Showing 30001 words to 33000 words out of 115850 words

Chapter 11 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

6272

yar iska ce sai me! da ake ɗauko karuwa fa a gidan karuwai a sata bara'ah a aureta balle wannan da take karkashin iyayenta, Kuma ke kika maganar bata da uba shin ita ta halinci kanta ne ko kuma iyayen nata sun shawarce ce ne da zasu aikata ni mutane auna bani mamaki sai a rinka cewa yarinya shegiya shin ita tayi kanta ne ke zaki aureta ne ko ke zaki zauna da ita ne?”


Kuka ta shiga rerawa irin na marasa gaskiya, Saif dai baice komai ba dan Momi ta biyashi, daman yasan bada saninta taje gidan ba.
jin tana kokarin maida kukan na gaske yasa shi katsa mata tsawa,




“Wallahi zan dake ke duk ba ki bar nan gurin ba”


Da gudu ta tashi ta nufi hanyar ɗakinsu, Rukaiya da Lubna suka rufa mata baya.
Momi ta kalleshi cike da natsuwa tace


“Kana ba wani matsala a wajen huda.?”


“Matsalan me Momi nifa ba mijin mace ɗaya bane kuma daman ni ina da niyar karin aure dan kinsan matsalolin da muke fuskanta tsakanin mu”


Ajiyar zuciya Momi ta sauke,


“Toh Allah ya zaɓa mana abinda yafi zama alheri”


“Amin momi haka nake son kice”


****** ****** ******


“Hello Dr.Khadija yau ana tuna damu”


“Hmm ai kullun kuna cikin rai ya kike ya gidan”


“Lafiya kalau ya aikin naku”


“Aiki da godiya, wai wata magana naji agame da mai gidanki ko gaskiya ne.?”


Dariya Huda tayi a ɗayan ɓangaren sannan tace,


“A jarida kika gani ko”


“Eh wai mijinki zai kara aure zai auri yar Dr.Salamatu Abubakar Yola”


“Zainab kenan ke yanzu ko ance miki mijina zai kara aure zaki yarda, ai Saif mijin Huda da Huda da Huda ne ita kaɗai”


“Wai ke yar yanzu baki daina wannan aikin kishin ba, Huda yaushe zaki san kin girma ya kamata ace izuwa yanzu kinsan ciyon kanki”


Huda ta tashi zaune, tana buɗar hanta,


“Zainab indai barin kishine ne.sanin kishin kai toh wallahi yanzu na fara indai akan Saif da uban kowa zan iya ɓatawa kuma wallahi wallahi matukar ina raye Saif bai isa ya kara aure ba nidai ce zama dani ko ba daɗi”


“Huda kiji tsoron Allah taya zaki ce ki hana mijinki aure bayan kinsan yana da dalilin yinsa, Huda ke ba haihuwa kike ba ya kamata ace kin tausaya masa kin barshi ya kara aure ko dan haka,
sannan bawan Allah nan kina zalumtarsa iya zalumta kina tare da abokinsa sannan ahi kansa bakya kyatata masa kuma yanzu kice zaki hana sa aure bakya tsoron hakkin Allah ne idan kika mutu me zaki faɗawa Allah”




Dariya tayi kamar wadda akayi ma albishi,


“Allah sarki Qawata Zainab aikwai ki fa da nasiha a koda yaushe, amman bakya yinta a inda ya dace, yau ni kaɗai nake aikata zunubi ne ko ni kadaice nake zaman aure da zina kowa fa yana nasa saɓon amman sai a zo a samu mutun ɗaya a sha masa kai ina ruwanki ne mijina ne ko mijinki, ni bana son wani wa'azi ki aje abunki wata rana zai yi miki amfani amman ba yanzu”


Bata tsaya jiran abunda Zainab ɗin zata ce ba ta kashe wayar tana jan tsaki,


“Ke kin cika matsala wallahi sai mutun na cikin farinciki ki ɓata masa rai, ki barni naji da abunda zanji mana nace miki ina so wata nasiha ne sai kace wata yarinya mtsss stupid”


Haka tayi da matsifarta tana jin haushin ɗaukar kiran da tayi,






MINAL...................
Sanye ta fito da gown ɗin atamfa tayi rolling ɗin kanta da jan ɗankwali, Fuskarta babu Kwaliya sai dai ta kawatata da murmushi na zumuɗin ganin abokin nata,


“Deen...”


