Showing 6001 words to 9000 words out of 115850 words

Chapter 3 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

5644

ki dawo ba Dad ne ya aikeni ai kinga ai bazan ce masa bazani ba ko?”
Jikar ya ɗauka tare da riko hannunta suka nufo parlor, har bakin mota ta rakashi, nan ya ɗanyi huge ɗinta
“Ki min addu'a kinji?”
Kanshi ta shafa
“Allah ya dawo min da kai lafiya”
“Amin thank you ki kula min da kanki”
Kai kawai ta ɗaga mishi tana kallon shi har ya tada motar ya fice,
Sai da ya biya Maitama ministers hill ya karɓi pictures ɗin Minal da information sannan ya wuce,


NEW YORK.....
14:44GMT jirgin su Minal ya sauka, kai tsaye ta nufi hanyar fita Airport ɗin, sanye da wani blue jean yayi tight ɗinta sosai, sai yar fashion t-shirt pink color,
Babu komai a hannunta daga ATM sai Passport, haka ta fito tana janye gashin kanta da iska ke kaɗawa,
Jin am dafata yasa tayi saurin waigowa,
“Sarah”
Abinda Minal ta faɗa kenan tana kallon budurwar farar fata,
Hannayenta Minal ta kama tana dariya
“Mil Barka da zuwa birnin mu birni mai yanci da walwala”
Mamaki ne ya bayyana a fuskar Minal
“Sarah ya a kayi kika san nazo?”
Sama Sarah tayi da glasse ɗin idonta
“Deen ne ya faɗa min tun jiya kuma shi ne ya faɗa min lokacin da jirginku zai taso da kuma lokacin da zai sauka shiyasa na tare ki nayi marmarinki sosai Mil”
Da dariya ta k'arasa maganar tana jan kumatun Minal,
Da sauri Minal ta rungume ta idonta cike da hawaye
“Nima nayi marmarinki Sarah ina sonki sosai”
“Nima ina sonki Mil”
Duk da yaren faransanci suke wannan maganar,
Nan Sarah ta rika hannunta suka nufi gurin da aka tana da dan aje motoci,
Wata red sport-car suka shiga Sarah ce a driver seat, Minal na zaune a front seat, a hankali ta tashi motor suka hay t-t.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!


NA


KHADEEJA CANDY




_DEDICATED THIS PAGE TO MIEMIEBEE Thank you DEEN🤞🏻._




BABI NA TAKWAS___8


Kallon shi kawai ta bishi da shi har ya zauna a kujerar dake facing ɗinta,
Shiru yayi yana kallonta sannan yace,
“Miyasa kika tsani Dr Salamu bayan ita ce ta haife ki?”
Shiru tayi kamar baza amsa mishi ba can kuma ta soma magana,
“Mummy ba ita ce ta haife ni ba bansan waye mahifina ba bani da kowa ban kuma san haka ba sai da wadda muka kulla maganar aure dashi yace min iyayenshi sunce ba zai aure ni ba dan bani da uba kuma Mummy ba ita ce ta haife ni ba,
Ni kuma ban musa masa ba saboda na sha tambayar Mummy waye Mahaifina taki ta faɗa min sai ma cewa take na daina mata maganar na daina damuwa zata yi min duk abinda nake bukata,
Kuma lokacin dana same ta da maganar sai tace min lallai ni ba da aure aka haife ni ba ni kuma da naji haka sai nayi unkurin hallaka kaina”
Tana maganar hawaye na mata zuba,
Tunda take maganar Saif ya natsu yana saurarenta har ta kai aya, tausayinta ne ya kama shi idan har abunda ta faɗa gaskiya ne ta chanchanci a tausaya mata dan rashin uba ko gurin namiji akwai ciyo barre ya mace,
Tashi yayi ya koma kusa da ita ya zauna yaja kanta ya dora saman kafaɗar shi,
Cak.! Kuka ya tsaya mata wata rahama ta ratsa mata jiki, lumshe ido tayi ta kusa kanta cikin jikinshi tana shakar daɗadden kanshin dake fita daga jikinshi.
Sunyi minti goma sha biyar a haka, sai can ya ɗago kanta yasa handkerchief mai ɗauke da sunanshi sai kanshi turare yake ya share mata hawaye, sannan ya tashi tsaye,
Kallo ta bishi dashi har yakai bakin kofa sannan ya juyo ya kalleta,
“Ki kwantar da hankalinki Deen ɗinki zai dawo yanzu”
Kai ta ɗaga mishi “Atm ɗina fa? ”
Bai bata amsa ba sai kawai ya juya zai fice, ganin hakan yasa tace “Please karka faɗawa Mummy ina nan”
Nan ma baice da ita komai ba ya fice,
A hankali ta kwantar da kanta hannun kujera tana kallon handkerchief ɗin shi da bari gefen kujerar, wani sabon kuka ya taso mata.




