Showing 45001 words to 48000 words out of 115850 words
Chapter 16 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
kuma kinsan duk namijin da yaga matarsa da wani dole yaji bakin ciki da ɓacin rai”
Shiru Minal tayi kamar mai nazari, tana haɗiye yawun dake bakinta,
“Amman Kairat yana sona ya kasa yayi min uzuri?”
“Ba zai miki uzuri ba saboda zuciyarsa a rufe take amman nasan gaskiya zata bayyana”
“Yes zata bayyana Kairat nasan da wannan dan karya bata taɓa ɗorewa ba but...-”
Sai kuma tayi shiru, ta share hawayen fuskarta, ta janye hannayenta daga rikon da Kairat tayi mata ta nufi ɗakinta.
Bayan Sallah insha i mummy ta shiga ɗakin, rike da kofin tea da biskit, dunkule ta hango Minal saman gado kamar marar lafiya, ganinta haka ya ɗaga mata hankali, tayi saurin karasawa kusa da ita ta yaye bargon tana faɗin,
“Minal baki da lafiya ne.?”
Tashi tayi zaune cike da karfin hali ta kirkiro murmushi,
“Lafiya ta Kalau Mummy sanyi ne kawai nake ji me kika kawo min?”
“Tea da biskit nasan tunda kika zo baki ci komai ba, are you sure lafiyar ki kalau?”
Mummy ta tambaya cike da damuwa a fuskarta,
Hannu tasa ta karɓi tea ta sha dan ta kara tabbatar ma da Mummy lafiyar ta kalau duk da ita kanta tasan bata da lafiyar,
“You see mummy i m fine”
Kanta mummy ta shafa, tana murmushi zuciyarta kuma cike da tsoro,
“I hope so tashi muje muci abinci nasa anyi miki shimkafa da miyar kifi abunda kike so”
“Bana jin cin abinci yanzu kuma kinga nasha tea sai dai ko zuwa anjima”
Mummy ba dan taso ba ta kyale ta, sai dan bata son tirsasa mata,
“Okey promise me anjima zaki ci”
“I promise mummy”
“Thank you”
Ta faɗa tana shafa kanta, sannan ta tashi ta fice,
Sai goma na dare ta sake dawowa ɗakin ganin bata fito ba ta saka ta agaba suka ci abincin tare.
Haka mummy ta rika yi mata a duk lokacin cin abinci sai ta zubo suci tare, ita kuma dan ta farantawa mummy ta kuma nuna mata bata damuwa sai taci duk da yake wani lokacin kaɗan take ci. Sam bata yarda mummy taga kukanta tun tana ɓoye kukan har kuka ya daina zuwa mata da kansa, sai dai ƴnauyin kirjin da take ji.
Yau ma mummy ta ɗibo abinci kamar yadda ta saba, amman yau a falo ta zaune,
“Kairat jeki ki kira min Minal”
Tace da ita tana kokarin karɓar ruwan da talatu ta ke mika mata,
Sai da ta kalli abinci sannan ta tashi ta nufi hanyar ɗakin Minal,
A bakin kofa ta tsaya ta sauke ajiyar zuciya sannan ta kai hannunta ta murɗa kofar ɗakin ta shiga.
Takardu taci karo dasu cikin ɗakin ki duk an watsar Minal kuma ta ba kofar baya ta rike kai da alama kuka take,
Hannu Kairat takai ta ɗauki ɗaya ɗaga cikin takardar dake bayan Minal,
_Miyasa ka tafi ka barni? Miyasa bakayi hakuri an same ni ta halal ba? Miyasa baka yi tunanin ya rayuwa ta zata kasance ba? Me na maka Haka me na maka?_
Shine abunda Kairat ta gani a rubuce, koda ta gama karantarwa idonta cike yake da kwallah, a hankali ta zauna bayanta ta dafa ta,
“Kuka kike yi sister.?”
