Showing 63001 words to 66000 words out of 115850 words
Chapter 22 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
wofi, na fahimci ka fara shaye-shaye kuma har yana kokarin taɓa maka kwakwalwa ya mai da kai mahaukaci har yar uwarka kana kokarin yi mata sheri”
Momi ta dafa shi,
“Ba haka bane Alhaji wani gurin yana fa da gaskiya ni kai na nayi.....”
“Kin yi me? So kike ki goya masa baya ko ai nasan komai yake yi da haɗin bakin ki ake yinsa daman ku mata karamar kwakwalwa ce da ku duk yadda yara suka ce zasuyi sai ku biye su toh ni ba zan ɗauka ba!”
Saif ya sauke ajiyar zuciya cike da ladabi yace,
“Dad kayi hakuri idan ranka ya ɓace amman wallahi abunda nake faɗa maka akan Huda gaskiya ne haka ma na Safiyyah”
“Bai dame ni ba bazan matsa maka ka mai da huda ba ba kuma zan saka zama da ita dole ba amman ina shedai maka ba zaka sake yin wani auren ba...”
Saif zaiyi magana Dad ya ɗaga masa hannu,
“Bana son wata magana tashi ka bar min parlour na”
Ba musu ya tashi ya fice Momi ta bishi da kallon tausayi har ya fice,
Daddy kuma ya bishi da kallon haushi dan shi gani yake kamar yana yin haka ne dan ya samu damar sakin mace tunda yayi ma Minal Huda ce ta biyu, so yake ya mai da kansa mai auri saki.
***
Kallo ɗaya Daddy yayi ma Momi ya gane ranta ya ɓace ganin yadda ta ɓata fuska kamar tayi kuka, yasan yadda Momi take son Saif dan shi ne ɗanta na fari kuma ɗa ɗaya tilo namiji a cikin ɗiyan da ta haifa saɓanin shi da yake da wasu yayan da uwar gidansa, sai dai kuma duk a cikin matansa babu mace da yake so irin Momi hakan yasa baya kaunar ganin ɓacin ranta,
Kokarin sakin fuskarsa yayi yana kallonta,
“Kin ɓata rai tun da nayi ma ɗanki faɗa ko? Kin fi son a bashi gaskiya ko da baya da ita uhm?”
“Ba haka bane Alhaji naso ka bashi dama ya faɗa maka yadda abun yake idan bai faɗi abunɗa yake ransa ba ya za'ayi kasan gaskiyarsa, yarinyar nan fa mutane da yawa sun ɗora zarginsu akanta nima kai na daɗe ina zarginta amman kai daga zuwan ka haushi da faɗa akan wata can bare kaki ka saurari ɗan ka”
Ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta,
“Bana son goya masa baya ne kar gaba yaje ya aikata abunda yafi wannan, kuma kinsan hausawa na cewa kaso naka duniya ta kishi ka ki naka duniya ta so shi, kin ga haka kwana kin baya yayi da Minal yanzu kuma ya sake da Huda”
“Abunda Yayi ma Minal Abban Lubna sheri ne akayi mata yanzu kuma ya gano gaskiya, Huda kuma da gaske ne ta aikata ba sheri akayi mata ba”
“Wa yayi mata sherin?”
“Safiyyah ce, shine dalilin da yasa yaje ya dake ta ranar a asibiti”
“A'a ki daina zancen Safiyyah ya za'ayi safiyyah tayi ma ɗan'uwanta wannan abun”
“Naji amman kasan ai baza ayi mata sheri ba ko? Kuma ni bana son kayi fushi da shi akan wata can da bata ma san kana yi ba”
Murmushi ya ɗanyi ya kau da kansa, hakan yasa ta kwanto jikinsa tana faɗin,
“Ina son kayi min izini gobe zanje duba Minal asibiti”
Yaji daɗin tambayar da tayi masa, Yana ɗaya daga cikin abunda yake kara masa sonta, duk inda zata je sai ta nemi izininsa duk da kasancewar ta yar boko kuma yar siyasa amman bata taɓa yarda ta fita ba tare da izininsa ba, Hannu yasa ya rumgumo ta cike da jindaɗi
“Nayi miki, ba ta da lafiya ne?”
