Showing 3001 words to 6000 words out of 115850 words
Chapter 2 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
sha'awar zama ni kaɗai ba tare da ita ba”
Ajiyar zuciya Momi ta sauke
“Kana yabo Huddallah da mugun hali wadda ni ban taɓa ganinta da shi ba, kuma idan ma tana da wani halin ai yanxu zata daina tunda saki ya shiga tsakanin ku,
Amman ace abi yak'i ci ya k'i cinyewa har iyayen ta su kai ga magana”
Shiru yayi kanshi a kasa wadda hakan ya bawa Momi damar cigaba,
“Ina son dan Allah ka mayar da matar ka ɗakinta ba zai yiyu ka dawo nan ka tare ba dan ka saki matarka kaje ɗan Allah ka ɗauki matarka ku kuma gidanku hankalin mu ya kwanta nata ya kwanta na iyayenta ma ya kwanta”
Gefen fuskar shi ya shafa “Shi kenan Momi insha Allah yau zanje na ɗauko ta ko Dad yayi min magana indai shine matsalanku daga yau ya wuce”
“Haka nake so Allah yayi maka albarka ya baku hak'urin zama ya kawar da fitina.
Amman a'ce dan ka saki matarka sai ka dawo gida ka tare sai kace mace”
Da dariya Momi ta k'arasa maganar,
Shi ma tashi yayi yana dariyar yayi mata sallama ya fice,
Yana fitowa ya nufi dining area,
Zaunawa yayi ya zuba ma kanshi abinci, sai da yaci yayi nas sannan ya dawo saman kujera ya zauna sai tunane tunane yake.
Sai kusan goman dare sannan ya tashi ya nufi part ɗinshi, ruwa ya sake watsawa ya shirya cikin shadda blue color da bakar hula bayan ya ďauki car keys ďinshi ya nufi parking space,
Yana tada motar ya ɗauki hanyar da yasan zata kai shi gidansu Huda,
A hanyarshi ta isa can ne ya kira wayar Dad yana labarta mishi yadda sukayi da Dr. Salamatu,
Murna Alhaji Aminu Ibrahim. Yayi sosai ganin Saif yazo ya tafi da matarshi,
Huda kan sai da nuna halinmu na mata wai ita ko a jikinta alhalin a zuciyarta farinciki ne falau,
Har taso tak'i zuwa sai kuma wata zuciyar ta hana ta dan tasan halin Saif duk tayi kuskuren k'in binshi ba zai sake dawowa ba sai dai ta kai kanta,
Nasiha sosai Mahaifiyar Huda tayi musu Hajiya Ramatu sannan ya ɗauki matarshi suka nufi gida,
WASHE GARI..........
Ziwww (vibration) kake ji wayar Saif dake saman bedside drawer tana yi,
Daker ya mika hannu ya ɗauki wayar saboda nauyin bachi da yake ji,
Huda na kwance saman kirginshi, ba tare daya duba mai kiran ba yayi picking ya kara a kunne,
Bansan mi akace mishi ba na dai ya buɗe ido da sauri ya zabura wadda har yayi sanadiyar tashin Huda “What?”
Abinda ya furta kenan yana kokarin saukowa saman gadon,
Tashi yayi tsaye yana faɗin “Ok gani nan zuwa”
Nan ya kashe wayar ya ɗora ta saman mirror,
Kallon Huda yayi dake mika ya sakar mata murmushi.
Bathroom ya nufa, a gaggauce ya watsa ruwa ya fito
Wardrope ya nufa ya shirya cikin kanana kaya Black Jean and white t-shirt anyi mata zane blue,
Huda dai sai kallonshi take ganin yana kokarin saka takalma yasa ta tashi zaune tare da jan bargo ta rufe jikinta,
“Dear wai lafiya dai?”
Dagowa yayi ya kalleta
“Wani ɗan aiki ne ya taso”
Fuskar mamaki tayi,
“Yanzu da safe nan dear yau fa weekend kuma ko breakfast bakayi ba”
Rika ta yayi ya kwantar saman gadon
“Cigaba da bachi ki i will be right back ok?”
Kiss ya manna mata saman goshi ya shafa fuskarta ya fice,
Cikin yan mintuna ya isa gidan, a parlor ya tararda Dr. Salamatu tare da wata budurwa da bazata wuce sa'ar Minal ba.