Ta faɗa daidai lokacin data karaso kusa dashi. Ya ɗan daɗe kamin ya ɗago kai ya kalleta da fushi a fuskarshi, nan take murmushin dake fuskarta ya ɓace,


“Sad face Deen mi nayi maka ko dan ban faɗa maka da wuri ba?”


“So.da gaske aure zakiyi kenan?”


Da kakkausar Murya ya tambaya,


“Ae mana Deen aka wasa da maganar aure ne, baka yarda ba dana faɗa maka a phone”


“You betray me Minal kin nuna min true color ki”


Mamaki ne ya cika mata fuska, mamako na taya ta farin ciki sai yace ta ci amanarshi me yake nufi ne,


“Ban fahimce abinda kake nufi ba Deen”


Wani murmushi yayi,


“Kin tsallake ni ki auri wani bayan kinsan duk zaman da mukayi ke nake jira”


Ido ta kura masa kamar bata gane abunda yake faďa ba,


“What you are staring at me common tell me I don't know nasan haka zaki ce”


Kai ta girgiza tana haďiyar yawu


“Deen ban fahimta ba”


“Yes ai bazaki fahimta ba amman bari kiji na faďa maki wani abun da baki sani ba, nima sai naci taki ki rubuta ki aje”


Yana kai wa nan ya juya, da sauri ta riko shi,


“Ni bana fatar cin amanar kowa Deen ni ban ta6a maka kallon matsoyi ba dan haka ban karanta sona a idonka ba kai kuma baka faďa min ba”


“Karya kike Minal karke kice bakinsan ina sonki ba babu wadda zai kalli zamantakewar mu da ke yace babu soyayyah a tsakanin mu kawai dai kin nuna duniya irin cin amanar da kika min ne kin bawa makiya na damar yi min dariya”


Kai ta girgaza idonta taf ta hawaye tace


“Wallahi ban sa kana sona ba Deen kallon aboki nake maka kuma ďan'uwa kada ka rubuta ni a matsayin mai cin amana ba zan iya cin amanarka ba Deen”


Idonta ya kallah,


“Zan yarda da hakan idan kika janye maganar auren ki da Saif kika aure ni”


Sakin baki tayi,


“Deen Saif ya riga yayi maganar aure na kuma na bashi da amincewa taya yanzu zan dawo nace na fasa Deen...-”


“Ba sai kin karasa ba Minal kin nuna min ni wanene a gareki Thank you”


Rigarsa ya ka6e ya juya a fusace ya shiga motarsa. ita dai tsaye kawai tayi yana kallonsa har ya fice.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO


NA


KHADEEJA CANDY


Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy




Kainuwa Writers Association




*25*


Numbar Momi ta kira, Bugu biyu aka ɗauka. jikina na rawa tace


“Hello Momi ina wuni”


“Ba momi bace Safiya ce momi tana part ďin Dad lafiya naji muyarki haka.?”


“Ba lafiya ba Safiyya wai kina da labarin Saif aure zaiyi.?”


“Allah sarki kardai kice min sai yanzu kika sani bayan saura sati ďaya a ďaura musu aure”


“Naji amman ban tabbatar ba sai yanzu dan ni a tunani na bada gaske bane sai yanzu da ya kawo min kayan faďar lefe wai saura sati biyu a ďaura masa aure”


“Toh ya rage miki ne saboda kiga kishiya ba zata wallahi anty da ba Yayana bane da nace azzalumin ace duk zaman da kukayi ya rasa da me zai saka miki sai kishiya, kishiya kuma irin wannan yar shaye shaye karuwa kuma shegiya hmmm namiji kenan”


Fashewa Huda tayi da kuka,


“Wallahi Safiya da ace a mafarki ne aka ce min Saif zaiyi aure bazan yarda ba amman yanzu wai har shi da kansa yake faďa min”