“Eh kasan Tana fama da ciwon nan na blood cancer kuma ga cikin da ke jikinta”
“Toh Allah bata lafiya ya sauke ta lafiya”
“Amin haba ko kai fa amman ka wani taso min ɗazu da matsifa duk kasa na tsorata”
Dariya yayi irin tasu ta manya yana kara janta jikinsa.
*** *** ***
Saif na fitowa part ɗin Daddy ƴyaji duk ya tsani gidan, babu abinda Saif ya tsana irin faɗa, faɗan da Daddy yayi masa yasa rance ya ɓace sosai, yasan kuma babu gurin da zai samu sassauci idan ba ganin Minal yayi ba dan a yanzu ita kaɗai ce farin cikin sa, komawa yayi part ɗin Momi ya ɗauki makullin motarsa ya bar gidan.
*** ** ***
“Sister ina zoben ki.?”
Kairat ta tambaya lokacin da idonta suka kai kan yatsun Minal,
“Saif ne ya cire shi”
“Saboda mi?”
“Wai yana so”
“Kuma kika kyale shi ya ɗauka”
“A a ban ma sani ba hannu na kawai ya rika ya zare”
“Kin ban mamaki Minal kinyi saurin ba da kai ace duk wulakancin da Saif yayi miki kina kulashi har ki bashi damar rika hannun ki yay....”
“Kairat.....”
Mummy ta tari numfashinta tana zuba ma Minal abinci a plate, ta cigaba
“Da zaki lura da zaki gane Saif yayi nadama Kuma yana son Minal sosai a yanzu”
Kai ta girgiza,
“Oh Mummy abunda nake kokarin lurar da ku ba shi kuke son ganewa ba, yana son ta zai wulakanta ta yaki saurarenta”
Mummy ta zauna kusa da Minal tana kallon Kairat
“Dole ne duk namijin da ya kama matarsa da wani yayi abunda Saif yayi koma abinda yafi wanda Saif yayi,
Zuciya a ɓace take a lokacin ido a rufe kunnuwa kuma a dwaɗe ba zai iya sauraren ta balle har yayi mata uzuri amman kin ga a yanzu da gaskiya ta bayyana yanzu ne zaiyi ma kansa bitar karatun da ya manta,
Minal tana bukatar kulawar Saif a halin da ake ciki yanzu ko dan abinda yake cikin ta.....-”
Shigowar Saif yasa Mummy katse maganar da take ta kalleshi, Hannayensa zube cikin aljihu fuskarsa ba yabo ba Fallasa ya gaishe ta,
Da mamaki ta amsa masa ganin dawowarsa yanzu bayan bai daɗe da tafiya ba, abinci dake Hannunta ta aje ta tashi ita da Kairat suka fice,
Murmushi ya sakar Minal ganin yadda ta sako masa ido tana kallonsa, da sauri ta rufe idon nata kamar mai bachi, karasawa yayi kusa da ita yaja mata hanci
“Tashi ki ci abinci ba wani bachi”
Buɗe ido tayi sai kuma ta ɗan haɗe fuska, yana taɓa mata hannu ta fisge, bai damu ba ya zauna a kusa da ita ya ɗauki abinci yayi one spoon zai kai mata a baki ta kawar da fuska
“Zan iya ci da kai na ka aje”
“Oh Kairat tace miki wani abu kenan ko?”
A nan ya aje abinci ya tashi da zimmar fita, tayi saurin riko hannunsa,
“Ba ta ce min komai ba kawai dai bana son ka bani ne”
Dawowa yayi ya zauna,
“Duk abinda nake miki Minal ina yi ne ɗan baby na da yake jikin ki, da kin haife min shi ba zaki saki ganina ba”
Yana faɗar hakan ya tada ita zauna ya soma bata abincin.
