Showing 12001 words to 15000 words out of 115850 words

Chapter 5 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

6261

babbar ministen man fetur_
Ajiyar zuciya ta sauke tace,
_Da kika dawo sai kika kika fitar da wannan saurayin naki wadda ya chanja miki tunani har kika rik'a k'ina a kanshi_.
K'asa Minal tayi da kanta tana haɗiyar yawu, idonta cike da hawaye,
Tashi Mummy tayi ta shiga bedroom, bayan kamar minti goma ta fito rike da wani littafi mai kamada Diary daga gani tsohuwar ajiya ce dan duk tayi kura, ta mika ma Minal tana faɗin,
“Wannan littafin na aje shi ne danki duk gurin da wani family members naku yake address ɗin shi yana nan ciki wannan shine tarihin ki Minal ina fatar zaki sami natsuwa”
Hannu Minal tasa ta karɓa tana kallon fuskar Mummy dake kokarin maida kukan dake son fito mata,
Juyawa tayi ta koma ɗakin hawaye na mata zuba, Hannu Minal ta mika zata rik'o hannun Mummy, da sauri Saif ya rik'e mata hannun tana kallonshi ya girgiza mata kai, alamar a'a.
Nan itama ta fashe da wani irin matsanai cin kuka ta chusa kanta cikin kirginshi, rumtse idon yayi da suka yi mishi jawur kamar wadda yayi kuka,


Kukan tayi sosai sai da ya tabbatar da ta samu sukuni sannan ya ciro handkerchief ɗinshi ya share mata hawaye ya rik'a hannunta suka fice,
Gurin da yayi parking ɗin motarshi ya nufa sai ya saka ta sannan ya shiga ya fara Driving,
Har suka isa babu wadda yace da wani uffan ita dai sai kuka take yi, shi kuma ya kasa bata hak'uri.
“Minal miye haka kuma tun ɗazu kuka kike kodai baki yarda da abunda Mummy tace miki bane?”
Bayan ya kashe motar yayi mata maganar yana ɗan buga sitarin motar,
“Na yarda Saif ina dai jin ban kyautawa Mummy ba ina ma ban aikata abunda na aikata ba miyasa idona suka rufe na kasa fahimtar Mummy mi yasa banyi mata uzuri ba? Ji nake yi ba daɗi bansan miye abun yi ba”
Kallonta yayi,
“Minal in dai har kinyi nadama to kije ki bata hak'uri ki nuna mata kinyi nadama kuma ki roki gafarar ta kinji?”
Kai ta ɗaga mishi tana share hawaye, sannan ta buɗe motar da niyar fita, sai kuma ta juyo ta kalleshi.
Murmushi ya sakar mata wadda ya faɗar mata da gaba ya wani lumshe sleeping eyes ɗinshi ya buɗe still yana murmushi,
Ta daɗe tana kallonshi kamar ba zata ɗauke idon ba, sai kuma ta k'arasa fitar ta rufe mishi motar.
Bai bar gurin ba sai da yaga ta shige cikin gidan sannan ya sauke ajiyar zuciya ya sama motar shi key,

Kai tsaye gidanshi ya nufa yana yin parking ya dubi a gogon hannunshi, 10:41pm ya gani kai ya ɗan girgiza ya buɗe motar ya fita,
Da sallama ya shiga yana kallon gurin da Huda ta saba zama, cikin sa'a kuwa ya hangota zaune ta tsaɓa ado tana kallon tv kamar bata san da shigowar shi ba, duk da yasan taji sallamar maybe tayi hakan ne dan yayi dare,
Kusa da ita ya k'arasa ya ɗan lek'i fuskarta
“Dear kina jina kika ki amsa sallama ko?”
K'ara ɓata fuska tayi,
“Sai da nace maka karka daɗe zamuyi zaɓen cake amman kaje ka zauna har yanzu”
Sai a lokacin ya tuna da maganar Birthday ɗinta, da sauri ya zauna kusa da ita,
“Ayyah Wallahi kwata-kwata na manta.. -”
Ganin yadda ta kalleshi yasa ya chanja maganar,
“I mean wani abun nayi important ba wai mantawa nayi ba”
Taɓe baki tayi “Ba wani nan daman dai baka ɗauki abun da muhimmanci bane har akwai wani abun important da yafi nawa?”
Bayan ta ya shafa cikin daɗadɗiyar murya da yasan zata kashe mata jiki ya soma bata hak'uri kamar mai raɗa,
“Am so sorry Dear tuba nake muje yanzu mu zaɓa”
Kallon shi tayi kamar ta musa masa sai kuma taji ba zata iya ba, ganin hakan yasa ya rik'a hannunta suka nufi bedroom.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!


