Showing 42001 words to 45000 words out of 115850 words

Chapter 15 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

5664

zubo mata wanda taso ta tsaidasu suka ƙi tsaiduwa,


Wani irin tausayinta ne ya fusgi zuciyarsa, sai yaji kamar a tsokar jikinsa hawayen suke zuba haka yaji kamar ya tashi ya koma kusa da ita ya share mata hawayen ya rumgumeta,
A take tsanar Saif ya shiga zuciyarsa, miyasa yake gallaza mata har haka? dan me zai ɗauke mata ƙafa har na kwanaki huɗu, akan abunda zuciyarsa ta tabbatar masa da bata aikata ba, shi taya ma zai faɗa mata saƙon da Saif yace ya faɗa mata? Sai yanzu ya gano dalilin Saif na shirya tafiyar da yayi ba tare data sani ba, kuma har yake son tafiyar ba tare daya faɗa mata ba, ko ƴyanzu ma in ban da ya tirsasashi da ba zata sani ba,
Tunani yake yadda Saif yake amsa masa maganar duk da yayi masa ta Minal da kakkausar murya, wanda ke nuna har yanzu cikin ɓacin rai yake,


“Saif yanzu kana ganin kayi tafiyar nan da Minal.baifi ba a maimakon Huda?”


“Da huda nake ra'ayin tafiyar Nasir ban ma faɗa ma Minal ba kuma bazan faɗa mata ba sai dai taji na tafi”


“Saboda mi naga ai itama matarka ce kuma hakkinta ne idan zakayi tafiya ka faɗa mata, ka kuma tambayi ta idan tana buƙatar wani abun”


“Toh baxan yi mata hakan ba au nasan dai abinci da yake cikin gidan zai isheta har na wani lokacin, dan Allah ka daina yi min maganar Minal Nasir indai kana son mu zauna lafiya”


“Amman dai kasan Allah ne ya ɗora maka hakki haka ko”


Ya fita cikin motar yana faɗin,


“Na wakiltaka kaje ka faɗa mata kayi mata duk abunda ya dace”


Bai tsaya jiran abunda zaice ba, ya nufi bayan motar ys fiddo kayan da suka siyo ya nufi cikin gidan,
Nasir na kokarin ribas Safiyyah ta fito daga falon Huda ta nufoshi tana tsayar dashi,


“Ya akayi ne?”


Ya tambaya bayan ya tsaya ɗin,


“Dan Allah Yaya ka sauke ni gida”


“Ba gida zanje ba gurin Minal zani Saif ya ban sƙo na kai mata ne”


“Oke muje kawai”


Da sauri ta shiga motar. Cike da son ta bishi ɗin dan taji wane saƙon ne Saif ya bashi ya kai ma Minal.
Gyara zaman da tayi ya dawo dashi daga duniyar tunanin daya tafi,
Ya kalleta a kasale muryarsa kuma na nuna rashin jindaɗi yace,


“Saif yace na faɗa miki tafiya ta kamashi zuwa Londom kuma gobe zai wuce duk abunda kike so ki faɗa min”


Da sauri ta kalleshi hawayen dake idonta suka ɓalle, suka cigaba da zuba, bakinta na rawa tace,


“Toh.”


Da sauri ta tashi ta nufi dan samun damar yin kukan da take haɗiyewa,
Shima tashi yayi tsaye, yana kiranta, bata amsa masa ba saboda halin da take ciki bata son juyo balle ma har ta dawo.




Ƙasan carpet ta faɗi tana wani irin kuka abun tausayi,
Ƙasa tayi mata zafi gashi kuma yanzu ƙsaman nason kama mata da wuta, Saif zai tafi ya barta bai damu da duk halin da zata shiga ba, miyasa har yanzu Saif ya kasa fahimtarta ko yayi mata uzuri?
Da sauri ta ɗauki wayarta da makulin matarta ta bar gidan. Tuƙi take tana kuka kanta babu ɗankwali jikinta ko mayafi babu daga ita sai doguwar riga ta isa gida,
Sai tayi fakin wani tunin yazo mata, shin mi zata cewa Mummy wane hali mummy zata shiga idan ta faɗa mata? Shin mummy ma zata yarda da bata aikata ba?
Ganin bata da amsoshi waɗannan tambayoyi yasa ta share hawayen dake idonta, ta buɗe motar ta fito ta nufi cikin gidan.