Sai da ya tabbatar da ta koshi sannan ya aje plate ɗin ya gyara mata jikinta ya kuma gyara mata kwanciyarta, ya hau gefen gadon ya kwanta, ya jata zuwa kirjinsa yasa mata hannu ciki riga, zabura tayi ta tashi zaune tana kallon shi
“What.?”
Ya tambaya kamar bai san abinda yayi ba,
“Dr yace na dai na kwana da wani a ɗaki ɗaya”
Ta faɗa murya kasa-kasa, murmusawa yayi
“Common Minal karki mai da ni wani kalar mutun mana, ko ba likita bane ni ai nasan aikin su, ko ki kwanta ko na ɗauke ki muje gida mu kwana”
Karantar da gaske yake a idonsa yasa ta koma ta kwanta ta bashi baya, Hannu ya sake sa mata A inda yasa ɗazu, ganin tana unkurin sake tashi yasa ya rumgumeta still hannun nashi yana cikin riganta,
“For the sake of our baby......”
Ya raɗa mata a kunne yana lumshe ido, buge masa baki tayi da kanta tana murkususun kwace kanta
“Sake ni naje wani ɗakin na kwanta bachi nake ji”
“No kwanta a nan ba zan miki komai ba i promise”
Ya faɗa yana zare hannunsa daga cikin rigan nata, a nan ta gyara kwanciyar ta, shi kuma ya sauke ajiyar zuciya ya shafa kansa yana haɗiyar yawu.
*** *** ***
MORNING @9:21AM.............
Da kansa ya haɗa mata kari, ya rika bata a baki tana ci har ta konshi sannan ya washe komai ya mai da gefe, ita kuma ta kwanta tana kallon windo, a nan ya shiga matsa mata kafafu a hankali, ganin tana jindaɗin matsar yasa shi fara wuce guri yana shafar cinyoyinta,
“Please Saif stop..”
Ta faɗa tana janye kafafunta, ɗauke hannunsa yayi yasa yatsunsa cikin gashin kansa yana matsar gashin ya lumshe ido.
Ringing ɗin wayarsa yasa shi buɗe ido, yasa a hannu aljihu ya ɗauko wayar yana dubawa, number Momi ce
“Hello”
Ban ji me aka ce masa ba na dai ji yace
“Ok”
Ya kashe wayar ya fita.
Bai daɗe ba ya dawo ɗakin tare da su Momi da kannensa,
Tashi Minal tayi zaune tana kallonsu, murmushin da ta gani a fuskar Momi yasa ta kalli Saif, shima murmushin ta ga yana yi mata. Momi ta nufo ta ta kama hannayenta
“My child.....”
Sai idonta suka cika da hawaye, rumgume ta Momi tayi tana shafa bayanta,
“Kiyi hakuri yata ki yafe mana rashin sani ne yasa muka wulakanta ki ashe ke alheri ce a gare mu”
Kuka Minal tasa ma Momi kuka mai ban tausayi da tsuma zuciya, Momi tayi ta bata hakuri har su Kairat da Mummy suka shigo, Kairat taji daɗin ganin Momi sosai hakan ya tabbatar mata da lallai Saif yayi nadama tun da gashi har mahaifiyarsa ta zo ganin matarsa, Fira Momi da Mummy suke hirar yaushe gamo, sun ɗan daɗe suna tattaunawa sannan Momi tayi musu sallama.
*** *** ***
Kai da kawo Abban Huda ya rika yi a gurin Saif ganin yadda ita Huda ɗin duk tabi ta haukace akansa, amman Saif ya ce sam shi kan ba dashi ba gaɗa a hurumi, shi kan ta riga ta fita ransa, ganin hakan yasa shi zuwa gurin Daddy ya tuntuɓe shi da maganar Daddy bai ki tasa ba sai dai kuma shi ɗin mutun ne da baya tursasa yayansa yin abunda basu tashi ba yasan a halin yanzu Saif ya riga ya yafe ta, hakuri kawai Daddy ya bashi yace su cigaba da addu'ah.