NA


KHADEEJA CANDY




_There are 4 things you can never recover, The stone..after the throw. The word..after it’s said. The occasion..after it’s missed. The time..after it’s gone._



BABI NA GOMA SHA BIYU___12




MINAL..............
Juyi take tayi saman gado tana tunanin Mummy, sai damn shafa Diary take wasu zafafan hawaye na mata zuba,
A hankali taja filo ta rungume, wani irin tsanar kanta ta karaji,
Tun jiya bata samu ta rumtsa ba gashi yau ɗin ma bachin yaki d'aukarta dan sam idanunta babu alamun bachi ciki,
Tashi tayi zaune tana cizon bakinta, ta janyo wayarta ta danna ma Deen kira, bugu ɗaya ya ɗauka,
“Hello Deen”
“Ma'am Deen kana kusa ne.? Ina son magana da kai”
Daga can cikin wayar ya amsa mata,
“A'a bana kusa Deen amman dana kare abunda nake zanzo ok”
Kasa kasa ta amsa mishi
“Ok”
ta kashe wayar, ta tsura ma Screen ɗin ido,
Motsin da taji yasa ta tashi ta nufi parlor, Kairat ta gani tsaye tana wasa da keys ɗin dake hannunta, da gudu taje ta rungume ta
“Ke lafiyar ki?”
Kairat ta tambayeta tana kokarin boye murmushin dake fuskarta,
Sakinta tayi ta kama hannayenta,
“Thank you for coming daman ina bukatar wadda zamu tattauna”
Zaunawa Kairat tayi tana faɗin “Saif ne yace min nazo”
Ajiyar zuciya ta sauke
“Kairat Mummy ta faɗa min komai ta faɗa min ko wacece ni Kairat Mummy ta wahala sosai kamin nakai matsayin da nake yanzu”
Nan Kairat ta tari numfashinta, “Kuma lokaci ɗaya kika juya mata baya idonki ya rufe kika kasa fahimtar komai kunnen ki a daɓe kika ki saurara mata”
Idonta cike da hawaye
“Nayi nadama sosai nayi dana sanin yin hakan da nayi kuma ina bakin cikin dana saka Mummy cikin bakin ciki”
“Toh idan dai har haka ne Minal kije ki bata hak'uri yanxu baki san halin da take ciki ba saboda ke Minal kuma nasan duk ta ganki zataji daɗi zata kuma yafe miki abunda kika mata kinsan Mummy bata da wani farinciki sai naki”
Shiru ta ɗanyi
“Sis kina ganin Mummy zata saurare ni kuwa zata yafe min nan take ta fahimci ne?”
“Sosai ma ai tasan ke a rashin sani kuka yi kuma kin gane kinyo ba daidai ba yanzu kika zo neman gafara zata yafe miki kinsan tana sonki sosai ai”
Haka Kairat tayi ta mata har ta karfafa mata gwuiwa.




