Showing 66001 words to 69000 words out of 115850 words
Chapter 23 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
ya ganshi sai a ɗauka yayi wata tara saboda girman da yayi,
Sai dai kuma wata matsalar ɗaya, ciwon ta a yanzu yafi na da, dan zubar jinin sosai take yinsa abun har ya fara ba likitocin tsoro kusan kullum sai an sa mata jini, gashi a yanzu har hannu take sawa ta cika shi da jinin dake mata zuba a hanci,
Yau ma Saif na shigowa ya ga ta cika hannun da jini har da sare, tasa ya ɗauko ya tara mata ta zuba jinin ya shiga gyara mata jikints jinin na kara mata zuba,
Ita kanta taji tsoron yadda taga zubar jinin yau daman ta daɗe da sadakarwa tasan ba zata tashi ba, ganin tsoron dake fuskarta yasa Saif ya rumgume idonsa taf da hawaye,
“Za ki ji sauki Minal okey karki da ta hankalin ki”
“Dan Allah Saif ka Auri Kairat marry her and make her happy ta yadda zaku kula min da abunda zan haifa,”
Ya ɗago fuskarta
“Haba Minal taya zan aure ta ina auren ki ? Ba zan sake yin wani auren ba dake zan zauna har a bada”
“Ba zamu yi irin wannan zaman ba Saif mafarkin mu ba zai taɓa tabbatuwa ba,
And Saif ka faɗawa Kairat ta kula min da Mummy da Baby na”
Hawayen dake idonsa suka zubo sai kawai ya samu kansa da wani irin kuka kamar mace, hannu tasa ta shafi fuskarsa
“Saif I love you I love you so much, If there ever comes a day when we can’t be together, keep me in your heart, I’ll stay there forever”
Ganin tana kokarin zauta shi yasa ya sake ta yana share hawaye,
“Bari na kira Dr”
Rike shi tayi
“Karka je Saif ina jin daɗin rumgumar nan da kayi min ina jin wani sanyi yana ratsa ni, Saif ka cigaba da nema min gafarar ubangijina ko da bayan mutuwa ta kuma kace Mummy ta yafe min, idan ka ga Mahaifina ka tambaye shi mi nayi masa ya gudu ya bar mu ni da Mummy na? Kace masa wace riba ya ci?. Saif ka nunawa ɗana kabari na ka karanta masa kyakkyawan tarihina ka ɓoye masa mummuna ka sashi a jikin ka ka nuna masa so kaji? Kar ka masa irin abunda mahaifina yayi min,
Saif ka faɗawa Deen na yafe masa kuma ina sonsa yana nan a matsayinsa na aminina Saif ka rika tunawa dani kaji ka rika yi min addu'ah”
Ture ta yayi da karfi
“Ya isa Minal ya isa”
Ya juya ya fita yana hawaye ya kira Dr. Hankalin Dr ya tashi sosa ganin yanayin ciwon nata a yau, cikin sauri ya rubuta mata wani magani wanda zai tsayar da zubar jinin,
jiki na rawa Kairat ta siyo maganin, dan Mummy da Saif hankalin su a tashe yake komai basa iya wa,
ana kawo maganin likitan ya bata ta sha, yasa wata nurse ta gyara mata jikinta Saif kuma ya hau saman gadon ya rumgume ta yana shafa kanta.
ba ayi minti goma sha biyar da shan maganin ba jinin ya ɗaina mata zuba, sai dai kuma suka nemi numfashinta suka rasa ga idonta yana motsi amman ba numfashi, a nan hankalin likitocin ya kara tashi da sauri suka canja mata gado suka nufi wani ɗakin da ita suka sa mata abun neman numfashi suka saita numfashin da computer suna dannar kirginta, amman ina mai kira yayi kira manzo mutuwa mai gaggawa idan lokaci yayi ba tsaya wa,
a nan suka ga ta kangare ido tana motsi da baki kaɗan-kaɗan.
