kasan ba zai yiyu ba, A washe garin daren da mukayi first night na kamata da Deen and you know what she's virgin”
Ya faɗa yana kallon shi, Nasir ya taɓa hannunshi
“Good wannan kawai bai isa ya karantar da kai Minal bata aikata ba, karka manta Saif Deen fa gani nake kamar yana sonta zai iya yi mata haka ko dan ya ɓata tsakanin ku”
“Yes Saif ina wannan tunanin but abunda yake ban mamaki shine taya akayi ya kai har cikin ɗakinta bata sani ba kasan ba zai yiyu ba kuma ita da kanta ta amsa ƙlaifinta after that, chat ɗin da suka yi kasan babu mai ɗaukar mata waya ya haɗa mata wannan ko?”
Shiru Nasir yayi dan bashi da abun cewa a wannan gurin, lallai ko kotu akaje yasan Minal bata da mafitar wannan shima kanshi yana mamakin yadda hakan ya faru, sai dai shi bai yarda wani abun ya shiga tsakanin su ba, sai dai zai iya yarda ita ɗince tace yazo, toh kuma chat ɗin da sukayi kayi fa! Oh Allah,
Ya dafe kanshi yana sauke ajiyar zuciya,
“Wai toh ya a kayi kaga chat ɗin da sukayi?”
“Safiyyah ce ta faɗa min”
“Safiyyah?”
Ya karɓa sunan da karfi fuskarsa kuma cike da mamaki,
“Toh taya akayi Safiyyah tasan abunda yake cikin wayar?”
Kafaɗunsa ya ɗaga
“I dont know kasan mata suna share ɗin phones ɗinsu, ni dai ba ma wannan ba i need to Minal ya aza ayi?”
“Tana success special hospital ICU unit 4 but amman maganar nan abun dubawa ce Saif i doubt yadda tasan chat ďin”
Saif bai sake ce masa komai ba dan shi hankalinshi bai bashi abunda ya ba Nasir ba, buɗe motarsa yayi ya shiga,
“Bari naje na ganta i can't wait to see her”
Kai kawai ya ɗaga mashi yana kallon motarshi har ya fice,
****************
Safiyyah tun da ta shiga ɗakin yake safa da marwa zufa na karyo mata, daga bisani ta figi gyalenta da makullin mota ta nufi parking space,
Kai tsaye gidan Huda ta nufo, bako sallama ta shigo parlour, kallo ɗaya Huda tayi mata itama hankalinta ya tashi ganin damuwa karar a fuskarta dan tasan duk abunda ya samu Safiyyah ya same ta,
“Lafiya Safiyyah me ya faru?”
Hannayenta ta rika suka zauna,
“Ba lafiya ba Huda Minal na ciki na wata uku kuma kinsan na Saif ne!”
Ihu Huda tayi da ɗora hannu saman kai ta fashe da kuka
“Na shiga uku na lalace taya hakan ta faru ? Wayyo ni Allah na”
Safiyyah ta daga ta,
“Babu lokacin wannan Huda mafita ya kamata mu nema saboda Saif bai gama yarda cikinsa bane Momi ma haka kamata yayi mu samu mafitar zubar da cikin, kinga kamin a ankaro cikin ya riga ya zube”
Sai a lokacin hankalinta ya ɗan kwanta,
“Kin kawo shawara toh yanzu ya zamuyi ina Minal ɗin take?”
“Tana asibiti jiya a ka kwantar da ita”
“Toh yanzu miye abun yi?”
Huda ta tambaya,
“Tunani nake yi ko zamu je asibitin ne mu samu wani likita yayi mata allurar zubar da ciki sai mu biyashi”
“Kina ganin hakan zai yiyu ?”
“Zai yiyu mana kuɗi miye basa sawa sai idan mutun baya dasu”
“Wace asibitin take ne? Akwai wata aminiyata babbar likita ce nasan zata iya taimaka mana”
“Walkan kinga ta kwana gidan sauki kenan, a Success Special hospital aka kaita”
“Wallahi can kawar tawa ke aiki amman wannan abun yayi daɗi”
Huda ta faɗa tana dariya, wani ihun daɗi Safiyyah tayi har da buga kafa
“Wayyo daɗi”
Tuno Saif yasa ta rufe baki,
“Inji Yaya baya nan dai?”