“Assalamu alaikum”


Ta shiga falon da ƴar far'ah kamar gaske, duk idonta a kumbure yake,
Tsohuwa ce ta amsa mata cike da mamakin abunda ya kawo ta gidan yanzu gata kuma a yamutse,


“Wa'alaikissalam Minal kece haka?”


“Nice Tsohuwa ya gida?”


Ta faɗa tana kallon Kairat dake kwance saman doguwar kujera tana bachi,


“Gida lafiya kalau Kairat ce kawai ba lafiya”


“Miya same ta”


Da sauri ta karasa kusa da ita, ta rame sosai tayi baƙi kamar ba ita ba,
Tsohuwa ta taso daga inda take ta nufo Minal tana faɗin,


“Tun ranar da kika tare washe gari ta tashi da rashin lafiya kuma Hajiya tayi tayi ta kaita asibiti ya ki ankira likita ya duba ta taki yarda a dole aka sama ta ido ko abinci kirki bata ci”


Tausayinta ne ya kamata Minal, nan da nan kukan dake tare da ita yayi kokarin dawowa, a take ta manta da nata damuwar, tana kallon fuskar Kairat, mi yake damun yar'uwata haka? Wane irin ciwo ne wannan miyasa bata son taje asibiti? bayan nasan Kairat da tsoron ciwo!
A hankali ta kai hannu ta taɓa jikinta, hawayen dake idonta suka zubar Kairat a fuska, Hakan yayi sanaɗiyar tashinta daga bachi,

Tana ganin Minal ta zabura ra tashi zaune, tana kiran sunan nata da kasallaliyar murya,


“Minal kice?”


“Nice Kairat mi ke damunki?”


“Aike ya kamata nayi ma wannan tambayar kinga yadda kika rame?”


Hannu takai ta taɓa wuyanta, sai kuma damuwarta ta dawo mata arai, tashi tayi ta nufi hanyar ɗakin Mummy,


“Minal Ina Saif...”


Tambayar ta tayi mata tasa ta juyo, ta kalleta,


“Yana gida gobe zaije London shine yace nazo gida”


“Kizo gida kamar ya?”


Kairat ta tambaya fuskarta ɗauke da mamaki. Duk yadda Minal tayi kokarin ɓoye damuwarta sai da ta bayyana a fuskarta saboda hawayen da suka shiga zubo mata, Duk da rashin kuzarin da Kairat take ji bai hana ta tashi ta rika hannu Minal suka nufi ɗakinta,


** ** **


Da kanta ta zaunar da ita saman gadon tana kallon fusakarta,


“Minal faɗa min meke damunki?”


Idonta na hawaye tace,


“Kairat jindaɗi na ragaggene, mafarkina yankanke ne a duk lokacin dana hango haske sai naga karshensa duhu ne, bansan nayi ma duniya take juya min baya ba i know rayuwata yar kaɗan ce amman naso jindaɗina na kasance dogo sai gashi ban samu haka ban Duk ƙlokacin da farinciki na raɓe ne toh bakin cikin da zai shafe ni sai ya fishi yawa”




Kukan da take yasa Kairat kuka,


“Minal ki faɗa min abunda yake damunki mi Saif yayi maki?”


Bata ɓoye mata komai ba, cikin abunda ya faru komai sai da ta faɗa mata.
Sosai jikin Kairat yayi sanyi, sai dai itama ɗin ta yarda da Minal ba zata iya aikatawa ba amman miyasa Deen ɗin yayi mata haka? Waya shirya mata wannan abun dole a kwai wani abu akasa, tausayin Minal ya kamata akoda yaushe cikin bakin ciki take Sai yaushe jindaɗin ta take mata fata zaizo mata, farincikinta a yanzu Saif ne kuma shima ya juya mata baya.
Hannu tasa ta share mata hawayenta, itama tana kuka, tace,


“Kiyi hakuri Minal zanyi masa magana kinji?”


Kai Minal ta ɗaga mata duk da tasan ko tayi masa maganar ba yarda zaiyi ba,


“Please Kairat karki faɗama Mummy zata iya shiga wani hali kinji?”