*** *** ***
Su Mummy na tsaye cirko-cirko suka ga likitan ya fito, kallo ɗaya yayi ma Mummy tausayinta ya kama shi, yasan yadda Mummy take son Minal dan shine likitan da take kula da Minal tun tana karama yasan yadda hankalin Mummy yake tashi duk lokacin da ciwon ta ya tashi,
yanzu taya zai iya faɗa mata mutuwar ta! Su kuma sai kallon shi suke sun kasa tambayarsa ya ake ciki.
Suna haka wani likitan ya fito daga ɗakin yana faɗin
“Dr. Sulaiman Abunda yake cikin ta yana da rai.........”
Dummmm gaban Mummy ya faɗi idonta cike da hawaye ta kalli Dr
“Ta mutu kenan?”
“Kiyi hakuri mutuwa tana kan kowa kuma idan lokaci yayi ba a tsaya wa”
Wata irin kara Mummy ta saki tana ja da baya, Kairat tabi gini ta sulale kasa zaune, Saif kuma ya nufi ɗakin da sauri yana faɗin
“No no no no nooooo!”
BABBAN GORO 41
Faɗuwa Mummy tayi zaune tana wani irin numfashin tana kallon tiles, da sauri likita ya nufe shi da Kairat, Kairat ta dafa ta,
“Mummy Mummy”
A nan ta ɗago ta kalli Kairat idonta a raunene kamar mai jin tsoro, ta jata jiki na rawa ta rumgume
“Minal my child.....”
Fashewa Kairat tayi da kuka hakan yasa Mummy tayi saurin sakin ta, ta matsa can ta dafe kai ta rumse ido,
Ta ɗan daɗe kamin ta buɗe idon ta kalli kofar ɗakin da Minal take ciki, a nan ta tashi tsaye ta nufin tafiya sai kafafun ta suka kasa ɗaukarta ta faɗi, da sauri likitan ya rika ta yana kiran wasu nurses,
Unkurin ta sake yi a karo na biyu da nufin sake tashi a nan ma faɗuwan tayi dan jikinta yayi ma kafafunta nauyi basa iya ɗaukar ta,
A nan ta soma jin wani kalar abu na daban, zuciyarta tayi mata nauyi kanta ya sara sai ta rika jin kamar mafarki take kalmar Dr ta rika dawo mata _Duk mai rai mamaci ne_ sai a lokacin idonta ya cika da hawaye alamun rashin ya fara fisgarta, kamin ka ce kwabo sai gata tana kuka mai haɗe da dariya,
“You know what? Minal she's always asking me Mummy idan bana nan ya zaki ji! Minal ina ma zaki zo yanzu kiji yadda nake ji....”
Kairat ta matso kusa da ita ta kama hannunta tana kuka mai tsuma zuciya,
“Mummy kiyi hakuri haka Allah yaso”
Fashewa Mummy tayi da kuka
“Mutuwa baki kyauta min ba, Minal ita kaɗai ce farin ciki na ita ce family na ita kaɗai na mallaka a duniyar nan miyasa zaki ɗauke ta ki bar ni bayan ni nafi dacewa dake haba mutuwa haba mutuwa....”
Rufe mata baki Kairat tayi tana girgiza mata kai,
A nan ta mai dubanta gurin Kairat
“Kin ga Minal ta tafi ta bar ni ko!......"
Shiru tayi tana kallon tafin hannunta, zuwa can ta sake kallon Kairat tace
“But never mind i will take good care of her clothed and her room so that I can be with her again I will always....... ”
Sai kuma tayi shiru tana kallon yatsun hannunta hawaye masu zafi na mata zuba,
“She's will come back to me very soon”
Ta faďa tana fisgar gyalenta tana kuka.
Yanayin kalamanta da kuma abunda take ya tabbatar ma da likitan tana kokarin barin hankalinta ne, A nan yasa wasu Nurse suka ɗauke ta aka ɗora ta saman kujera suka nufi wani ɗakin da ita sai surutai take...