Dr. Salamatu na ganinshi ta tashi tsaye da sauri hawaye na bin fuskarta,
Gurin ya samu ya zauna zaiyi magana ta riga shi
“Saif bani da wadda zan kira ya taimaka min sama da kai Saif yata zata iya shiga cikin wani hali bani da kowa sai ita, ita kaɗai na haifa Saif ka taimaka min karna rasa ta dan Allah”
Cikin kuka ta k'arasa maganar har muryarta na rawa,
Kanshi ya shafa ya sauke ajiyar zuciya,
Sam bai jidaďin yadda ya tararda Dr.Salamatu tana kuka ba ko kađan baya son kuka ko na yaro balle babbar mace,
jin kukan nata yayi yawa yasa ya ɗago kai ya kalleta “Yanzu ya kike so nayi?”
Da sauri buduwar ta kalleshi tace
“Koma minene kayi mana ka taimaka mana”
“Tana ina yanzu?”
“Tana Airport munje bamu samu ganinta ba ance Kasar zata bari kuma kaga zata iya shiga ko wane irin hali tunda zuciyar ta a rufe take”
Wannan karon Dr. Salamatu ce take maganar cikin kuka,
Shiru yayi ya tsurawa carpet ɗin ido har na tsawon lokaci...
Can wani tunanin yazo mashi da sauri ya tashi ya fice ba tare da yace dasu komai ba.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!
NA
KHADEEJA CANDY
_Vote me on wattpad @khadeeja _candy_
BABI NA SHIDA___6
Cikin yan mintuna suka isa,
Sara na yin parking ta kalli Munal Minal suka tuntsire da dariya, da gudu suka fita motar suna a rigaggan shiga cikin gidan.
Minal ce ta riga kaiwa tsakiyar parlor, tsayawa tayi tana juyi da dariya,
“I really don't know how much I miss this place”
Kai Sarah ta girgiza daidai lokacin da k'arasa kusa da ita,
“Maybe a million”
“Nope” Minal ta faɗa tana juya ido,
“Thousands”
“Nope”
Sarah ta zauna saman kujera tana faɗin
“Oops you really don't missed it at all”
Faɗawa Minal tayi saman kujerar tana dariya,
BAYAN AWA UKU...
Minal ce jingine jikin windon kitchen tana kallon flowers,
Wani iska ne maidaɗi yake kaɗawa sai faman sauke ajiyar zuciya take tana.
Sarah na jingine jikin kofa, tana kallonta ba tare da ta sani ba,
“Mil Deen ya faɗa min kinyi kokarin kashe kanki kuma kin gudu kin zo nan ba tare da sanin kowa ba miyasa?”
Kamar daga sama Minal taji maganar, da sauri ta juyo ta kalleta,
Can kuma ta ɗauke kai ta ratsa gefenta ta fice daga kitchen ɗin
Rufa mata baya Sarah tayi tana faɗin,
“Nima baki son faɗa min ko.?”
Tsayawa Minal tayi cak. Ganin hakan yasa ita ma Sarah ta tsaya bata k'araso kusa da ita ba,
“Deen ya faɗa miki komai Sarah”
Ba tare data juyo ba take maganar,
Sarah ta ɗaga mata kai
“Eh ya faɗa min baki son maganar”
Juyowa Minal tayi idonta cike da hawaye, da yaren faransanci tace,
“Wadda zan Aura ya guje ni, kuma matar da nake zama tare da ita take kulani tana yi min gata ashe ba ita bace Mahaifiyar data haife ni ahalin da nake yanzu ban san waye Mahaifina ba basan a ina iyalina suke ba bani da kowa ni kaɗai nake”
Sanyi jikin Sarah yayi ganin yadda hawaye ke zuba a idon Minal,
K'arasowa tayi kusa da ita ta rungume ta.
“Shhhhh ki daina cewa baki da kowa bai kamata ki damu ba har yanzu ba ke kaɗai kike ba muna nan tare a koda yaushe ni ina nan a tare dake Deen ma yana tare dake kuma ba zamu taɓa rabuwa ba”
Maganar take tana buga bayan Minal alamar lallashi,
Sun daɗe a haka kamin Minal ta sake ta, ta wuce bedroom.
