Showing 27001 words to 30000 words out of 115850 words

Chapter 10 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

5651

dashi, idan tace baxata ba Minal zatayi tunanin wani abun ne idan kuma taje Minal zatayi tunani wani abun ne kuma, toh ya zatayi.?
Minal ce ta katse mata hanzari, da faďar


“Jeki kace gata nan zuwa”


“Toh”


Da sauri ya tashi ya fice. Kairat ta kalleta


“Haba Minal nace miki zani ne?”


“Amman kinsan Saif yafi karfin wulakanci ko.?”


“Lallai kan Kuma baki san abunda yake tafe dashi cikin daren nan ba”


Talatu ta faďa tana kokarin tashi. Tashi itama Kairat tayi ta nufi hanyar ďakinta, Ta daďe tsaye kamin ta saka hijabinta ta fito.


Tsaye ta hangosa jikin mota sanye da bakar jallabiya ya rumgume hannayesa yana kallon sama kamar mai kidayar taurari,
da sanyin jiki ta karasa kusa dashi, cikin sallama. a hankali ya sauke idanunsa akanta ya kamar mata murmushi.
Bata jira ya amsa tambayar ba ta aika masa da tambayoyi,


“Me kazo yi yanxu da dare nan Saif.? Minyasa kace akira maka ni ? mi zanyi maka.?”


Ido ya kura mata,
“Wace Tambayr zan fara amsa miki”


“Mi kazo yi da dare haka.?”


“Daga gurin Abbah nake wasu file na kai msa shine nace bari na biyo kinsan kusa ne”


Kai ta ďaga masa tana kallon windon falo kamar mai jin tsoro,


“Miyasa kace a kirani Bayan ga Minal.?”


“Ke naga damar kira”


Cikin kakkausar murya ya bata amsa, Nan ta kallesa,


“Abunda kake bai kamata ba Saif”


“Ke kina yin abunda ya dace ne.?”


“Ba haka bane yanzu Minal zatayi tunanin ko wani abun ne”


“Toh sai me dan tayi tunanin kina tsoronta ne?”


“Bana tsoronta”


“Miyasa kike gudun 6acin ranta.?”


“Saboda ina son farin cikinta”


Kai tsaye yake mata tambayoyin tana bashi amsa. A hankali ya gyara tsayuwarsa fuskarsa ba yabo ba fallasa yace,


“Bari na faďa miki wani abu da baki sani ba a kaina Kaiyrat, Bana yin abu a tambaye ni dalili, bana tambaya a maida min tambaya, bana cewa A ace min B ba mai kallon tsakar idona ya faďa min bakar magana, Bana kira a kashe idan bani na kashe ba. Duk abubuwan nan dana faďa kin aikata su na kyale ki ne dan kawai ina mutunta ki and i have something behind your heart, so don't try me again”


Nan ya jefa mata gift ďin dake hannunsa,


“Bana kyauta a mayar min idan kinga dama ki ďauka ko ki jefar”


Bai jira cewarta ba ya buďe motarsa ya shiga, da wani karfi ya fisgeta ya fice gidan kamar kyaftawar walkiya.
Sai a lokacin ta iya yin tsotsin kirki, dan tunda ya fara maganar tayi saranda tana saurarensa. Dukawata tayi ta ďauki gif ďin da aka naďe cikin jar fefa mai zanen heart, ta nufi kofar falo, jikinta sayyaye.
Tana turo kofar falon Minal ta kalleta, Murmushi Kairat ta sakar mata tabkaraso da sauri kusa da ita kamar ba ita ba,


“Minal kinsan meye.?”


Kai ta girgiza mata, Kusa da ita ta zauna tana mika mata Gif đin


“Wai kiran da yayi min danki ne fa kinga abunda ya siyo miki wai tsoron baki yake ji karki watsa masa kasa a ido.”


Da sauri Minal ta mika hannu ta kar6a zuciyarta cike da farinciki,


“Tsorona sai kace wata dodo miye a ciki.?”


“Ai bai yarda na buďe ba wai sai na kawo miki kuma yace na gaishe ki”


Da karfi Minal ta fixge fefar. Kairat gabanta sai faďuwa yake kar Minal.tqga wani abun da zai sa tayi tunanin yana sonta Allah allah take idan bai rubuta sunan ta ba ko wani abu daya danganceta, Da farko batayi niyar bata ba sai kuma tayi tunani idan bata bata ba toh me xata ce mata Saif yazo yi a gida kuma gurinta.