Bata ɓoye nata ba ta juyo tana ɗaga mata kai,
“Yes kuka nake yi kukan da bashi da magani, miyasa ya buga min tabon da ba zai gogu ba? da zanga Mahaifina a yanzu da nayi masa tambayoyi masu yawa”
Hannayenta biyu tasa ta riki fuskar Minal, idonta cike ta hawaye ta soma mata magana kamar mai rarrashi
“Ashe har yanzu baki koyi Hakuri ba Minal? Har yanzu baki fahimce miye duniya ba?”
“I try but you know what? Ke shegiya ce bada aure aka haife ki ba wannan kalmar ita tafi komai bakan ta min rai miyasa mutane basa fahimta ne shin ni nayi kaina ko kuma jindaɗina ne na kasance haka? Yanzu Huda ta kirani ta gaya min magana son ranta ta aibanta ni tayi tirr da rayuwa mena tarewa mutane ne ? Dame zanji!”
Kuka take sosai har muryarta na rawa, ganin hakan yasa Kairat ta rumgime ta suna kukan tare.
Zuwa can ta janye jikinta tana share mata hawaye tace
“Karki bari Mummy taji wannan maganar hankalinta zai iya tashi”
Kai ta ɗaga mata tana kara goge hawayen,
“Taso muje tana falo tana jiranki zaku ci abinci”
Nan ma kanta ɗaga mata ta tashi ta shiga banɗaki ta wanke fuskarta sannan Kairat ta rika hannunta suka fice.
*** *** ***
SAIF............
Tunda ya sauka London, baya cikin walwala duk wani jindaɗi da yake tunanin idan ya baro nageriya zai samu bai same shi ba, shida yazo da zimmar yin wata biyar sai gashi ko wata uku bai yi ba yaji ya kosa da garin,
Wani gefen kuma gani yake ko dan Huda taki yarda ta biyo shi shiyasa abubuwan suka taru suka yi masa yawa, ga damuwar da yaxo da ita tayi masa tsaye a rai a maimakon ta ragu sai ma karuwa da take.
Idan ya rufe idosa babu wanda yake ganin sai Minal, gashi sai mafarkai yake yi barka tai, duk wani sukuni dake tare dashi sai ya rasa shi, gani yake kamar zai iya cire Minal a ransa amman ya kasa yanzu da yake son ɗasa kiyayyarta a zuciyarsa, soyayyarta ce take karuwa, wani ɓangare na zuciyarsa kuma sai tausayinta yake ji, yes rayuwar Minal abun tausayi ce amman miyasa tayi min haka naso muyi rayuwa mai kyau ni da ita amman ta ruguza min tsari ta wargaza min lissafi.
Wani dogon numfashi yaja ya lumshe ido,
_nasan a duk inda kike kina bukata ta kusa dake, koda mun rabu zuciyoyin mu ba zasu iya rabuwa ba,_
“Why? Minal why?”
A fili ya furta ya tashi daga kwance da yake yana kallon sili kamar wani bakon ɗakin.
*** *** ***
A hankali ta sauke idonta daga kallon silin da take, ta mai da dubanta ga wata fulawa dake gefen kofar sitting room, tana sauke ajiyar zuciya,
_Har yaushe ne lokacin da nake mafarki zaizo? Sai yaushe Saif zai gane gaskiya? Ina son ka gane gaskiya Saif ba dan na zauna da kai ba sai dan muyi rabuwar mutunci, daga lokacin da ka gane gaskiya Na rabu da kai kenan rabuwa ta har a bada_
A zuciyar ta take wannan maganar, tana dafe da kanta,
wani kololo taji ya tsaya mata a zuciya ya tokare mata gaba, yayi nauyi sosai, ajiyar zuciya ta shiga saukewa, wai ko zata samu sawaba,
ta tashi ta nufi windon dake facing ɗinta ta rike labulayen tana kallon Garden.
Abu taji ya gangaro mata daga hanci kamar majina,
da sauri ta nufi dinning, ta ɗauki tissue ta goge, sai gashi ya kara zubowa kamin ta hankara har ya zubar mata a hannun, ɗago hannun tayi ganin abu kamar jini tana dubawa, jinin da gaske ba kama bace,
“Innalilahi wa'inna ilaihi raji'un”
A fili ta furta tana zaro ido, numfashinta ya shiga rawa a'lamar tsoro.