Fridge Sarah ta nufa bayan ta buɗe ta ɗauki wata farar kwalba ta nufi ɗakin da Minal ta shiga,
Zaune ta tararda ita tsakiyar godo idanunta a rufe ta dafe kai tana girgiza shi.
Kwalbar Sarah ta mika mata “U need a fresh brain Mil”
D'agowa ta fara yi tana kallon kwalbar kamin ta mika hannu ta karɓa,
“Thank you”
Ta faɗa tana lumshe idanunta da sukayi ja saboda kuka.
Murmushi tayi mata “Your welcome”
Ta kai hannu ta ɗauki car keys dake saman drawer, ta nufi kofa tana faɗin,
“I'm out”
Kai Minal ta ɗaga mata,
“Ok take care”
“I will” Ta faɗa tana kokarin rufe kofar.
Minal sai da taji tashin motar sannan ta buɗe kwalbar ta dagata sama ta kafa a baki,
Bata dire ba sai da taji babu gurin iska a cikinta sannan ta sauke kwalbar tana haki,
Nan da nan wasu ruwa suka tarar mata idanu,
Kai ta girgiza jin jirin da ya soma ɗi banta, tafi minti biyar a haka sannan ta sake kai kwalbar a baki ta shanye ragowar.
D'aga kwalbar tayi sama tana kakkaɓewa daga bisani ta jefar da ita,
“Oh i need more”
Cikin magagi tayi maganar kamar mai jin bachi, tana kokarin mikewa tsaye,
Sai da ta kai tsayen jiri ya ɗubeta ta faɗi kwance saman gadon,
wani irin numfashi ta rik'a ja tana juya ido har bachi yayi gaba da ita.
21:42GMT......
Saif ya sauka masaukinsa sai da ya huta sannan ya shiga bedroom ya sakarma kanshi shower yayi alwala ya fito,
Wani farin yaɗi ya saka marar nauyi, ya shinfiɗa carpet ya kabbarta sallah,
SOME MOMENT LATER....
Kwance take saman gado bayan ya kare cin abinci, sai faman gyasa yake yana shafa ciki,
Babu wadda ya faɗo mashi a rai sai Huda da sauri ya tashi ya ɗauko wayarshi daman tun cikin jirgi ya chaja sim.
Nan ya shiga saka number Huda, ringing tayi ta yi sai da ta kusa hankewa sannan aka ɗauka,
“Hello dear”
Shiru tayi har sai da ya ɗauka ta katse, sannan tace
“Kaga yarinyar da kaje nema?”
Cige bakinshi yayi,
“Wace yarinya kuma? Mi kike nufi ne?”
ciki da mamaki yayi maganar,
“Oho ni ina na sani Dad dai yana son magana da kai”
Tashi yayi daga kwance da yake zuwa zaune,
“Ina Dad ya ganki?”
“Gidan naje ɗazu bayan fitarka”
A takaice ta amsa mishi, faɗa ya shiga mata
“Wa kika tambaya da zaki je? Ba zaki zubar da halinki ba ko? Kuma kinsan... -”
Shiru yayi jin ta katse wayar, yayi murmushi jin haushi,
“Lallai yarinyar nan yayi miki kyau”
Ya daɗe tsaye yana girgiza kai kamin ya shiga danna ma number Dad calling.
Cike da fargaba yayi sallama, bayan Dad yayi picking, bai amsa Sallamar ba ya haushi da faɗa,
“Me kaje yi a new york? Kayi yimin karya kayi ma matarka karya kace nine na aike ka sai ka faɗa min sakon da na aikeka karɓowa”
Shiru Saif yayi ya rasa abinda zai ce,
“Baka ji nane kayi min shiru mi kake son maida kanka?”
Nan ma shiru yayi yana jin faɗan har cikin ranshi,
faɗa sosai Dad yayi mishi sannan ya bashi umarnin barin kasar gobe da safe,
Jiki na kwari Saif yayi mishi Sallama, ya faɗa saman kujera yana busar da iskar bakinshi,
“Ni mi ma yasa na kiraki?”
Tsaki yaja,
“Wallahi ba ki da kirki ko kaɗan”
Nadama yake sosai na kiran Huda da yayi, ya daɗe zaune gurin yana tunane tunane daga bisani ya tashi yayi shirin bachi.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!