Cake ne cikin kwali mai ganen heart guda shida guri ďaya, ďaya ta ďauka tabkai bakinta ta lumshe idon tana murmushi. Can kuma ta buďe idon ta rumgume Kairat, Dariya Kairat tayi wadda zan iya cewa bata kai ciki ba, tace


“Minal kin jidaďi ko.?”


“Sosai ma”


“Minal kina son Saif ko.?!”


D'agowa tayi daga jikinta tayi kasa da kanta,


“Amman ina jin tsoron kar shima ya juya min baya Bana sin daga baya wata matsalar ta fito yace ba zai zauna dani ba”


Hannu Kairat ta kai ta rika fuskarta, tana murmushi


“Zai soki Minal ba zai barki ba Saif ya banbanta da sauran maza Ba zaki sake bakin ciki ba Minal no more sad, no more tears wadda kikayi a baya is enough idan mutun bai faranta miki ba Minal toh bazai bakanta miki ba”


Sake rumgume ta Minal tayi ta rumtse ido tana sauke ajiyar zuciya,


“Na gode sosai Kairat”


“Don't mention you deserve more”


Kairat ta faďa tana lumshe ido,


“Kuma shima kamar yana sona ko Kairat.?”


Kai ta ďaga mata tana share hawayen da suka zubo mata,


“Sosai ma Minal yana sonki sosai”


Kara rumgumeta tayi cike da jindaďi.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.


NA


KHADEEJA CANDY



Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy




BABI NA ASHIRIN DA BIYU___22


Cike da ɓacin rai ya isa gida. Mamakin kansa yake wai Namiji kamar shi Kairat zata tsaya tana yimai yadda taga dama, wani gurin kuma laifin kansa yake gani tunda shi ya sake mata fuska har taga damarsa.
Da wannan tunanin ya shiga ɗakinsa, Kwance ya hango Huda ta baje saman gadon tana sharar bachi, matsawa yayi kusa da ita ya kura mata ido hannayensa zube cikin aljihu. Zuwa can ya ɗauke kai ya nufi wadurof ya canja kayan jikinsa zuwa na bachi, bayan ya gama shirinsa na bachi ya kashe wutar ɗakin yazo bayan Huda ya kwanta.


* * *


“Mtwssss”


Yaja tsaki, Nasir ya kallesa,


“Wai dan na yi maka sammako kake wannan tsaki.? idan mitin ɗin ne baka son zuwa sai ka na koma na sauke ka”


“No ba haka bane mitin ai ko baka zo ba dole ne naje, kawai wani abun ne yake ɓata min rai”


“Name.? ko san yan jarida sun yaɗaka”


Kallon rashin fahimta Saif yayi masa,


“Sun yaɗani kamar ya wani abun na aikata ne.?”


“Kar dai kace min baka san komai ba!”


“Allah ban sani ba, meke faruwa ne?”


“Aiko kusan jarida nawa ta buga wai kana soyayyah da ya Dr. Salamatu”


Hannu yasa ya dafe kansa, yada soma sara masa yanzu,


“Kai wai yan jaridar nan basu da hankali ne! Su abu kaɗan ya zama na labari Mtwss”


“Wai kana nufin bada gaske bane.?”


“Babu abunda ke tsakanin mu, ni ba sonta nake ba beside ni Qawarta nake so kuma ita ma ta fara bani haushi”


“Baka sonta amman kake kula ta.? Haba Saif nifa ba mutun bane da zaka ɓoye ma sirrinka”


“Allah da gaske nake ni babu abunda ke tsakanin mu, ina kula ta ne kawai dan tana bani tausayi saboda kazantacciyar rayuwar da take, amman ni ba sonta nake”


Murmushi Nasir yayi ya bugu sitarin motarsa,


“Karka ce min baka sonta Saif, baka sonta kake kokarin ɗorata a hanya? Wannan ai kai ba zai ɗauka ba”

Saif ya ɗan fusata,


“Ai sai kayi tayi tunda baza yarda ba”


“Ka yarda kana sonta Saif Tausayi silar so da baka sonta da bazaka iya zama da ita ba koda na minti ɗaya ne, and Saif abunda kake kokarin yi ba xai taɓa yiyu ba Kairat bazata taɓa sonka ba koda tana son ka bazata nuna maka ba,
Saboda taraiyarsu da Minal ta zamo kamar yan'uwa, toh faɗa mi taya Kairat zata so abunda Minal take so?”