COMMENT ON EVERY LINE, AND YOU SILENT READERS PLEASE VOTE
#OneloveOneheart
#KhadijaAbubakarAlkali
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO
NA
KHADEEJA CANDY
*31*
Da sauri ra nufi ɗakinta, tana shiga ta maida kofar ta rufe tana maida numfashi,
Ta daɗe a gurin a zaune, kamin ta tashi jiki ba kwari ta shiga banɗaki, ta kunna fanfo tana kwanke fuskarta da hanci. Fashewa tayi da kuka lokacin da idonta suka kai kan madubin dake gabanta ta kalli fuskarta, sai ita kanta taba kanta tausayi,a gefe ɗaya kuma Mummy take tausaya ma bata san halin da zata shiga ba idan bata raye tasan yadda Mummy take son ta kuma suka Shak'u, Mummy bata da kowa a yanzu sai ita kamar yadda itama bata da kowa sai mummu, toh idan guda ya mutu ya bar guda ya guda zaice ta rayuwarsa zata kasance?
A hankali ta sulale kasa tana tana rera kuka a hankali, ta yadda babu wanda zaiji sai wanda ke kusa da ita, jinin ko sai zubo mata yake kamar ana k'ara turo shi.
Kuka tayi sosai har idonta ya lumbura, fatar idonta tayi ja, sai da taji an kira sallah, sannan ta tashi tayi alwala ta ɗauki wani karamin tawul ta rufe hancinta dashi saboda zubar da jinin yake mata, sannan ta fito daga banɗakin kamar wanda aka cirewa lakka.
Tawul ɗin tasa ta ɗaure hancinta sannan ta canja tufafin dake jikinta ta saka hijab tayi ta soma sallar, bayan ta kare ta cire tawul ɗin ta kai shi toilet ta sake ɗauko wani tana daɗe hancin da shi kamar mai jin wari,
“Minal...-”
Jin kiran Mummy yasa ta kara gyara zaman tawul ɗin a hancinta ta juyo tana kallon kofa,
Mummy ta shigo fuskarta shimfiɗe da murmushi,
“Minal muje kici abinci nasa an... -”
Shiru tayi bata k'arasa ba lokacin da hankalin ta ya kai kan hancin Minal,
Cikin tashin hankali ta k'arasa kusa da ita, ta dafata tana tambayar ta muryar ta na rawa,
“Minal...mi..ya sa...mu hancin... Cin ki? Ko ciwon ne ya tashi”
Murmushi tayi kamar da gaske, babu abinda yake damunta,
“A'a Mummy mura ne”
Kokarin goge hancin ta tayi ta yadda Mummy ba zata gane ba, ta buɗe shi tana faɗin,
“Kin gani, mura ne babu wani abun majina ce take min zuba”
Tana faɗar hakan ta maida tawul ɗin kan hancinta, sanin idan bata mayar ba jinin zai iya mata zuba har Mummy ta gani,
Mummy bata sake ce mata komai ba sai kawai ta mata murmushi ta juya ta bar ɗakin zuciyarta na rawa da bugawa,
Sauri sauri take mai kamar gudu ta nufo falo da zimmar ɗaukar wayarta dake kan kujera,
“Lafiya Mummy?”
Kairat ta tambaya ganin yadda hankalin Mummy ya tashi,
“Minal ce na gani tana rufe hanci ina jin ciwon ta ne ya tashi tace min mura ne amman nidai ban yarda ba”
Cikin muryar kuka take bata amsar, tana neman wata number a wayarta,
Da gudu Kairat ta tashi ta nufi ɗakin Minal, durfane ta tarar da ita tana kuka kamar mai neman gafara, da sauri ta dafata idonta cikin da hawaye tace
“Sister are you crying?”