“Baya nan ke kuwa a da bazan bari muyi maganar nan a parlour ba”
“Toh kinsan yanzu yadda za'ayi tashi zakiyi muje gidan su likinta mu yi mata magana muji yadda za ayi”
“Toh bari na kira ta naji ko tana gida”
Tashi Huda tayi ta nufi ɗaki.
Bata jima ba ta fito sanye da Hijab tana faɗin
“Tashi muje tace tana gida amman anjima kaɗan zata je aiki”
Tashi Safiyyah tayi cike da jinda ɗi ta suka fice,
*** ***
A hankali taji ana taɓa mata fuska ana shafa kanta zuwa wuyanta, numfashi ta sauke a hankali ta kara karkaro kanta ta dan taji daɗin yadda ake shafa ta ɗin duk da bata san waye ba,
Kanshin turaren da taji yasa tayi saurin buɗe ido, kan fuskar Saif ta saukar da su yana mata murmushi,
“Kamar Saif....”
Ta faɗa tana maida idon nata a lumshe, dan gani take gizo idonta yake mata saboda da famarkin shi da take,
Jin an taɓa mata ciki yasa ta kara buɗe idon, dirr kuma ta sake sauke su akan fuskarsa, yanzu kan ba gizo idonta ke mata ba, Saif ne ganin hawayen dake kwance cikin idonsa, hannu tasa ta ture masa hannu sai ta rike mata hannun gam yana hawaye,
“Minal.....”
Sai kuma yayi shiru ya kasa magana, toh me zai ce mata? Cikinsa ne ko ba nashi ba bashi da tabbaci bai kuma kamata ya bata hakuri ba tunda ita tayi masa laifi kuma in har da gaske ne shi ba zai iya zama da ita ba.
Yana wannan tunanin yaji tana kokarin kwatar hannunta, a nan ya sakar mata hannun ya kalleta kamar zaiyi magana sai ta rigashi,
“Please Saif i need to be alone”
Hannu yasa ya share hawayen da suka zubo masa ya juya cike da jin haushin tashin ta da yayi daga bachi tunda gashi ya rasa abunda zai ce mata, daman shi burinsa ya ganta kuma ya ganta bai san salon da ya kaishi taɓa mata fuska ba.
Bayan ya fice ta sauke ajiyar zuciya,
“Alhamdulillahi”
Ta faɗa tana lumshe ido, ta samu sassaucin halin da take ciki, tasan Saif ya yarda da cikinsa ne a jikinta shiyasa ya kawo kansa gurin ganinta.
A ɓangaren Safiyyah suna fita suka nufi gidan Dr. Zainab, karba tayi musu mai kyau ta kawo musu abin sha, bayan sun ɗan taɓa fira suka bayyana mata abunda ke tafe dasu, Sunsha mamaki lokacin da take gaya musu ita ce Doctor dake duba Minal,
“Ni nake kula da ita sai dai abunda kuke so ba zai yiyu ba dan ba aiki na bane”
Safiyyah ta marairaice murya,
“Haba Dr dan Allah ki taimaka mana wallahi ko nawa kike so zan baki ki ma bani account number ɗinki zan turo miki so mun taɓo”
Sam Dr.Zainab ta ki yarda, hakan yasa Huda nuna mata ɓachin ranta a fili,
“Haba Zainab ace duk amincin dake tsakanin mu kin kasa yi min wannan aikin bafa ita mukace ki kashe ba kuma abunda xaki xubar fa ba a riga an busa masa rai ba”
“Abunda kike son na aikata abune mai matukar wahala Huda ba zan iya ba”
Sata gaba sukayi ita da Safiyyah suna mata magiya, ta roko da daɗin baki, ganin zasu ɓata mata lokacin zuwa aiki yasa tace
“Shi kenan zanyi Shawara”
Sunji daɗi sosai basu bar gidan ba sai da Safiyyah ta karɓi account number ɗinta,
A mota firar kawai suke suna jin daɗi, sun san matsalar su ta warke, bayan Safiyyah ta sauke Huda sukayi Sallama ta nufi gurin da Deen yake, dan tun ɗazu ya matsa mata da kira wai yana son ganinta,
Wani babban restaurant mai kyau da tsada naga ta nufa tana yin farking ta kira shi a waya,
“Gani na iso kana ina?”