******


Kuka sosai Dr. Salamatu tayi har sai da ta godewa Allah kukan data shekara ashirin da wani abu batayi irinshi ba, rayuwarta, ta baya dawo mata a rai wani kololo ya tsaya mata a rai.
Ajiyar zuciya take ta faman saukewa, sakamakon wano kololo da yayi ya tsaya mata tana dafa zuciyarta wai ko zata zamu sassauci amman sai kara jin abun take yi Har yaya kokarin taushe mata numfashi,
Hakan yasa ta tashi ta nufi downstairs,
tana sauka ta buɗe firig ta ɗauki gorar Swan, saman firig ɗin ta ɗauki cup ta zuba ruwan.
Sai da tasha kopi biyu sannan taji abun ya ɗan kwanta mata, dawowa tayi saman kujera ta zauna tana sauke ajiyar zuciya, jin bata samu sukuni ba yasa ta tashi ta nufi babban parlor gurin da tsohuwa da Talatu suke zaune suna kallo.
Har ta kusa isa sai kuma ta juya ta nufi upstairs, ɗakinta ta koma ta kwanta sakamakon ciyon kan da taji yana son taso mata, idonta ta rufe kamar mai bachi tana haɗiyar yawu,

“Mummy.........”
Kamar daga sama taji kiran da muryar Minal hakan yasa tayi saurin buɗe idon ta kalli kofa,
Gurfane take kasan gwuyoyinta fuskarta shakaf da hawaye,
“Mummy ki yafe min na tuba nayi nadama nayi hakan ne dan kawai nasan ko wacece ni Mummy I'm so sorry”
Da sauri Mummy ta sauka saman gadon ta nufi kofar ta tada ita tsaye ta shigo ta ita cikin ɗakin,
Sake zubewa kasa Minal tayi ta rik'e kafafaun Mummy tana kuka kuka na gaske mai nuna tayi nadama har a cikin ranta,
“Mummy ban kai Ya ba ban miki halanci ba ban kyauta miki ba ban kuma kyauta ma kai na ba nayi babban kuskure dana yi miki mummunan zato ki yafe min kar kiyi fushi dani”
Dafata Mummy tayi tana hawaye
“Ki daina kuka Minal banga laifinki ba daman nasan sai wannan ranar tazo dole ne wata rana zaki bukaci sanin ko wacece ke, ni ban taɓa fushi dake ba, na kuma yafe miki duk abinda kika yi min”
Tashi Minal tayi tsaye ta rungume ta tana kuka,
Murmushi Kairat dake tsaye bakin kofa tayi ta kunno kai cikin ɗakin,
“Daman ai na faɗa miki Mummy zata yafe miki kinsan tana sonki sosai ai”
Sakin Mummy tayi ta share hawayenta ta kalli Kairat, “Thank you Sister”
Kumatunta Kairat taja
“You most welcome”
“Allah yayi muku albarka”
Mummy ta faɗa tana kallonsu cike da jidaďi,
Haɗa baki sukayi gurin amsawa,
“Amin Mummy”
Snap suka zube Kazan carpet Mummy Tana Kara labarta ma Minal halin rayuwar ta,
Daren ranar ɗaki ɗaya suka kwanta da Mummy ko wane zuciyar shi cike da fariciki.