*** *** ***
Kamar mahaukaci Saif ya shiga ɗakin, ya nufe ta da sauri ya shiga girgiza ta
“Minal Minal Minal Minal wake up!”
Da wani irin karfi yake girgiza fuskarta, zafafan hawayen dake masa zuba na ɗiga a saman kumatun ta, ganin bata motsa ba ya hannunshi ya matse mata baki
“Talk to me Minal Saif ɗin ki ne please Minal please”
Ya faɗa yana taɓa lips ɗinta da wani irin karfi. A nan wata nurse ta nufo shi ta ɗafa tana janshi baya
“Kayi hakuri ta riga ta rasu iya.......”
Bata karasa maganar ba ya kai mata wani mugun haushi nan take bakin nata ya fashe da jini, ba shiri ta fasa ihu tayi waje da gudu.
Hannu yasa ya tallafo kan Minal ya rumgume ta tsam-tsam a kirginsa kamar mai rai yana kuka
“Please Minal karki Min haka kin san bamu taɓa irin wannan wasan da ke ba, Minal wake up please ko dan babyn mu kin san Mummy tana son ki how can go and leave her! Im still here”
Dukowa yayi dai-dai ita ya haɗa fuskarta da tasa hancinsa yana gugar nata yadda ya sata mata lokacin da take raye,
“I love you Minal...”
A hankali ya faɗa idonshi a lumshe yana goga mata hancinsa hawaye na mishi zuba, yasan da tana da rai da yanzu ta shafa kanshi ko ta mayar masa da amsa.
Hakan yasa ya sake ta yayi baya yana kallon fuskarta kamar wanda yaga wani abun tsoro ya fashe da wani irin kuka yasa yatsunsa cikin gashin kansa yana matsar gashin da kokarin buga kansa a ginin ɗakin.
Daga likitocin har nurses ɗin babu wanda yayi unkurin yi masa ko da magana balle ma taɓa sa sai kallonsa suke.
Shi kuma kuka yake ba kakkautawa kamar karamin yaro, can kuma ya tashi tsaye da sauri kamar wanda akayi ma shocked ya bar ɗakin da gudu,
Duk gun da yabi kallon sa ake har ya isa parking space, bana jin yasan lokacin da ya buɗe motar ya shiga har yayi mata key, sai da ya tsinci kansa a saman ti-ti sannan ya fara tunanin ina zai je?
_Gida gurin Momi_ Wata zuciyar ta bashi amsa a nan ya kara gudun motarsa kamar mai wasan tsere ya danne sitari da hannu ɗaya babu ruwansa da wanda ke kan ti-ti sai dai idan kai kaso rayuwar ka ka kauce ba dai shi ya kauce maka ba.
Yadda masu gadin gidan suka ganshi yasa suka tak'a masa bingigoginsu, ganin yadda ya nufo gate ɗin da gudu abunda suka san bai saba yi ba, abu ɗaya ya gana du buɗe masa wuta sanin Motar Saif ce basu sani ba ko shi ɗin ne sai dai suyin shirin ko ta kwana,
Wata mahaukaciyar horn ya danna musu amman ba su buɗe gate ɗin ba ganin yadda suka yi ciro-ciro suna kallonsa yasa ya buɗe Motar ya fito ya nufi cikin gidan yana kuka kamar mai sauti kamar mace.
Yanayin yadda ya turo kofar falon yaba Mummy tsoro, bata kara katsewa ba sai da ta ganshi yana kuka, tun kamin ya karaso kusa da ita ta nufe shi tana tambayar ba'asi,
“Subhanallahi lafiya? Miya same ka haka?”
Hannayensa ya shiga nuna mata yana wani irin kuka mai karfi
“Momi Min....”
Muryarsa ce ta sarke ya kasa karasawa saboda kukan da ya taushe masa zuciya. Cike da tsoro Momi ta dafa shi tana faɗin
“Mi ya same ta mi ya samu Minal ɗin?”