“Kuma kinsan wani abun haushi su Momi da Dad suka goya masa baya sam ni hakan bai min daďi ba dan ni tun lokacin da aka ce yarinyar nan tayi unkurin hallaka kanta naji na tsaneta, shiyasa naje har gidansu nayi mata wankin babban bargo data faďa masa yazo gida dukanane kawai baiyi ba amman sai kinga yadda yake tada jijiyar wuya akanta ita kuma Momi ta goya masa baya”


Cikin muryar kuka Huda tace,


“Wallahi Safiya ban yi zaton Momi zata goya masa baya ba ya aureta mace haka”


“Hmm ai duk goya masa baya sukayi nice kawai nayi masa magana ina nuna masa illolinta sai yace min wai shima tausayinta yake gani kuma idan bai aureta ba hankalinsa bazai kwanta ba wai yaci amanar ta jifa ke har Nasir goya masa baya yayi gurin aurenta wannan yarinyar ta tsafe kowa nice kawai bata samu sa'ah kuma nafi karfinta”


Kasa magana Huda tayi sai kuka take, tana murje murje kasan karfin, hankalinta ne ya kara tashin jin ance kowa ya goya masa bayan yayi wannan auren,


“Oh ji min Anty Huda wai kuka kike ne! Allah sarki ni ina ganin laifin mata masu kuka akan kishiya name a a wallahi bazan wahalar da rayuwa taba”


Daker ta iya furta,


“Safiya hankalin Saif ya riga ya gama tafiya gurin yarinyar nan kwata kwata yanzu baya kulani gashi sai zagin iyayena yake yana cimin mutunci shiyasa ma na kira na faďawa Momi ina cikin matsala Safiyyah”


“Ke ďan Allah ki daina zubarda hawayenki akan wata yar iska, ai akan wannan yarinyar komai sai iya yi miki dan ta riga tayi masa magani amman kinsan wani abun ba ai idan tasan wata bata san wata ba indai magani ne tayi ni kuma zanyi mata makirci wadda yafi magani”


Tashi Huda tayi zaune, tasa hannu tana share hawayenta


“Me kike nufi Safiyyah zaki taimake ni ne?”


“Ae taimako kan zanyi miki zan yima kaina da duk family mu dan wannan da kika gani da kowa zata iya raba shi kuma tunda nace bana sonta bana sonta sai na hana auren ta da Yaya”


Wani sanyi sanyi Huda ta fara ji, cikin zuciyarta wadda bai gama hawa saman fuskarta taba,


“Mi zakiyi Safiyyah.? wallahi da kin taimaka min daman nasan duk cikin family ku babu mai sona irinki”


“Yanzu ne zan nuna miki so Huda sai na hana ta zama gidan Yaya kota halin yaya keda yaya kuma mutu kan raba, ai daman ance mai laya kiyayi mai zamani kuma BABBAN GORO SAI MAGOGIN KARFE,in dai ita takamarta magani ni kuma zan nuna mata zamani da boko da kuma kalar barinki da bata sanshi ba”


Wannan karon Dariya Huda tayi,


“Amman wallahi da kin faranta min rai kin cire min damuwata”


“Hmmm kawai kisa ido kiyi kallo, ke dai daga yanzu ki daina nuna masa kishi da haukar nan ta mata ki bishi kar kuma ki sake kiran Momi da sunan yi mata sheidair wani wani sau da kafa sauran bayani sai gobe idan nazo.”


Tana kaiwa nan ta katse kiran, da sauri Huda ta kalli wayar tana buďar baki da fuskar mamaki,


“Ikon Allah daman ance duniya mai faďi abunda ka sani shi ka sani wadda baka sani ba baka sanshi ba ashe Safiyya mace ce”


Abunda ta faďa kenan tana kokarin tashi tsaye,da nufin komawa saman gado ta zauna.






****** ****** ****


MINAL.................
Safa da marwa kawai take cikin falon, tana busar da iskar baki. Tun kairat na kallonta har ta gaji tayi mata magana,


“Wai lafiyarki Sis kike wannan yawon haka.?”