Saif ya kalleshi,


“Ce maka akayi tana sona?”


“Tana sonka Saif kuma kaine ka ɗasa mata son a zuciyata, da bata sonka bazaka mata abu ta kyale ka ba, An faɗa min babu wadda ya isa yasa Minal tayi abunda bata tashi ba amman kai kana sata kuma ta daina,
Kai da bakinka kake faɗa min minal tana shaye-shaye tana zuwa club tana mu'a mala da maza yadda kai hakan baya yi maka daɗi, kasan abunda yasa baka jindaɗi! saboda kana sonta, Kairat ta fita hankali da hali mai kyau hakan yasa taja hankalinka har ka fara sonta, Bari na faɗa maka wani abu da har yanzu ka kasa ganewa Saif, Minal ce kake so ba Kairat ba Kairat halinta kake so Minal kuma zatinta kake so da ace Minal zata canja hali, Halinta ya dawo kamar na Kairat, da bazaka sota ba, Toh kaga Minal ce ainihin mace da kake so”


Shiru yayi, ya tattara girar kasa da sama yana nazarin maganganun Nasir. Ganin hakan yasa Nasir ya faka gefen ti-ti, ya kalleshi kana ya cigaba,


“Saif Minal matar aure idan kayi mata kallon tsafta, Zaka iya maidata yadda kake so tunda kana rike da zuciyarta, Idan ka ɗorata a tubar sai ta Kairat natsuwa da cikar kamala, kuma zata rika ganinka da kima ta mutunta mahaifiyarta ma nasan zata jidaɗi zaka buga baban tarihi a rayuwarta, Yanzu isan kaso Kairat idan Kairat ta canja halinta tsanarta zakayi, amman Minal kaga yadda halinta yake kuma kana tare da ita a haka,
Saif idan baka so Minal ba ka zalunce ta, dan kai ne ka nuna mata kulawar da har ta ɗasa mata sonka a zuciyarta, Minal abun tausayi ce Saif, Ta rabu da saurayinta akan bata da uba, yanzu kaima idan ka rabu da ita zatayi tunanin sabod haka ne, kuma zaka ɓata taraiyarsu da Kairat.”


Ajiyar zuciya ya sauke ya lumshe manya idanunsa, ta lumtse labbansa. Nasir ya cigaba,


“Idan ka auri Minal zaka fi samun kwanciyar hankali saboda bata da ishenshen wayo sosai kamar Kairat, amman kaga ita bom ne zaka haɗa tsakaninta da Huda babu wadda zai kyale wani kaga anyi ba ayi ba kenan”


A hakali ya buɗe idonsa ya kalli tsadadden agogon hannunsa yace


“Ja Mota muje kar muyi latti”




*** *** ***






Kukanta daya jiyo.ya haddasa masa faɗuwar gaba tun kamin ya karaso cikin falon, Da hanzari ya karaso kusa da ita ya zauna jikinsa na gogar nata,


“Lafiya kike kuka waya mutu.?”


Da jajayen ido ta kalleshi,


“Ni kan da mutuwa ce.da ta fimin sauki sama da abunda naji kuma na gani”


Bayanta ya shafa, alamar rarrashi


“Toh faɗa min minene”


“Saif mi kaga a jikin Minal da ni bana dashi har ya ɗauki hankalinka kake sonta ? a da na ɗauka zance mutane sai yanzu na tabbatar tunda har a jarida an faɗa wai ynzu kana daf da aurenta, saboda ta ɓata da saurayinta saboda kai Saif miye bana maka?”