“Yes Kairat bazan iya ɓoye miki ba, but please karki faɗa ma Mummy”
“Oh my God”
Da sauri ta tashi ganin yadda jinin take zuba a hancin Minal ta nufi kofar fita,
Minal. Sai kiranta take amman bata jita ba tsabagen hankalinta baya gurin. Karo suka tashi yi da Mummy, dan tana kokarin fita Mummy ta shigo,
Da gaggauwa Mummy ta nufo Minal,
“Tashi muje asibiti na kiran Likitanki baya nan amman yace zai kira wata Dr. Zainab zata duba ki”
Tashi tayi ba musu, Mummy ta rik'a ta suka fice, gidan baya ta zauna ita da Kairat Mummy na driving suka nufi asibitin.
*** *** ***
Kaɗan-kaɗan yake cin abinci yana wasa da bakin kofin da aka zuba masa drink,
Momi na lure dashi, tun zaman shi gurin chokali huɗu kawai yakai bakinsa sai kamar wanda baya son abinci ko kuma aka sashi ci dole, Tasan matsalar iyaline take damunsa tunda Safiyyah ta faɗa masa abunda ya faru tsakanin sa da Minal, yanzu kuma yayi dawowar da ba'a zata ba kuma yaki sauka gidansa ya sauka a gurin ta,
“Saif duk kai kasa kanka cikin wannan matsalar yanzu da ace yar'uwarka ka aura zaka shiga wannan halin ne? Yaro da kai kana jama kanka matsala haka siddau”
Ajiyar zuciya ya sauke ya busar da iskar bakinsa,
“Oh Mummy so nawa zan faɗa miki Safiyyah bata daga cikin tsarin matan da nake so wallahi bazan iya aurenta ba kuma ko na aureta ba daɗi za muji ba tunda ni bana so”
“Su waɗannan da kake so ai sun nuna maka son duk cikin su babu na kwarai kowa gasa maka giɗa yake a hannu, da ita ka aura da duk haka bai faru ba tunda ita tana sonka”
“Ko tana sona dole ne sai hak'uri tunda ba ayi ma namiji auren dole”
Tashi yayi dan baya son ta kara sako masa wata maganar, ya ɗauki makulin motarsa yana faɗin
“Ga file can idan Dad yazo sai ki bashi ni zanje gida”
Taɓe baki tayi,
“Toh ka gaida gidan kuma ina son ka natsu ka sake tunani Saif.... ”
Bai ce mata komai ba ya juya ya fice ransa a jagule ita kuma ta bishi da kallon tausayin halin da ɗan nata ke ciki.
***
11pm, dai-dai Minal ta farka, ta kwashe awa biyu tana bachi, dan suna isa Dr. Zainab ta karɓe aka wuce da ita ICU Unit 2 tayi mata alurrar bachi, ta saka mata drip.
Kokarin tashi ta shiga yi sai taji an rik'a ta an tayar zaune, ɗago kai tayi suja haɗa ido ta Kairat fuskarta shakaf da hawaye,
Saurin ɗauke kai tayi, tana haɗiye yawu,
“Ki aje kukan ki har lokacin da yinsa zaiyi sai kiyi amman ba yanzu ba”
Hannayenta Kairat ta kama tana kuka,
“Minal mi yasa kika saka kanki a damuwa, Dr. Tace ciwon ki yayi tsauri sosai”
Dr. Zainab ce ta shigo, rike da wasu files, ta shiga duba Minal da tafiyar numfashinta a computer tana rubutawa.
A nan Minal tayi ta kara matse hannunta cikin na Kairat idonta cike da hawaye tace,
“Sis please promise me zaki kula da Mummy”
“I don't have to kinsan zan kula da ita, amman ki bar wannan maganar”
Hawaye ne suka shiga zuba a idon Minal, ganin hakan yasa Kairat ta kasa ɓoye kukan ta har sai da ta fasa shi,
“Please stop crying Sis you are very strong woman i wll fight it you can fight this sick”
“Bana tunanin haka Kairat wannan ba irin ciwon da kike tunani bane, blood cancer ne kuma kinsan ina da sikila. Kairat Mummy ce damuwa ta bansan irin halin da zata shiga ba. Zan mutu da bakin cikin abu biyu a rai na bakin cikin zan mutu na bar Mummy ita kaɗai kuma Saif yana min kallon maciyiyar amana”
Ido Kairat ta tsura mata tana hawaye, Dr. Zainab ma kallonta take cike da tausayawa.