“Momi ta .....ta..t....”
Kin fitowa maganar tayi, ya faɗi kasan tile yana maida numfashi ya fashi da wani irin kuka mai karkarwa da kara ya kai ma tile ɗin wani mugun naushi.
“Innalillahi wa inna Ilaihirraji'un”
Shine abunda Momi take ta maimaitawa tana jimama mi ita a zaton ta ko ba'ace abunda yake cikinta ya samu matsala ba ita ba sai.
Da sauri Lubna ta fito daga ɗakinta ta nufo gurin da suke, bata tambayi miya faru ba dan yanayin da taga ɗan'uwanta tasan mutuwa ce kawai zata iya sashi shiga cikin irin wannan halin,
Nan itama na ta idon suka ciko da kwallah a hankali ta risina ta dafa ɗan'uwan nata tana masa kallon tausayi.
A firgice ya ɗago suna haɗa ido ya rumgume yana kuka ɗa faɗin
“Lubna Minal Minal Minal”
Kukan suke daga ita har shi har Momi babu mai ba wani hakuri.
*** *** ***
Zaune take guri ɗaya tana rusa kuka kuka ne wanda ake cewa shi ke zuwa da kansa shi yake yin kansa, kukan take ji yana zo mata ta ko'ina zuciyarta ta faɗa tayi kasa jijiyar kanta ta taso idanunta sun kumburo majina sai tsiyaya take mata,
“Kuka ba shi da muhimmaci a gare ta yanzu addu'ah take so”
A hankali ta ɗago ta kalli Doctor sai kuma ta kara rushewa da kuka.
Ajiyar zuciya ya sauke ya mika mata wata farar takarda mai rubutu,
“Baby da yake cikinta yana da rai shi muke son muyi tiya ta mu ciro dan haka muna bukatar sa hannun ki tun da Dr. Salamatu hankalinta baya jikinta, Saif kuma ya bar asibitin”
Kamar bata ji abunda yace ba ta cigaba da rera kukan tana wani wahalallen numfashi
“Urgent ne Kairat, sign to save yours sister child....”
Hakan da yace mata sai yasa kuka nata ya tsagaita kalmar shi ta tuna mata da maganar Minal lokacin da take exercise a falo garin kallon Tv ta tashi faɗuwa sai a kayi sa'ah Kairat ta kawo tayi saurin tare ta tana faɗin
“Glad i save you”
Sai ita kuma tayi Murmushi ta kalli Kairat tace
“You will always save me and my family Kairat put this in your heart...........”
Hannu ta kai ta dafe zucuyarta hawaye na zubo mata a hankali,
“Kairat ke muke jira”
Kiran da yayi mata yasa ta ɗago jajayen idanunta ta kalli paper, still hawaye na mata zuba ta mika hannu ta karɓi pen ɗin da nufin signing.
Hello my people naga addu'o in ku naji daɗi kuma na gode sosai mamana taji sauki thanks all for your prayers I really appreciate it Allah bar zumunci, Keep your eyes open i always update Insha Allah just keep vote and comment on every line thanks for the love heart you all
HAFSAT AHMAD wannan Shafin na ki ne kedai bless you dear
BABBAN GORO 42
Assalamu Alaikum readers of ™BG i want to use this opportunity to say something hope za ku ba ni aron hankalin ku! I know we are writing to entertaining, but we have to touch the reality, ina son duk mai karanta littafan KHADEEJA CANDY ya rik'a sawa a ransa kamar gaske ne yake faruwa saboda ina tafiyar da littafai na ne akan abunda hankali zai ɗauka.
Na samu messages ɗin readers wasu like karki kashe mana Minal please. wasu like idan kika kashe ta kin ɓata Novel ɗin ki. wasu like ni ban taɓa ganin inda aka kashe star a Novel ba. Wasu idan kika kashe ta me kika yi kenan. wasu like bai kamata Minal ta mutu ba. wasu like Please ki ce dogon suma tayi and list goes on and on and on and on and on......