NA
KHADEEJA CANDY
_Sadaukarwar ta Anty Maijidda ce_
_VOTE ME ON WATTPAD @KHADEEJA _CANDY_
BABI NA BIYAR___5
Direct Asokoro villa ya nufa, yana yin parking ya nufi part ɗin Dad,
Tsaye yayi lokacin daya isa bakin kofar ɗakin ya shiga kwankwasawa da sallama cike da adabi,
“Waye ne?”
Daga can ciki aka amsa mishi,
Jin muryar Momi yasa ya tura kofar ya shiga a hankali
“Nine Momi”
Fuskar mamaki Momi tayi “Lafiya kayi mana sammako haka?”
Kusa da ita ya zauna ,
“Lafiya kalau wata alfarma nazo nema gareku”
Dad dake shan tea ya kalle shi
“Alfarma kuma wace irin Alfarma kake nema?”
Sai da ya nisa sannan yace
“Dad So nake ka bada umarni tsayarda duk wani jirgi da zai tashi daga yanzu zuwa nan da karfe goma sha biyu”
Daga Momi har Dad kasa fahimtar shi sukayi
Momi tace
“Miya faru Matsalar tsaron ne ko me?”
“Babu ko ɗaya Momi yanzu Dr. Salamatu ta kirani tana kuka tace na taimaka mata karta rasa rayuwar yarta tana son guduwa ne tabar kasar.
Shine nake son ka hana tashi da jiraje idan na kwace passport ɗinta sai komai ya cigaba”
Kai Dad ya girgiza
“Bazan maka haka ba Saboda ya ɗaya tilo a hana dubun mutane yin abinda suke so”
Rokon shi Saif ya shigayi,
“Dan Allah Dad ka taimaka min ba dan kowa zakayi ba sai dan ni, Dad zata iya shiga ko wane irin hali idan ba'a hanata tafiyar ba, yanzu Dad idan Safiya ce ya zaka ji?”
Dafashi Momi tayi
“Saifullah Safiya ba zata yi abinda wannan yarinyar tayi ba wannan ina tunanin bata da hankali ko kuma tana share share-”
Tarar numfashinta yayi
“No Momi ba haka bane akwai abunda mahaifiyar ta tayi mata ne”
Juyowa yayi gurin Dad yana mishi magiya
“Dad Please do this favor for me na riga na faɗi haka zansa ayi dan Allah karkasa naji kunya ka bada umarnin”
Dad yace
“Kai ke da ikon kasar ne da zaka ce haka za'ayi?”
Tasowa Momi tayi ta dawo kusa da Dad ta zauna cikin lafazi mai alamar tausa ta soma lalla6ashi,
“Ka taimaka mishi karya ji kunya tunda har ya faɗa, yana nufin yana da matsayi a gurinka”
Shiru Dad yayi na tsawon lokaci, kamin ya janyo waya ya bada umurni yin hakan,
Godiya sosai Saif yayi mishi sannan ya tashi ya fice suka bishi da kallo,
Gudu ya rik'ayi kamar zai tashi sama cikin yan mintuna ya isa Airport ɗin,
Kai tsaye gurin da ake tantance fasinjoji ya nufa, tun kamin ya k'arasa ya rik'ajin sanarwa an hana tashi da jirage na wani ɗan lokaci,
Yana isa gurin duk suka tashi tsaye suka sha jinin jikinsu, hannu suka bashi bayan sun gaisa ya kalli babban su,
“List ɗin passenger da zasu tashi nake so”
“Ok Sir”
Nan ya kalli na gefensa
“A kawo mishi list”
Da sauri mutumin ya juya ya nufi wani ďan tebur dake kusa da su
Cikin yan mintuna ya kawo mishi files kusan guda goma sha biyu,
Wayarsa ya ciro cikin aljihu ya danna kira ana daukar yace
“Minene full name ɗin da take anfani dashi”
Can naji yace ok ya kashe wayar,
Wadda ke rike da files ɗin ya kallah
“Duba min Amina Alhassan Minal”
Jiki na rawa yace,
“Ok Sir bari musa a computer yafi sauki”
Kai kawai ya ɗaga mishi yaja kujera ya zauna,
Ana saka sunan nan take computer ta nuna har da ɗan karamin pic ɗinta,
Juyowa yayi ya kalli Saif
“Sir gata amman tana cikin fasinjoji da suka tashi”
da dauri ya yashi tsaye
Da karfi Saif ya furta
“What bayan an faɗa muku karku bar jirgi ko ɗaya ya tashi.? Mi kuka aikata kenan a baku umarni ku tsaɓa me kuka dauki kanku sai kunyi nadamar abunda kuka aikata”
B'ari jikinsu ya shigayi ko wanne cikinshi ya ɗori ruwa, ɗaya daga cikinsu ne yayi kokarin yin magana
“Yan laɓai ayi hak'uri koda aka bada umarnin hana tashi da jirgi jirginsu yayi minti talatin a sama kuma kasan idan jirgi ya riga ya tashi babu yadda za'ayi a tsayar da shi”
Shiru yayi ya jingina da gurin, can ya kalleshi
“Ina jirgin ya nufa?”