KUN TUNA WACECE DR. ZAINAB?
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO
NA
KHADEEJA CANDY
®
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)
*32*
Tsit ɗakin yayi, kamar ba kowa babu abunda kake ji sai sautin kukan Kairat, Minal ma kuka take amman ba mai sauti ba, Dr. Zainab ta dafa ta idonta cike da hawaye,
“You have to be strong, ciwon dake jikin ki ba shi ke tabbatar miki da mutuwa zaki yi ba, so nawa masu lafiya suke mutuwa su bar marar lafiya? Wannan ciwon naki dalilin tashin sa rashin shan magani da kike yi har na tsawon watanni kuma kika ɗauki damuwa kika saka a cikin ranki,
ki sassautawa zuciyarki ta yadda zai taimaka mana gurin daidai ta tafiyar numfashinki da kuma samun lafiyarki, sannan kuma ya taimaka kama baby dake cikin ki tayi rayuwa mai lafiya”
Da sauri Minal ta kalleta, cike da rashin fahimta, Kairat ma kallonta take dan tayi maganar ne kamar a dunk'ule,
“Dr ban fahimta ba me kike nufi ne?”
“Kar dai kice min baki san kina da ciki ba?”
Ta tambaya tana kama hannun minal tana saitawa da agogon dake manne a hannunta,
“Kina nufin Minal tana da ciki na haihuwa?”
Kairat ta tambaya, cike da son sani Dr Zainab tayi murmushi,
“kina da ciki na haihuwa na uzara da nasa miki ɗazu na'ura ce dake nuna duk abinda ƴake cikin jikin mutum ta nuna kina ɗauke da ciki na wata uku har da yan kwana ki”
Rufe baki Kairat tayi tana murmushi mai haɗe da hawaye, Minal kuma ta lumshe ido tana haɗiye yawu,
“Nasan Saif zai fi kowa farinciki idan yaji saboda yadda ya daɗe yana neman haihuwa”
Buɗe ido Minal tayi ta kalleta, wacece ita? ya akayi tasan Saif? taya ma tasan ita matar Saif ce,
“Wacece ke?”
Kairat ta tambaya cike tana mata kallon rashin yarda,
zaunawa Dr.Zainab tayi saman gadon ta Minal take ta kama hannunta tana murmushi
“Karki yi mamakin taya nasan Saif kike aure, ke da shi duk yan manyan mutane ne kinsan babu yadda za'ayi ayi auren ku yan kasa basu sani ba,
babu jaridar da bata buga labarin auren ku ba anan najeriya, nasan Saif yana matukar son haihuwa ne saboda abokin aiki na ya taɓa duba shi shi da matarsa”
Minal ta share hawayen da suka zubo mata,
“I just can't believe ina da ciki bsn taɓa jin alamu ba”
“Ba lallai bane kiji alamu akwai cikin da sai ya girma yake sa mace ta canja wani kuma tun farko yake sawa wani kuma sai a tsakiya”
Lumshe ido Minal tayi tana maida numfashi, Dr. Zainab ta kalli Kairat
“A bata kayan marmari taci fruit kar a bata abu mai zafi da kuma mai nauyi idan tace zan dawo na bata magani”
Ta faɗa tana haɗa takardun dake hannunta, kai Kairat ta ɗaga mata
“Okey Doctor thank you”
Murmushi tayi
“It's my job”
Bayan ta fice, Kairat ta rumgume Minal tana dariya,
“I can't believe this dear Alhamdulillah naji daɗi sosai”
Murmushi Minal tayi wanda ba zan iya fassara yanayinsa ba na farinciki ne ko akasin haka ko kuma na har ƴyanzu bata yarda da tana da cikin ba!
Shigowar da wata abokiyar Mummy tayi ko kuma nace mai take mata baya, yasa Kairat ta sake ta suka kalleta, ko wanne fuskarsa babu ɗauke da murmushi,
“Masha Allah Minal an samu sauki Allah ya kara lafiya haka