WASHE GARI............
Dummm! Kake ji wani wawan dudu Kairat ta kai mata a baya, a firgice ta farka ta tashi zaune,
“Mi akayi?”
Baki Kairat ta saki
“Huh tambaya ta ma kike dubi time ko gani karfe nawa yanzu wane irim bachi ne haka?”
Sai da ta murza ido sannan ta dubi a gogon,
“Eleven pass ten”
Kairat ta bugar mata kai
“Kika kai har 11 kina bachi dan kawai jindaɗi”
Kan ta dafe
“Oh Sis kan nan ma fa ciyo yake min”
“Yau toh ni ina ruwana ya fashe mana dan Allah wake up”
Tashi tayi dan tasan ba yadda ta iya dan idan tace zata koma Kairat ba zata barta ba, bedroom ta nufa tana mika,
Bata daɗe ba fito tana faɗin “Ina Mummy Sis?”
“Ta tafi aiki tun ɗazu tana da meeting ɗin da bazata iya canceling ba kuma bata son a tashe ki ta dai ce na kula dake”
Taɓe baki Minal tayi tana rike da kofar toilet,
“Haba Dear yama za'ayi Mummy tace ki kula dani how old are you ma da zaki iya kula dani definitely Mummy ba za tace haka ba”
Tashi Kairat tayi tana dariya,
“Of course i can little girl come let me show you something”
Da gudu ta fisgi hannun Minal suka nufi downstairs, bata sake ba sai da suka kai Dinning room,
“WOW”
Minal. Ta faɗa tana kallon kalolin abincin da aka jere, saman dining ɗin,
“Kairat duk wa yayi wannan?”
“Nice mana duk wazai miki wannan idan ba ni ba”
Plantain Minal ta ɗauka ta kai baki,
“Please Sis faɗa min gaskiya”
Sai da ta ɗan tsakure ta sannan tace
“Mummy ce ta haɗa miki kinsan tana sonki ai”
Wani irin daɗi ne ya ziyarci zuciyar Minal, hannu tasa a baki tana murmushi,
“I know and I love her too”
Murmushi Kairat tayi ta mika hannu a ɗayar kujerar ta ɗauko wani ɗan karamin kwali mai zagaye da fulawowi,kamar gift ta mika mata
“And this one is from Saif”
Da sauri Minal ta karɓa taja kujera ta zauna ta shiga buɗewa,
Wani ɗan karamin Cake ne da wata yar karamar paper fara mai haske gefen cake ɗin, sai da ta gutsuri cake ɗin taci sannan ta shigo karanta takardar,


``` HELLO MINAL....


How are you? How particularly is Dr. Salamatu weather treating you? Ina fatar komai ya zama daidai yanzu! Na hango ki kina ta rawa cikin bachi na,```


Murmushi ne ya suɓuce mata ta lumshe ido tana tsutsar baki, har na kusan mintuna sannan ta buɗe su kan takardar,


```Ah ha! That is it i just want to see your smile and say good morning to you have some breakfast and have a nice day.```


*~Sign~*
*Mr. S B_B*




A bayan takardar aka rubuta,

*Your Brother From Another Mother*




Da murmushi ta rungume takardar tana kallon Kairat data sakar mata ido,
“Waya aiko ko shine ya kawo da kanshi?”
Hannayenta ta ware alamar ban sani ba,
“Nikan karki tambaye ni nima gani nayi a aje miya rubuce a ciki?”
Da sauri ta mayarda takardar bayanta
“Ba ruwanki please ni dai bani number shi idan akwai”
Baki da murguɗa mata
“Nima bana da ita kije can ki nema”
“Kince Mummy tace ki kula dani fa haka ake kula sa mutun ba'a bashi abunda yake so?”
“Ai kince karya nake yi right? Bazan iya kula dake ba”
“A'a na daina zaki iya Allah”
Dariya Kairat tayi ta nufi Stairs,
“Toh kici abinci saina baki yar Mummy”
Murmushi Minal tayi ta shiga cin abincin cike da shauki.








Wattpad @khadeeja_candy


Candynovels.wordpress.com


#Share
#Vote
#Comment
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO....!


NA


KHADEEJA CANDY




_Never ignore a person who loves and cares for you, because one day you may realize that you’ve lost the moon while counting the stars._