“Bazan faɗa mata ba”


Suka rumgume juna suna kuka.
Sun ɗauki lokaci a haka sannan ta taso ta fito daga ɗakin ta baro Minal.


Gardem ta nufa ruke da wayrta tana danna ma Saif kira,
Sai da tayi masa miss calls biyar ana shida ya ɗauka,


“Ya akayi.?”


Muryar Saif ta ratsa jiyoyin jikinta da kunnenta ta game ilahirin jikinta,
Wani dogon numfashi taja sannan yace,


“Dan Allah dan Annabinsa ina son kaganinka na haɗa ka da girman Allah”


“Me xanyi miki.?”


“Kazo dai yanzu ina son ganinka dan Allah da ya halince ka”


Bai bata amsar zaizo ko bazai zoba sai kawai taji ya katse kiran, lumshe ido tayi ta sauke ajiyar zuciya, ta juyo jikin a mace ta dawo falo.


Toh yanzu ya zata ɓulloma ƙlamarin ba lallai bane ya gansu da maganar ta waya sai dai kuma tasan ba zai zoba tunda ya kashe mata waya, toh kodai ta kyaleshi, wata zuciyar tace baza iya jure ganin Minal haka ba, kuma tasan Mummy ma idan taji zata iya shiga wani halin.
Tana cikin wannan tunanin mai gadinsu ya shigo yace Saif na sallama da ita a waje,
Tashi tayi da sauri bayan tace masa yace tana zuwa ta shiga ɗaki ta ɗauko hijab ɗinta ta nufi kofar fita,
Tsaye ta hangonshi jikin motar hannayensa zube cikin aljihu yana sanye da wata shadda blue colour ta karɓi jikinsa sosai ɗinki yayi masa kyau, fuskarsa babu annuri,
Ita kuma fuskar tasa take kallo har ta karasa kusa dashi,


“Na gode da kazo Sannu da zuwa”

“Ba godiya nazo kiyi min ba ba kuma tarbarki nake so ba dalilin kiran nake son ji”


Ya faɗa kamar a fusace, ajiyar zuciya ta sauke murya a kasale tace,


“Dan Allah kazo mu shiga ɗakin baki sai muyi maganar”


Baice mata komai ba sai kawai ya nufi hanyar ɗakin bakin ita kuma ta rufa masa baya, tana kare masa kallo.




Bayan sun zauna, ta kalleshi tana murzar hannunta tace,


“Saif Minal ta faɗa min abunda ya faru, nasan zakayi wahalar fahimtar ta amman ....-”


Hannu ya ɗaga mata,


“Idai maganar Minal ce toh ki hutar da kanki babu ta yadda zaki juya min kwakwawa alhalin ga gaskiya ina gani da ido na kuma ta faɗa ta bakinta ta amsa laifinta”


“Saif ba haka bane nasan Kasan Minal amman ba zata iya aikata irin wannan a cikin gida ka ba...-”


Tashi yayi tsaye, yana mata wani kallo,


“Na auri minal ne saboda ina sonta kuma ina tunanin idan na aureta zan iya canja mata hali sai gashi na tararda tuwon da ta tuka a gidana yafi wadda take tukawa a gidansu,
Sai a yanzu na yarda ta zancen mutane da suke cewa Minal bata da tarbiya bata dace dani ba”


Ta tashi tsaye itama,


“Haba Saif! Wannan wace irin magana ce haka nasan kana tare da ɓacin rai amman ya kamata ka tausayawa Minal kayi tunanin halin da zata shiga kodan rashin mahaifin nan ta take mafama dashi”


“Rashin mahaifi.?”


Yayi murmushi,


“Nina sa mata rashin mahaifin ne ? Minal bata da tarbiya Kairat bata da kirki bata min halacci ba sai yanzu nake nadamar auren ta da nayi”


Kairat ta fusata sosai, dan haka ta nuna masa tsaya,


“Karka sake zagin Minal karka sake ce mata bata da tarbiya kar bakinka ya sake faɗin wata mummanar kalma akan Minal idan hankalinka ne ya ɓace toh ya dawo jikinka Saif”