“Ina ciki hawa na biyu na ganki ai karaso kawai”
Kashe wayar tayi ta rufe motar ta ta nufi gurin,
Tsaye ta tararda shi bakin kofar hall ɗin fuska babu annuri yana kallonta,
“Ya akayi ne Deen sauri nake yi gida zanje ka dame ni da kira”
Shiru yayi kamar ba dashi take ba, ganin bashi da niyar magana yasa tayin dariya,
“Deen kenan idan wani abun kake so ka faɗa ni wuce zanyi yanzu fa ba kamar da bane da zaka rika yi min haka haka da hankali na riga na gama da naka kawai ka jira result”
“Result ɗin me?”
Sai a lokacin yayi magana,
“Idan ta fito ka aureta mana bashi kake jira ba”
“Kin riga kin ɓata ni gurin Minal babu yadda za'ayi ko da Saif ya sake ta na iya aurenta sannan yanzu haka Minal na can asibiti kwance a dalilin abunda muka mata”
Iskan dake bakinta ta bursar
“Deen Deen kana bani mamaki wani lokacin fa kasan ba xaka iya jurar lokacin da komai xai daidai ta ba miyasa ka aikata”
“Ai ke kika sani na aikata koɓ”
Ya faɗa a fusace,
“Nasa ka ka aikata kai ko kunya baka ji ba ? Mace kamar ni xata sauya maka tunani ka aikata abunda baka yi niya ba? funny kar fa ka fito min da wani can ko kace wai tausayinta zai sa ka tona ma kanka asiri”
“Ko kuma ke na tona miki ba”
“Ka tona na ma kanka dai ai kasan ko kotu aƙaje kai ne tsamo tsamo a cikin laifin tunda kai ka shiga har ɗakinta kuma ka rika matar mutane kuma ka nuna ma mijinta kana tare da matarsa, so kayi hankali dan naga har yanzu baka gama sanin wacece Safiyyah ba fool!”
Wata harara ta watsa masa ta juya tayi tafiyarta, ya fisacta sossai yasan duk abinda ta faɗa kansa hakan yake dan ta riga ta ɗaure gashi kuma tasa yaci amanar minal ya ɓata kansa gurinta, har shi zata raina ma hankali haka?
Rufa mata baya yayi da sauri, zuciyarsa cike da tsanarta. Cikin sa'ah kuwa ya cin mata a stairs tana sauka bata an karaba kawai taji an turo ta da wani irin karfi, gangarowa tayi tana wani irin ihu da ya ɗauki hankalin duk wanda ke cikin restaurant ɗin.
IMAGE WHAT HAPPEN NEXT.............
[9/14, 9:07 AM] Auntie Candy: BABBAN GORO
NA
KHADEEJA CANDY
®
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
*36*
Kasa Saif yayi da kanshi ya ƙlumshe ido yana sauke ajiyar zuciya,
“Ka yarda da ni Saif zan maka duk yadda kake so amman idan nima kayi min yadda nake so”
Buɗe ido yayi ys kalleta,
“Wa nene wanda kike son a sako miki.?”
“Mijin Mahaifiyata ne bayan rasuwar Mahaifin mu mahaifiyata ta aure shi ni kaɗai ce ta haifa da Babana sauran duk nashi ne tun da aka kamashi ita da sauran yan uwana sun kasa samu natsuwa ni kaina na kasa samun natsuwa saboda rashin natsuwar nata”
“Mi yayi aka kamashi?”