Cikin sauri ya bashi amsa
“New York”
“Akwai jirgin da zaije can yanzu?”
Saif ya Tambaya
“Babu shi yanzu Sir sai dai anjima da maraice karfe hudu abinda yayi kasa”
Kai ya ɗaga musu ya tashi ya fice.
Driving yake yana danna calling ana yin parking yace “Dr. Salamatu jirgin su Minal ya riga ya tashi nasa an tsayarda tashin jiraje amman already nasu ya tashi”
Shiru ya ɗanyi sannan yace
“New York ta nufa eh i will try my best nan da 6 hours zan isa can zanyi wani abu akai insha Allah”
Yana kashe kiran ya sake danna wani kiran
“Hello Hashin ina son kujera ɗaya daga cikin kujerun da zasu je New York anjima, no yanzu akwai inda zanje karka yarda nayi missed flight”
Yana kaiwa nan ya danna red bottom ya karama motarshi jiya.
3:11PM......
Ya shigo gida da gudu Huda ta tareshi,
“Dear tun safe sai yanzu?”
Kiss ya manna mata a gefen kumatu
“Am so sorry dear wani ɗan aikin ne ya rik'e ni”
“Dear wai wane irin aikine yau fa Weekend”
Zaunarda ita yayi saman kujera
“Meeting mukayi da wasu Indian yanzu ma new york zanje”
“Wasa dai kake ko?”
Tashi yayi yana faɗin
“Allah da gaske wani aikin ne ya taso”
Bedroom ɗinshi ya nufa nan itama ta tashi ta rufa mishi baya,
Koda ta shiga ta tararda shi yana cire rigarshi, ido ta bishi dashi har ya ɗaura tawul ya shiga bathroom,
Gefen gado ta samu ta zauna ta zubawa bathroom ɗin idon har ya gama wankan ya fito,
Wardrobe ya nufa, ganin yadda ake kallon shi yasa ya sakar mata murmushi
“Wai wannan kallon na lafiya ne?”
Bata ce mishi komai ba har ya goge jikin shi ya shafa mai yana kokarin saka tufafi tace
“Wai da gaske tafiya zakayi?”
“Gashi kina gani karfa ki ɗaga hankalinki ba dadewa zanyi ba”
Ya k'arasa maganar tare da ɗaukar turare yana fesawa a jikinshi.
Juyowa yayi ya kalleta yadda ta wani haɗe rai sai yasa shi yin murmushi ya fesa mata turaren a gefen wuya ya zauna kusa da ita
“Wai minene na wannan fushin my heart?”
Kamar ta fasa kuka “Toh dear kaje new york ɗin dani mana ko kuma ka bari har wani sati”
Dariya yayi
“Ai ba zai yiyu ba idan ma yawo kike so toh ki bari har na dawo sai muje duk inda kike so”
A gogon hanninshi ya duba da sauri ya tashi tsaye
“Kai kinga har 3:40 tayi kuma 4 zamu tashi”
Bedside drawer ya buɗe ya ɗauki wasu abubuwan da yasan zai bukata ya saka a wata yar karamar jaka
Hannunshi ta riko cikin yanayin damuwa
“Dear ko dai baka hak'ura bane?”
Hannun nata ya manna ma kiss
“Na hak'ura mana ai da bazan barki