Matsowa yayi kusa da ita yana murmushin gefen fuska,


“Kina sonta da yawa Kairat shiyasa kika da ɗaukar mata da soyayyarki shiyasa kika rika kai kawo wajen ganin na aureta kika rika kareta bayan kinsan bata dace dani ba,
Kika zaɓi ke ki mutu ita ta rayu, akaina kike wannan ciwon Kairat na sani”


Kai ta girgiza masa,


“Kayi kuskuren fahimtar Saif babu soyayyarka a cikin zuciyata ko kaɗan”


Kara matsowa yayi kusa da ita ta yadda tana iya juyo bugun zuciyarsa, yace


“Ki kalli kwayar ido na ki faɗa min baki sona ki karya ta kanki da kanki indai har da gaske babu sona a cikin zuciyarki!”


Kasa ɗago kai tayi ta kalleshi balle har ita iya furta abunda ya bukace ta dayi.
Hakan yasa shi yin murmushi mai sauti,

“You see ba zaki iya ba, kin cutar dani Kairat da kika karkata zuciyata zuwa ga Minal bayan kinsan halinta kin kuma san bata dace dani ba, i hate you but i hate her more”


Yana kaiwa nan ya kaɓe mata rigarsa ya juya a fusace ya bar mata falon,
Sai da taji tashin motarsa sannan ta share hawayen dake idonta ta nufi kofar cikin gida, tana buɗe kofar taga Minal tsaye a bakin kofar da hawaye shaɓa-shaɓa a fuskarta.








_ME ZAKU CE AKAN WANNAN.? ME KUKE TUNANIN ZAI FARU A GABA.?_


#VOTE
#Comments
#Oneheart
#KhadijaAbubakarAlkali
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO


NA


KHADEEJA CANDY


*_Ga barka da Sallah na baku, ni kuma ku aje min nama😋 zanzo na karɓa😊_*


*30*


“Miyasa baki faɗa min kina sonshi ba? Miyasa kika bari na aureshi bayan kinsan ke yake so?”


Sune tambayoyin da Minal ta riƙa yima Kairat tana hawaye,
Itama hawayen take sai motsi take ta baki, kamar mai son yin magana ta kasa,
Girgiza ta Minal ta shigayi da ƙarfi tana kuka.


“Ki bani amsa mana Kairat miyasa kika sadaukarda soyayyarki ga wace farin cikinta kaɗan ne?
Miyasa kika bari na auri Saif bayan kinsan ba nice mace da yake so ba kinsan ban dace da rayuwarsa?
Miyasa zaki cutar da kanki kuma nima ki cutar da akan abunda zaki iya juyashi ya zame miki farin ciki?”


Kuka Kairat take yi sosai kukan da bazata iya furta mata koda ‘A’ ba balle ta amsa mata tambayoyinta.
Ganin hakan yasa Minal ta saketa tayi baya-baya har ta jingina da bango, ta sulale ƙasa tana matsar gashin kanta,


“Allah na tuba idan wani abun na maka Ya Ubangijina na tuba ka yafe ni, Allah karka kama ni da laifin da bansan na aikata ba Allah karka ɗora min abunda bazan iya ɗauka ba”


A hankali taji an shafa tsakiyar gashin kanta zuwa bayan ta sannan aka duƙo dai-dai tsawonta an sa hannu a anshafi gefen fuskarta,
Wani sanyi taji ya ratsata, ta lumshe ido tana ƙara saita fuskarta ga Mummy,


“Ko wane Bawa da irin jarrabawar da ake jarrabarsa da ita Minal, kowa da adadin Allah ya ɗibar masa na rayuwarsa da jidaɗinsa da farinciki da kuma mutuwarsa,
Ba'a taɓa dauwama a abu ɗaya Minal jindaɗi bai taɓa ɗaurewa ba,
Dole ne ka mutu ka barshi ko kuma shi ya ƙare ya barka, kamar haka ne wahala bata ɗaurewa, dukan abunda yake fararre toh ƙararrene wannan abun, Ɗan Adam baya taɓa samun abunda yake so 100%,
Allah yana jarraba bayinsa badan baya sonsu ba sai dan ya gwada imaninsu da irin juriyarsu, wani yana can yana neman irin rayuwarki bai samu ba, yana neman farinciki koda ma wadda bai kai naki ba bai samu ba,
Kiyi haƙuri Minal ki kasance kicin bayin da haƙuri yake zame musu riba, kiyi haƙuri dan Allah kar lokaci yazo wanda haƙurin zai zame miki dole kuma a lokacin baki da lada, kiyi haƙuri Ƴata kici jarrabawa ki yarda da ƙaddara baki san abunda mahaliccinki ya tanadar miki ba”