“Yan danfara suka danfare shi ya ranta musu kuɗi sai suka gudu shine su kuma suka kamshi”
“I hope gaskiya kika faɗa min!”
“Ko da yana da wani aibin toh ban sanshi ba, dan ni haka mahaifiyata ya faɗan min kenan”
“Fine Miye sunan shi?”
“Sunanshi Alhasan Muhammand Yola”
Wayarsa ya ciro daga aljihu ya dannan kira, bata daɗe tana ringing ba aka ɗauka,
“Ka bincika min wani da aka kama mai suna Alhasan Muhammad yola”
Yana faɗa ya kashe wayar, ya kalleta
“Make sure gaskiya kika faɗa min akan Huda dan duk na gani karya kike sai na sa an wulakan ta ki”
“Gaskiya ce mana Saif how do think mace kamar ni can lie to someone like you!
idan zaka yarda zan fara baka evidence yanzu”
Bata tsaya jiran abinda zai ce ba ta ɗauko wayarta, ta shiga danne-danne, daga bisani ta ɗago ta kalleshi
“Ka buɗe Bluetooth ɗin ka zan turo maka wani abun yanzu sannan ka bani number wayar ka zan turo maka wasu abubuwan ta whatsapp”
Bai mata musu ba ya mika mata wayar ta tura masa abubuwan, ta mika masa wayar tana faɗin,
“Ina son ka kunna wannan Audio ka ji a cikin Audio akwai wanda zaka ji yadda suka shirya komai tsakanin ta da Safiyya na abunda akayi ma Minal kuma nasa maka wata number mai sunan Faruk inason kasa number a wayan Huda jaga ya sunan zai fito sauran abubuwan sai ka cika alkwari nima zan cika maka”
Hannu yasa ya karɓa bai ce da ita komai ba kwakwalwarshi a tushe take, shi har yanzu bai yarda ba sai ya samu hujojin akan hakan, yana zuyawa ta kira shi
“Saif.... Kayi kuskuren auren Huda ka aureta ba tare daka bincika wacece ita ba baka bincika tarbiyarta ba Huda tana tare da abokin karatun ka ko kuma nace abokin ka tun bata aure ka ba sanadiyar sa ta sanka ka ganta kace kana sonta”
Bai juyo ba kuma har lokacin bai ce mata komai ba ya fice.
Har ya isa parking space bai san ya isa ba saboda tunani.da yake magangun Dr.Zainab ne suke masa yawo kai ya daɗe tsaye gurin motarsa kamin ya buɗe ya shiga, koda ya isa gida har wani ciwon kai yake ji a cikin motar ma ya daɗe zaune kana ya fito ya nufi cikin gidan.
Yana tura kofar falon Huda dake zaune sanan kujera ta taso da gudu ta tarbeshi tana faɗin,
“Oyoyo Habibi sannu da zuwa”
Kallo ɗaya tayi masa ta ganshi abnormal, sai dai ba zata iya tantance halin da yake ciki ba, saboda yayi kamar marar lafiya kamar kuma mai damuwa.
“Dear lafiya na ganka haka?”
Ta tambaya cike da damuwa, Kallon fuskarta yake sai yanzu yake tuna wasu abubuwan nata, maida ta yayi gefe ya nufi upstairs hanyar ɗakinsa yana shiga ya maida kofa ya rufe ya zauna gefen gado ɗafe da kai,
daker ya samu ya shiga banɗaki ya watsa ruwa ya fito, ya saka jallabiya da gajeren wando, Sai a ƙlokacin natsuwa ta ɗan shige shi, yana shirin zama Huda ta shigo ɗauke ta turen drinks fuskarta ba far'ah, kusa dashi ta zauna ta zuba masa drinks ɗin tana masa magana,
“Dear ga Drinks ɗin ka kasha nasan rayuwar ka zatayi sanyi sai ka faɗa min abinda yake damunka”
Ko ɗago wa baiyi ya kalleta ba balle ya bata amsa, sosai hankali ta ya tashi rabon da taga ɓacin rai shi irin wannan har ta manta, toh mi yake damunshi ko wani abun akayi ne?