Da sauri tazo kusa da ita ta zauna, fuskarta cike da tsananin damuwa tace


“Sis Deen ne nayi da kiran wayrsa bai ďauka ba daga karshe ma sai kashewa yayi har yanzu fushi yake dani ya kasa fahimta ta”


Wani dogon tsaki Kairat taja,


“Deen! Deen!! Deen!!! haba Minal miyasa ba zaki aje shi a inda ya aje ki ba har yashe zaki fita harkar sa ne aure fa zakiyi kuma ke da kanki kike faďa min Saif yace kiyi masa alkawarin ba zaki kara kula sa ba yanxu Deen ďin nan ya fita harkar ki ai kodan haka yaci ace kema kin kyale shi”


Tashi tayi tsaye a fusace, ta nufi hanyar Upstairs tana faďin,


“Ai daman nasan ke ba fahimta zakiyi ba, shekarar mu nawa tare yanzu yana fushi dani ace bazan bashi hakuri ba, ko an faďa miki abota karya ce shashasha kawai”




Da ido kawai Kairat ta bita tana kaďa kai,


“She kenan kije yi ta yin abunda kike ganin yafi miki wadda bai ji bari ba yaji hoho”








**********************




“Amincin Allah ya tabbata a gareka ya kai wannan natsattsen matashi”


A hankali ya ďago kai ya kalleta. a nan ta cire katon bakin gilashin dake makalle idonta cikin tattausan lafazi tace,


“Sarki ya tabbata ga Ubangijin wannan halittar,
Hakika kana da kyau, da kwagiji kana da cikar kamala da sanya zuciyar yan mata faďuwa, babu wata mace zaka ce kana sonta ta kika sai idan tana da wata manufar ne da daban,
Mutum ne kai mai rikon amana wadda har hakan yasa Minal ta aminta da kai kai kuma ka bata kanka ka zamo mata raqumi tana jan akalar daga karshe tace amanar ka, wadda ko kwankwanto babau nasan zaman da kayi a wannan gurin ita kake tunani”


Kallon natsuwa yayi mata, shidai bai ta6a ganinta ba sai dai fuskarta tayi masa kamada fuskar wadda da yasani,


“Wacece ke.?”


Ya tambaya yana mata wani kallo, idonsa a jawur kamar wadda yayi shaye-shaye, murmushi ta sakar mashi sannan tace,


“Sunana SAFIYYAH BASHIR BATURE kanwa gurin SAIF BASHIR BATURE zan iya zama.?”


_Safiyyah Bashir Bature_ cikin zuciyarsa ya maimaita sunanan yana kallon mutanen dake zaune gurin shakatarwa kamar mai neman wani.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.


NA


KHADEEJA CANDY


Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy




*24*




“Saif tun ɗazu ne yazo i was so sad...”


Hannu ya ɗaga mata, fuskarsa a haɗe


“Minal kin dame ni da labarin Deen bana da alaka dashi so please ki daina min a maganar sa”


ta ɗan gyara zamanta, ta fuskance shi


“Am sorry but ni yanzu yana ganin naci amanarsa fa”


Banza tayi mata kamar bai jita ba, zuwa can ya kalleta yace,


“Minal kinsan abunda nake so dake”


“A'a”


“So nake kiyi min alkawari ba zaki sake kula wani namijin ba ba zaki sake saka tufafin da zasu fitar miki da tsiraici ba, ba zaki sake kula Deen ba da duk abinda ya shafe shi”




“Saif Deen abokina ne fa”


“Ni kuma mijinki ne just promise me Baby”


Baza iya masa alkawin rabuwa da Deen ba ko kuma kin kula shi dan haka yasa ta tashi da nufin shiga cikin gidan,


“Ok i wll thing about it”


Da sauri ya riko ta yana dariya, daman yasan abune mai wahala tayi ta rabu da Deen yanzu,


“Common Minal karkice min kinfi son Deen da ni”


Dawowa tayi ta zauna,


“Saif kana da muhimmanci a gareni kana babban gurbi a zuciya matsayinka daban matsayin Deen daban bana son kana haďa matsayin sa da naka,
Saif yanzu Deen yana kallo na a matsayin mace da taci amanar ya kamata na goge wannan shatin da idonsa sukayi mani”


“Fine”


Kawai yace ya tashi, ya nufi kofar da zata fitarshi daga Garden ďin,
Da hanzari ta cigabansa,


“Haba Saif daga magana sai kayi fushi”


“Dole nayi fushi Minal nifa wadda zaki aura taya kike ganin zan iya jure kina magana da wani me kike son mutane suce ta kike son a kalleni.?”