Kai ta girgiza ma Mummy alamar gamsuwa ta rumgumeta suna kuka,
Kairat ma tana tsaye a gun da take tana nata kukan, aka sara mai ba wani haƙuri.
Sun daɗe a haka sannan Mummy ta rika ta suka tashi tsaye tare ta nufi hanyar ɗakin.
Wanka mummy tasa tayi sannan ta kwanta taja bargo ta lulluɓe, zaune mummy tayi kusa da ita tana kallonta har bachi ya ɗauke ta,




*** *** ***


Bata farka sai bayan la'asar, tana tashi ta sake yin wanka tayi sallah, sannan ta nufo downstairs, Babu kowa falon sai tv dake ta aikinsa, windon falon ta nufa tayi tsaye tana kallon Parking space, wani yanayi take ji mai wuyar fassara, bata jin kuka a yanzu sai dai na zuci ta take, fuskarta tayi wani fari kamar marar jini, lumshe ido tayi ta sauke ajiyar zuciya.


“Minal...-”


Buɗe ido tayi ta juyo tana kallon Kairat ba tare da ta amsa ba,
Karasowa tayi kusa da ita idonta cike da hawaye tace


“Kina jin haushi na ko?”


Ko dai bata ɗaga mata ba balle tayi mata magana sai kallon fuskarta take,


“Na sani Minal, amman ina son ko fahimce ni bana nufin ɓata miki rai ko kara miki bakin ciki Minal nafi son farin ciki kin fiye da nawa bazan iya auren abunda kike so ba,
Banyi hakan da wata manufa ba sai dan sama miki farinciki saboda yadda kike sonshi”


Har lokacin bata ce mata komai ba sai kawai ta ɗauke kai jin hawayen da suke son zuɓo mata,
Ganin hakan yasa Kairat ta juya jiki ba kwari ta nufi hanyar upstairs


“Kina son shi Kairat”


Cak. Kairat ta tsaya ta juyo ta kalleta tana share hawayen ta tace,


“Idan nace miki bana son shi nayi karya Minal babu wata cikakkiyar mace da tasan kanta zats kalli Saif tace bata sonshi koda bai nuna mata ba balle ya nuna,
Saif yana da cikar kamalar mace bata isa ya kalleta yace yana sonta taki amsa masa ba duk yadda nake son wani Minal nafi sonki da dashi”


Hannu Minal tasa ta share hawayen da suka zubo mata tana murmushi, ta soma magana a hankali tana takowa kusa da Kairat,


“Nasan Har yanzu baki gama karantar waye Minal ba Kairat har yanzu baki waye ni ba,
Nasan kina sona Kairat you don't have to tell me nasan kina son farin ciki na nasan zaki iya yin komai a kaina amman kinyi abu ɗaya daya ɓata min rai kuma nake ganin laifin ki akanshi kin san minene.?”


Ta dafa kafaɗar Kairat tana kallon fuskarta,

“Saboda me zaki sadaukar da soyayyarki ga wanda kika san soyayyarta zata zame mata bakin ciki da damuwa,
Miyasa baki faɗa min Saif baya so na ba miyaaa zaki zugashi ya aure ni bayan kinsan ba nice zaɓin sa ba miyasa kika yi haka Sister?”


Hannunta Kairat ta rika,


“Saif yana sonki sister wallahi ni shaida ce da ace baya sonki da bazai aure ki ba kinsan waye Saif Minal babu wadda ya isa ya sashi abunda bai tashi ba,
Kece mace ta farko da ya fara so kuma ya aure ki a yadda kike, Minal nice bana da tabbacin son da yake min saboda yana sona na dan halayen da yake tunanin na ɗara ki dasu, da ace zan canja hali da ba zai so ni ba amman ke kinga a yadda kike kuma yake sonki a haka ɓacin rai ne yasa shi yin kalaman da yayi miki ɗazun Minal ke kanki kinsan Saif yana sonki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login