“Saif kayi min magana mana ko nayi maka wani laifin ne?”
Ta faɗa cikin muryar kuka, sai a lokacin ya kalleta ya ɗan murmusa kamar babu komai,
“Wani ne ya ɓata min rai a office amman karki damu ya wuce”
Drinks ɗin ta karɓa ya sha yana janta da fira dan ya kawar mata da zagin dake ranta,
Ita kuma hankalinta ya kwanta ganin ya dawo dai-dai.
DARE.....................
Tare sukayi hira a ɗakinta sai da ya tabbatar da bachi ya ɗauke ta sannan ya ɗauki wayarta ya saci kafa ya fice ɗaga cikin gidan ya nufi gurin motarsa ƴa buɗe ya shiga bayan ya rufe ya kunna Audio da Zainab ta tura masa,
Ba karamin mamaki yayi ba jin abunda Audios ɗin ya kumsa jikinsa ya mutu sosai da abunda kunnuwansa suka ji masa, tabbas muryar Huda ce kuma duk maganganun da yaji akan sa ne sai kuma Minal wani gefen da saurayin nata, Duk wasu tambayoyin da yake son sani ya samu amsar su a Audios. jufa ce ta shiga karyo masa a nan take yaji kansa na tsarawa, wayarta ya ɗauka ya saka number da Zainab tasa masa, Ga mamakinsa sai ga number ta fito amman ɗauke da sunan _FAIRUZA_ a nan take ya danna ma number kira da wayarta, Bai kara katsewa ba sai da yaji muryar namiji muryar abokinsa ƴa ɗauka,
“Hello Sweetheart baki yi bachi ba?”
Bai amsa ba sai kawai ya kashe wayar, ya fito cikin motar a fusace ya nufi ɗakinta, yana isa mai number ya kara kira, wani mugun bugu Saif ya kai mata ta farka a firguce tana haki, wayar ta mika mata ba tare da yayi mata magana ba daman already yayi picking yasa hands-free,
Karɓa tayi amman bata kara wayar a kunne ba sai kallon Saif take jikinta na rawa,
“Hello Sweetheart naji kiran ya katse ne kp network ne?”
Jin muryar mutunen yasa ta kalli gaban wayar number da taga hankalinta yayi matsifar tashi, kamar wanda ya ruɗe sai tace
“Wanene?”
Tana kallon Saif,
“Wanene kuma Faruk ne ba Huda bace?”
Shiru tayi batayi magana ba sai kallon Saif take abunda ka marar gaskiya nan da nan idonta ya faɗa wani zafi ya rufeta baki buɗe tana numfashi kamar marar lafiya, jin hakan yasa mai kiran ya kashe.
[9/14, 9:07 AM] Auntie Candy: BABBAN GORO
NA
KHADEEJA CANDY
®
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
*35*
Fita Kairat tayi da saurin ganin yadda Minal ke kiran sunan Mummy tana kuka,
Ga mamakin ta sai ta tararda ita ma Mummy tana nata kuka wanda ya fi na Minal shiga rai, miya faru ko ita ma ɗin taji abunda Dr. Zainab ta aikata?.
Kasa mata magana Kairat tayi sai kawai ta dafa ta tana hawaye, A firgice Mummy ta juyo sai a lokacin ta tuna duniyar da take, ganin hawaye a fuskar Kairat yasa ta share nata hawayen tana tambayar ta
“Lafiya Kairat mi kike yi ma kuka?”
“Abunda kike yi ma kuka Mummy”
Ta faɗa hawayen na kara zubo mata, a zatonta Mummy tana kuka ne akan abunda Dr.Zainab tayi
“Wallahi Mummy duk cikin Minal ya zube sai nayi shari'ah da wannan likitar bazan yafe mata ba”
Mummy ta rika hannunta cike da fashin fahimtar inda ta dosa
“Mi kike nufi Kairat mi ya samu ciki Minal.?”
Ta share hawayen da ke idonta,
“Mummy Dr tayi mata