Shiru tayi yana nazari, wani gurin yana da gaskiya sai dai ita kan bata iya rabuwa da Deen yanxu,


“Ok i wll i promise amman Saif Deen ba yanzu ba i want to talk ko him”


Kafaďunta ya dafa,


“Fine amman ba just at onces”


Kai ta ďaga masa, azuciyarta kuma ba daďi.
Hannunta yaja ta rakashi har gurin Motarsa.






****** ****** *****


“Ku ajesu a nan”


Yace da yaran da suke ďauke da akwatuna, yana nuna musu gurin da zasu aza,


Sai da suka gama jearasu tsaf sannan suka fice. Shi kuma ya xauna saman kujera yana kwalama uwar gidan kira


Da Sauri ta sauko downstairs, ďaure da tawul, jikinta kuma da sanyin ruwa, da alama wanka ta fito.
Murmushi yayi mata,


“Oh wanka kika fito ne”


“Ae dear waďannan kayan fa.?”

Ya kishingiďa da kujeara yana sauke ajiyar zuciya,


“Gasu nan dai duba ki gani”


Ba musu ta shiga buďe akwatu nan zuciyarta cike da fargaba,
Kayane na gani na faďa masu kyau da tsaďa babu abunda babu cikin tun daga kan kayan kwaliya zuwa na shafe shafe su tufafi ba a maganarsu,


Bayan ta gama dubawa ta ďago da raunanin, idanu ta kalleshi,


“Na gani Saif kayan waye.?”


“Naki ne ko baki so.?”


“Nawa fa kace?”


“Ae Momi tace na siya na kawo miki abunda babu sai ki faďa min kuma duk abinda kike so ki faďa min”


“Momi fa kace Saif ka fito kayi min magana ban gane inda ka dosa ba”


Ya ďan daďe kamin yayi mata magana dan yasan maganar ba zata mata daďi ba, ita kuma ta sakar masa ido tana mai kallon jiran amsa,


“Kayan faďan kishiya ne nan da sati biyu zanyi aure insha Allah”


Bushewa tayi da dariya, duk falon ya cika da amonta, ta nuna shi da tsaya


“Haba dai Saif bana son irin wannan wasan fa ni kasan babu abunda na tsana irin ayi min wasa lokacin da nake gaske”


Kallon, kur yayi mata,


“Ba wasa bame sweetheart wallahi da gaske nake”


Tashi tayi tsayi, fuskarta babu annuri,


“Au ashe da gaske da ake faďar kara aure zakayi ina karya tawa yau har ya rage sauran sati biyu a ďaura maka auren, kai ko kunya baka ji ka buďe baki ka faďa min har ka ďebo wannan hegun kayan ka kawo min nayi me dasu tsirara ka ganni ne amman ban ta6a sanin kai azzalumi bane sai yau Saif”


Kalamanta sun fusata shi dan shi ba irin mazan nan bane masu tsaya mata na faďa musu magana son ransu ba,


“Ke kimshin haukarki ya tsaya kanki karki kuskura faďowa kaina wallahi zaki raina kanki duk abunda zakiyi sai dai kiyi amman bazan fasa aure nan ba tunda iayayena basu hanani ba babu wadda ya isa ya hanani”


Bai jira cewarta ba ya nufi hanyar ďakinsa. Ita kuma ta shiga ďiban kayan tana zubarwa tana kuka,


“azzalumi wallahi ba za'ayi wannan auren ba mugu ni zaka ďasawa bakin ciki wallahi sai ka raina kanka”


daga nan ta zuba da gudu ďakinta, tana ihu kamar mahaukaciya.Kasan carpet ta faďi tana murje murje da kiran ta shiga uku, ta daďi a haka can wani tunani yazo mata da sauri ta nufi gurin wayarta.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO


NA


KHADEEJA CANDY


Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy




*26*


Daf da zata tura kofar falon ta shiga, Saif ya buďe ta ta fito yana gyara hannun rigarsa, da sauri ta gaishe shi


“Yaya ina wuni”


“Lafiya kalau Safiyyah ina kika fito haka .?”


“Daga gidan wata kawata nake sai nace bari na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login