Sannu-sannu bata hana zuwa sai dai a daɗe ba aje ba, kuma bayan wuya sai daɗi hankalin Minal a yanzu kwance yake babu abinda ƴke damunta, kula take samu ta ko'ina bata da matsala a yanzu in ban da rashin lafiyar da take fama da ita dan ciwon yaki ci yaki canyewa kullum sai karuwa yake kamar ba abunda ake yima magani ba, hakan yasa likitoci suka bada damar ya rika fita da ita suna ɗan zaga gari sai dai ba tafiya mai nisa ba ko da a cikin asibitin ne zasu iya yinta, ganin cikinta ya fito kuma yana ɗan yi mata nauyi.
Yau ma kamar kullum yana zaune saman gadon tayi matashin kai da cinyarsa yana karanta mata magazine yana saka mata gauta a baki.
“Saif...”
Ta kirashi a hankali, bata damu da ya amsa mata ba ta cigaba
“Huda ta kira ni ɗazu”
Rufe magazine ɗin yayi ya kalleta,
“Mi tace miki?”
“Kawai ta gaishe ni kuma ta tambayi kana nan nace mata a a lokacin ka ɗan fita ne”
“Da wace wayar ta kira ki?”
“Waya ta mana”
Hannu ya kai ya ɗauki wayar dake kan filo
“Daga yau ba ke ba waya sai kin haihu”
“Haba dai karka min haka mana wallahi ita ta kira ni”
“Naji ai, na dai ce ba zaki sake rika waya ba that's all”
“Amman Saif da ka saurare ta baka sani ba ko wani abun zata ce maka ta faɗa min wai tana kiran ka baka ɗagawa”
Leɓenta ya rika ya ɗan matsa kaɗan,
“Da ba ke bace kika min wannan maganar da sai na buge miki baki”
Turo baki ta ɗanyi, wai ita ala dole tayi fushi, yadda tayi ɗin sai ya bashi dariya har ya aika mata da kyautar kiss yana shafa ta.
Shigowar Dr. Zainab bai sa ya dai na abunda yake ba, tun da ba yau ta soma ganin yana taɓa ta ba kuma a ganinsa ba haramun yayi ba sai dai ace yayi rashin kunya,
“Sannun ku da hutawa”
Ta faɗa tana murmushi, tashi Minal tayi zaune
“Yauwa Dr sannu da zuwa”
“Yauwa Minal ya lafiyar jikin?”
“Alhamdulillah”
“Ina ganin ni daga yau za muyi canji aiki da abokin aiki na wato likitan da yake kula da ke ya dawo kuma shine zai cigaba da kula da ke har lokacin da zaki samu sauki”
Ta kalli Saif da bai san ma abunda take faɗa ba dan hankalin baya gurin, wasa yake da yatsun Minal yana goga mata fuskarsa yana raɗa mata wasu maganganu a kunne wanda ita kaɗai tasan manufar su kuma take jin mi yake faɗa,
“Saif ...”
Dr. Zainab ta kirashi ta yadda zai iya bata aron hankalinsa
“Yes”
Ya amsa mata ba tare da ya kalleta ta ba, sai dai ya ɗan ɗago kai alamar yana sauraren ta,
“Na gode sosai da ka cika min alkawari na a yanzu haka mahaifiyata tana cikin farin ciki nima kuma ina cikin sa dan farin cikin ta shine nawa”
“Your welcome”
Ya faɗa yana ɗan cizon kumatun Minal. Murmushi tayi
“Minal Allah ya kara lafiya ya kuma saukar da ke lafiya”
“Amin na gode sosai”
Juyawa tayi ta fice daga ɗakin tana murmushi, indai sabo ne ta saba da ganin irin wannan soyayyar a gurin Saif tun da Huda ma yana mata kuma ganinta bai sa ya daina abunda yake.