Bushewa yayi da dariya, hakan yasa ta kara fusata, daker ya iya saita kansa ya kalleta


“Wallahi kina burgeni Huda kin iya kishi kamar a shirin fil ko kuma littafin marubuta, Toh miye na zama kina zubar da hawayenki a banza wai zanyi aure, nifa Mijin mace huɗu ne ni banga abun kuka a ciki ba duk kinbi kin haɗa wannan zufar”


Tashi tayi tsaye tana masa kallon tsana,


“Da gaske ne kennan.? aiko Saif da kayi min butulci”


“Butulcin mi Huda na taɓa miki alkawarin bazan yi maki kishiya bane”


Harara ta watsa masa ta shige ɗakinta. Shi kan ko ajikinsa dan baiga anfanin kukan ba, shi dai yasan bazai mata alkawarin kin aure na tunda yana niyar yinsa ko da ba yanzu ba.
Ruri wayrsa tayi alamar kira, Number Minalya gani, sai da tayi ringing kamar zata katse sannan ya ɗauka, Zazzakar muryarta ta daki dodon kunnensa,


“Assalamu Alaika”


Sallamar da tayi tasa yaji kuzarin amsa mata,


“Wa'alaikissalam”


“Saif ina son magana da kai, oh sorry ya Gida?”


“Gida lafiya kalau faɗi maganar ki”


“A'a ba a waya zan yi ba ina son kazo gida yanzu”


Shiru yayi, kamar ba zaiyi magana ba, jin haka yasa ta marairaice masa murya kamar mai shirin yin kuka,


“Saif dan Allah wata magana zamuyi”


“Ok gani zuwa”


“Thank you sai kazo”


Kashe wayar yayi ya tashi ya nufi gurin cin abinci, sai da yaci ya koshi sannan ya nufi ɗakin Huda. Zaune ya tararda ita manne da waya a kunneta, tana ganinsa tayi sauke sauke wayar tana kallonshi.
Daga bakin kofa ya tsaya yana murmushi,


“Kin daina kukan.?”


Banzanta tayi masa, ta juyarda kanta, bai sake ce mata wani abunba ya juya ya nufi ɗakinsa.
Wanka yayi ya shirya cikin kananan kaya masu kyau da ɗaukar hankali, sun karɓe shi sosai sun kama jikinsa, sai kanshin turare yake kamar kanfanin pure cure. cikin takun girma ya dauko kasa ya nufi harabar gidan.




*** *** ***


Ido ya sakar mata, hannayensa zube cikin aljihu yana kallon yadda ta nufoshi da gudu, kanta ba ɗankwali, gashin kanta yasha gyara ya sauko har gadon bayanta, tana sanye da doguwar riga baka har kasa sosai tayi kyau kamar wata matashiyar ba indiya, yadda take gudun ma abun sha'awa da gashin kanta sai kaɗawa yake iskar na ɗibarsa.
Numfashinta kamar zai ɗauke ta karaso kusa dashi, ta mika masa jaridar dake hannunta,


“Saif kaga abunda suka rubuta a jarida game da mu?”


Ko motsi bai yi ba balle yayi mata magana,har lokacin kallonta yake da yadda ɗan karamin bakinta ke motsi,

“Saif ya kamata kayi wani abu kasan halin yan jarida ko ɗazu sai da wani ya kira ni yana tambaya na wai da gaske ne!”


Sai a lokacin ya haɗe yawun dake bakinsa, Ya gyara tsayuwarsa


“Baki iya gaiauwa bane!”


Da sauri ta gyara gashin kanta, ta ɗan natsu


“Sorry Ina wuni.?”


Bai amsa ba, sai kawai ya mika ɗayan hannunsa ya karɓi jaridar dake hannunta yana dubawa. Zuwa can ya ɗago kai ya kalleta,


“Toh miye a ciki karya suka faɗa ne.?”


Sororo tayi tana kallonsa jin irin tambayar da yayi mata, ta daɗi ita dashi suna kallon juna kamin ta iya saita muryarta,


“Karya kan suka faɗa”


Jaridar dake hannunsa ya aje saman mota ya kai hannunsa ya rika gefen fuskarta, a hankali ya furta


“Ba karya suke ba Minal I LOVE YOU AND I ONLY WANT YOU TO LOVE ME!”


Wani bugu zuciyarta tayi wadda bata taɓa jin irinsa ba a rayuwarta. Kallon kallo suka rikayi ita dashi. Idonshi sun karantar da ita gaskiyar abunda ya furta mata, sai da bata da tabbacin hakan tunawa da maganar da kanwarsa tazo tana faɗa mata jiya.
Da sauri ta janye fuskarta, idonta taf da hawaye tace


“Saif baza taɓa son mace irina ba, bana cikin tsarin matan da kake son ka aura, kanwarka ta faɗa min kana yaudarata ne kawai dan ka cin ma burinka, Saif tace min bana da tarbiya,
Kuma ni karuwace sannan kuma yar zina!. Nasani baza so ni ba saboda bana da Uba kuma ga ciyon dake tare dani and i know i m not your type”


Hawaye ne suka zubo mata, dai-dai lokacin data kai aya a maganarta
Wani irin kalar tausayinta yaji ya kamashi. A gefe ɗaya kuma yana mamakin wace kanwar tasa ce tazo tayi masa wannan lalatar,
A hankali ya matso kusa da ita ya kama hannayenta


“Minal ai kinsan ban neman mata ko?”