BABI NA GOMA SHA UKU___13




“Wai kina nufin bachi zakiyi.?”
Idonta a lumshe ta ďaga mishi kai alamar eh,
“Toh karma ki fara kwana biyu fa haka kike min kina barina online gurin za6a miki Cake har biyu na dare kina sharar bachinki kuma yanzu kice bachi zakiyi ai nine n chanchanci haka”
Maganar yake yana wani shafa bayanta ita Kuma tana kwance saman cinyarshi, ďaga kai tayi ta kalleshi
“Anjima kuma zaka za6a min rigar da zan saka da takalmi”
Murmushi yayi,
“Lallai yarinya daďi yayi miki yawa kiji daďin sake yin bachi ki barni ko?”
Zatayi magana wayarta dake kan flat table tayi ringing, da sauri ya ďaga ta daga jikinshi ya nufi gurin da wayar take, juyowa yayi bayan ya duba wayar yace
“Number ba suna”t
Tana jin haka tayi saurin tasowa kamin ta karaso ya danna picking ya kara a kunne,
Yanayin fuskarshi naga ya chanja alamar mamaki,
“Wanene.?”
Da sauri naga ya kalli wayar ya kalleta
“Muryar naji wai hello Dear nace wanene ya kashe wayar”
Faɗuwa gabanta yayi da sauri ta karɓi wayar ta shiga dubawa,
“Ni ban ma san mai number ba ina jin wrong number ne”
Kafaɗunshi ya ɗaga ya rik'a fuskarta ya sakar mata kiss a goshi,
“Bari naje shirin aiki karna zama doja akai karata gurin Dad ok?”
Kai ta ɗaga mishi yayi mata murmushi ya nufi ɗakinshi,
Da kallo ta bishi sai da ya shige sannan ta dafe kirjinta ta sauke ajiyar zuciya ta nufi kicin tana dannar wayar,
Yana shiga ya cire kayanshi ya shiga bathroom yayi wanka ya fito ya shiga shirya kanshi,
_DiLLL_ wayarshi tayi kara alamar sako, kallon wayar kawai yayi ya ɗauke kai sai da ya gama shirinshi tsaf sannan ya ɗauki wayar ya duba,


``` HELLO Mr. S. B_B


Minal Alhasan ce bansan kallaman da zanyi amfani dasu wajen gode maka ba na sani cikin farin cikin da ban taɓa mafarkin shiga ba na gusar min da duk wani bacin rai na, ka sami nida Mahaifiyata cikin farin ciki mun koma kamar yadda muke a da na gode sosai Saif Allah ya saka maka da Alheri bazan taɓa mantawa da kai ba.


FROM MINAL!```




Murmushi yayi yasa wayar aljihu ya fice,




“Wai mi kike ma murmushi ne?”
Kairat ta tambaya,
Murmushin ta sake yi ta mika mata wayar,
“Duba da kanki”
Ba musu ta karɓa tana dubawa,
“Oh Sis yanzu ki rasa irin text ɗin da zaki tura Mishi sai irin wannan ?”
Fuskar mamaki tayi “Mi kike nufi?”
“Toh yanzu dan Allah miye abun burgewa cikin wannan massage ɗin sai kace wata yar kauye”
Tsaki taja ta fisge wayarta ta tashi da nufin barin ɗakin,
“Aikin banza daman ai ni ban taɓa yin abu kika yaba min ba kullum ni ban iya komai ba”
“Matsalar ki kenan ba ada ikon faɗa miki gaskiya sai ki hau tsakanin da Allah ni banga abun burgewa cikin wannan message ɗin ba abu kamar ba wace tayi karatu a waje ba”
Tsakin ta sake ja a karo na biyu ta watsa mata harara ta fice tare da jan kofar ɗakin da karfi,
Dariya kawai Kairat tayi ta cigaba da dannar wayarta.




*******************




Bashi ya dawo gidan ba sai 9:30pm a gajiye ya shigo, kai tsaye ɗakinshi ya nufa ya shiga bathroom ya watsa ruwa ya fito jallabiya ya ɗauka ya saka tare da ɗan short jean sannan ya fito ya nufi ɗakin Huda,
Zaune ya tararda da ita laptop na gabanta tana faman duba wasu riguna, ko sallamar da yayi bata amsa mishi ba,
Kusa da ita ya zauna bayan ya sakar mata kiss a kunci yace
“Dear mi kike yo haka baki masan na shigo ba?”
“Wallahi ina ɗan duba wasu riguna ne da zan saka ya aikin?”
“Alhamdulillahi aje wannan aikin muje muci abinci yunwa nake ji”
“Nima fa yunwar nake ji daman kai nake jira ka dawo”
Hannunta ya rik'a
“Toh na dawo tashi muje downstairs”
Kallonshi tayi “Take away fa nake nufin kayi mana dan tun abincin rana ne da Larai ta dafa kuma faten doya kasan kuma baka sonta ni kuma ban samu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login