*** *** ***
“Saif Mi kayi mata hala?”
Kiss ya rika mata yana faɗa mata,
“Wani ne nasa aka sako mata ko mijin mamanta ko me oho wani dai Alhasan Muhammad Yola”
Ras! Ras! Sunan ya kayar mata da gaba duk da bata san mai sunan ba, amman ba zata manta da Mummy ta faɗa mata fullname ɗin mahaifinta ba shima Alhasan Muhammad Yola, sai dai ba lallai bane ya zamo shi ɗin bane,
“Mi ya faru? Ko kin sanshi ne?”
Ya tambaya ganin computer ta nuna faɗuwar gaban nata,
“A'a ban sanshi ba”
“Miyasa gaban ki ya faɗi?”
“Babu komai”
Baya son ya matsa mata da tambaya, gashi kuma yaga yanayin ta ya canja kwantar da ita yayi yana buga bayan ta alamar tayi bachi.
Amman ina bachin yaki yazo mata sai ma ta dasawa kanta sabon tunani, ganin hakan yasa ya tashi ya sauko da ita saman gadon
“Muje mu ga gari”
Da sauri ta gyara tsayuwarta daman abunda take nema kenan, shi kuma ya rika hannunta ya ɗauki wasu abubuwan da likita yace ya rika, rika mata idan zasu fita.
*** *** ***
Yawo ya rika yi da ita har sai da tace masa ta gaji sannan ya biya wani shago ya saya mata kayan ciye-ciye, a maimaikon ya dawo da ita asibitin sai kawai taga ya nufi wani gida da ita,
“Mi za muyi a nan?”
Ta tambaya tana kallon fuskarsa shi kuma ya bata amsa yana kokarin kashe motar
“Karatu”
“Wane irin karatu kuma?”
Bai ce mata komai ba ya buɗe motar ya zagaya gefenta ya buɗe mata
“Fito muje ciki ba zamu daɗe ba”
“Mi zamu yi a ciki?”
“Idan muka je zaki gani ai”
Kamar tayi masa musu sai kuma ta fito suka nufi kofar shiga cikin gidan.
Saman kujera ta zauna tana karewa parlour kallo shi kuma yayi murmushi ya zauna kusa da ita yana jan hancinta, tana kallon shi ya ɗaga mata gira ya kai hannu ya taɓa cikinta,
“Saif ka daina mana”
Ta faɗa kamar zatayi kuka,
“Baby na ne ai”
Unkurin tashi tayi yayi saurin rumgumeta yana dariya, ya shiga matsa mata jiki yana murzawa cikin wani irin salo wanda ita kaɗai tasan fassarar sa,
kallon tuhuma tayi masa, shi kuma ya ɗaga mata kafaɗu yasa mata hannu cikin riga, zatayi magana ya haɗa bakinsa da nata..........
*** *** ***
A ɓangare Safiyyah ma bata da wata matsala, dan Momi bata nuna mata komai ba gashi kuma tana samun kula gurin Gwaggo, kafar ta ma zan iya cewa ta warke tafiyar ta ce kawai ke da saura ta dawo dai-dai,
abu ɗaya ne yake damun ta wanda kullum shi ne yake ci mata tuwo a kwarya, son Saif son da ba zai taɓa gogewa a zuciyarta ba, son da bai taɓa bari taga laifin Saif ba, son da kan rufe mata ido ta aikata komai,
Ajiyar zuciya ta sauke ta lumshe ido, Gwaggo dake rike da carbi ta kalleta
“Ki dai na damun kanki Safiyyah, ki bari kawai ki kara jin sauki hankali ya kwanta zamu samo kan Saifu sai mun ba kowa mamaki”
Bata ce komai ba ta kai hannu ta ɗauki plate ɗin indomie dake gabanta ta fara ci.
*** *** ***
Wasa-wasa yanzu cikin Minal yana cikin wata na bakwai, duk wanda