Haba dears! Yanzu dan Minal tana star a Novel sai a ce ba za mutu ba? Ke yanzu dan ana sonki a gidan ku sai ace ba zaki mutu ba? Ki rika sawa a ran ki kamar ke ce ko kuma wata ce hakan yake faruwa da ita, wasu na cewa wai Minal bata ji daɗin rayuwa ba ya kamata ace taji daɗin rayuwa kamin ta mutu ina son ku koma baya ku karanta gurin da kuka manta, Minal tayi rayuwa mai kyau kuma ta jindaɗi Mummy ta nuna mata gata sosai har hakan yasa ta fara shaye-shaye babu wanda ya isa ya tsaya ya faɗa mata wata magana ta kyale shi remember? daga lokacin da ta fahimci bata da uba ta soma fuskantar bakin ciki a rayuwarta, masu cewa ya kamata ace ta gana da mahaifinta ba duka abunda mutun ke so yake samu ba, Nasan wata mata da iyayenta suka yi auren kasa da kasa babanta ɗan Najeriya mamanta yar Ghana sai suka rabu tana karama lokacin da ta girma ta mallaki hankalin kanta sai ta nemi ganin mahaifiyarta haka ta haɗa kuɗi motar ana sauran kwana uku ta tafi aka kira aka faɗa mata mamanta ta rasu kuma bata taɓa ganin mahaifiyar ta da ido ba, image idan Novel ne sai a ce bai yi kyau ba right? karku manta Mahaifin Minal shi ya wulakanta ta da kan shi, akwai masu cewa taya za ace Minal ta mutu ta bar Mummy bayan ita kaɗai ta mallaka a duniya da ace reality ne da nace mu ku haka Allah yake ikonsa idan yaga dama akwai wanda har ya gama rayuwar sa ba zai taɓa ganin jininsa ba akwai wata friend ɗita maybe wasu daga cikin kun sun santa ana ce mata Hannatu Ismail tana daf da kare karatun ta Allah ya karɓi abarsa kuma ita kaɗai iyayenta suka haifa sun ɗora mata buruka da yawa babu irin jindaɗi da bata yi a gidan su amman mutuwa ta kutsa ta ɗauke ta toh haka rayuwa take muna cikin sha'anin mu take ɗauke mu. ya kamata mu rik'a kula da irin wannan, na fahimci wasu suna karanta Novels ne kawai da nishaɗi kalilan ne ke karanta su fahimci sakon da abun ke son isarwa ko kuma darasin dake ciki.
Idan a reality ne kuna ganin mai ciwo irin na Minal zata rayu? No way duk da nasan rayuwa a hannun Allah take karku manta the Doctor said mai blood cancer leukemia in dai yayi Cronin they can't survive kun tuna? sannan ku koda yaushe ace dogon suma a Novels always in reality hakan yana yawan faruwa? No nasan ita ce ansar! To haka zaku rika sawa a zuciyarku idan kuna karantawa after that akwai Kairat, Huda, Safiya, Saif duk suna raye only Minal is gone and she has to, bari na tsaya a nan kar wasu suce na cika surutu i says a lot, anyway thank you for your time i really appreciate your efforts ina fatar za ku fahimci bayanin nawa zaku kuma tuna abunda kuka manta. I heart you all stay bless all the best one heart one love 😍 happy reading👌🏿
42
Kairat nayin Sign ya juya da sauri ya shiga ɗakin da take, tare da taimakon nurses da wasu likitoci aka shiga da ita ɗakin tiyata, a kofar ɗakin tiyatar Kairat ta tsaya tana safa da marwa hawaye na mata zuwa tana jiran a fito da ita kashe kunne tayi taa sauraro jin take kamar ace mata Minal ɗin tana raye.
Sun ɗauki