Kai ta ɗaga mashi,


“Toh taya zanyi amfani dake na cinma burina miyasa baki yi wannan tunanin ba,?
Minal rashin mahaifinki bai dame ni dan nima da Allah yaso da haka zai yi min, duk kuma mutu min da zai kyamace ki dan ciyon dake jikinki wawane,
Minal weather you believe me or noti I LOVE and I really mean it ai kinsan babu Wanda ya isa ya sani abunda ban tashi ba ko?”


Nan ma kai ta ďaga masa,


“So just trust me I'm for what ever”


Yawu dake bakinta ta haɗiye, tace


“But...-”


Da sauri ta ɗora yatsansa saman leɓenta,


“Shiiii no but kawai ki bar zuciyarki taso wadda take so zan tsaya miki naci alwashin kasancewa dake har abada”


D'agowa tayi ta kalli cikin kwayar idonsa, shi kuma ya sakar mata murmushi ya rumgumeta.




A hankali Kairat dake tsaye bakin kofar Garden tana kallonsu ta share hawayen dake idonta, ta nufi wata bishiyar mangoro, ta jingina da ita, ta ɗaga kanta sama wasu hawaye masu zafi suka rika zuɓo mata.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO.


NA


KHADEEJA CANDY


Candynovels.wordpress.com


WATTPAD @khadeeja_candy



Kainuwa Writers Association




*23*


Ido a rufe ya isa Asokoro villa, dan yau so yake yaji wace munafurka qanwarsa ce tayi masa wannan wawancin,
Sallama ma dan ta zamo masa dole ne kawai yayi ta.
Kallo ɗaya Momi tayi masa ta gane yana cikin ɓacin rai,

“Momi ina wuni.”


Ya gaisheta ne yana kokarin zaunawa saman kujerar dake fuskantar ta ta,


“Lafiya kalau Saifullah ya gidan?”


“Lafiya kalau Momi ina su Safiya.?”


“Suna ciki lafiya dai.?”


Bai ɓoye ma Momi komai ba, akan Minal da kuma abunda tace Kanwar tasa tazo tace mata,
Kai Mummy ta girgiza,


“Amman basuyi tarbiya ba, ina ruwansu da ita Safiya Rukaiya Lubna”


Momi ta kwala musu kira, ba ɓata lokaci suka fito suka zauna suna gaida Saif,


Bai amsa ba sai kawai yace,


“Cikin ku wacece taje gidan su Minal?”


Kallon kallo suka rik'ayi da junanasu zuwa can Safiya tace,


“Nidai ba ni bace”


“Toh wacece.?”


Ya tambaya a tsawa ce, nan kuma kowa yayi shiru, Momi ta kalleshi,


“Ita bata faɗa maka ko wacece cikin su ba.?”


“Ae ita ai bata sansu ba tace wadda ta faɗa mata dai fara ce kuma tace ita kanwata ce”
“Wannan ba hujja bace tunda dukansu fararene”


Faɗar Momi tana kallonsu, Saif ya fusata sosai


“Wallahi ko wacece ta faɗi kanta kamin na gano ta dan wahala kawai zata sha”




“Nice Yaya”


Tana faɗa ta koma gefen momi, tana kallonsa


“Toh uban waya aikeki”


Ta ɗan ɓata fuska,


“Amman Yaya ya za'ace wannan yarinyar kake so fisabillillahi yarnya nan fa bata da Uba kuma shaye shaye take kuma ance yar iska ce”


Kamin yayi magana Momi ta rigashi,


“amman Safiya baki da hankali toh ina ruwanki da ita ba shi ya ganta a haka yace yana so ba”


“Amman Momi jifa harda yan jarida sai buga labarin suke ai ana son idan mutun zaiyi aure ya auro yar mutunci yarinyar nan fa yar iska ce kuma bata da uba”


Momi ta fusata,


“Idan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login