Driving yake yana shan karatun Sheik Shuraim, har ya isa Maitama Ministers hill tunanin Minal yake, gaskiya duk wadda yake cikin gata irin na Minal ya wayi gari akace bashi da uba xaiyi bakin ciki sosai,
Yana yin parking Dr. Salamatu ta fito da sauri ta nufoshi,
“Anyi nasara kuwa?”
Kai ya ɗaga mata ya mika mata abubuwan daya karɓa hannun Minal,
“Anyi nasara ki rike wannan nasa a kasa mata takunkumi bata iya zuwa ko ina a yanzu koda tana da waɗannnan abubuwan”
Da sauri tace “Ina take Saif?”
“Wannan ne kawai bazan faɗa miki ba dan ta rik'i haka a gareni kuma kinsan ke kika saka ta cikim halin da take ciki yanzu”
Yana kaiwa nan ya juya ya shiga motarshi, jiki a sanyaye ta k'arasa kusa dashi “Kaima kana zargi na kamar ita?”
“Toh misaya ba zaki faɗa mata wacece ita ba? A yanzu ta riga tasan ba kece kika haifeta ba idan ma har shine kike jima tsoro karta gujeki ko? da kin faɗa mata gaskiya tun farko da bata shiga halin da take ciki yanzu ba”
Tana kokarin maida hawayenta tace “A shirye nake na faɗa mata komai Saif nayi nadamar yin hakan da nayi”
Kafaɗunshi ya ɗaga “Idan bukarta hakan ta taso ita da kanta zata neme ki”
Bai tsaya jiran abinda zata ce ba yayi ma motarshi key, itama bata kara cewa wani abun ba har ya bar gidan.






********






“Dear wai mi yake damunka ne naga cin abincin kawai kake amman hankalin ka baya gurin?”
Drink ɗin dake gabashi ya ɗauka sha yana murmushi,
“Wai yanzu Huda idan kika wayi gari Hajiyar ki tace ba ita ta haife ki ba kuma Abbah yace ba shi ne mahaifinki ba kuma duk family da kika gani ba naki bane ya zaki ji?”
Kallon mamaki tayi mishi “Wannan wace irin magana ce wannan Saif?”
“Please just answer me”
Kai ta jinjina “Gaskiya zanji ba daɗi zan kuma yi bakin ciki wata kila har na gudu saboda takaici kuma zanso sani suwaye iyayena ya kuma akayi na zo hannun waɗanda ba iyayena ba”
A hankali ya kaɗa kai alamar gamsuwa yace “Kuma ace akan haka har na rabu dake ya zaki ji?”
6ata fuska tayi "Haba dai dear miye na wannan maganar kuma gaskiya idan ka rabu dani kashe kaina zanyi ko kuma na haukace gaskiya ka daina bana so”
Hannayenshi ya ɗaga “Na daina Dear”
Cigaba yayi da cin abinci yana tunane tunane,
“Wai miyasa kayi min wannan tambayar?”
Kallonta yay da murmushi “Saboda kina kaunar Saif”
Dariya tayi ta tashi tsaye,
“Toh angon Huda nidai na koshi over”
Tashi shima yayi tsaye “Nima ai na koshi daman ke nake daku”
Hannunta ya rik'a suka nufi bedroom bayan ya kashe wutar parlor.




VOTE!
COMMENT!!
SHARE!!!
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!


NA


KHADEEJA CANDY


_Vote me on wattpad @khadeeja _candy_




BABI NA BAKWAI___7




SAIF.....
Yana yin Sallah Asuba ya shirya y nufi Airport, dan yasan halin Dad ɗinshi matukar ya tsallake abunda umarni daya bashi komai zai iya faruwa,
Karfe 10pm a gogon ya iso yana sauka Airport yayi ma direba shi waya, cikin kankanen lokaci ya iso suka nufi gida.
A parlor a tararda Huda, tana ganin shi ta taso fuska a washe ta tareshi,
“Sannu da zuwa dear”
Bai amsa mata ba ya ɗauke kai ya nufi ɗakin shi, yana shiga ya cire kayan jijinshi ya shiga bathroom ya ɗan watsa ruwa, bayan ya fito yayi sallah. ya nufi dining
Tana ganin ya fito ta bishi tana mishi magana, nan ma banza yayi da ita har ya kare cin abinci ya koma ɗakinshi,
Nan ta bishi tana kiranshi tana shiga taci gaban shi tana mishi magana.
Sai a lokacin ya kalleta,
“Wai minene Huda mi kike so nayi miki ne?”
Cikin ɗaga murya yayi mata tambayar,
Kamar ta fasa kuka, “Tunda ka dawo kak'i kayi min magana sai fushi kake dani”
“Ai dole nayi fushi dake halin nan naki bana sonshi kuma bazaki chanja ba,
Miyasa kika je kika faɗawa Dad maganar tafiyar nan bayan ga yadda mukayi da ke wama kika tambaya da zakije.?”
Hawaye ta somayi
“Saif saboda ka daina sona kake min haka ko? Shiyasa ka sakeni bayan kuma ka mayar da ni kaki yarda na dawo gidan ka, washe garin dana dawo ka taka jirgi kabar kasar nan dan kuma na faɗawa Dad yayi sanadiyar dawowarka shine zaka hauni da matsifa, saboda ka ga ina sonka Saif ko shiyasa kake son karkata zuciyarka zuwa ga wata ko?,
Mi yasa kake son wulakanta ni Saif yanzu one year da yin Auren mu amman ace har saki ya shiga tsakanin mu, What is next kuma?”
Kuka ta saka mashi marar sauti, shikan ido kawai ya sakar mata dan gaskiya ma tayi mishi yawa,
Kamar da wasa sai gata har kasan carpet tana kuka mai karfi.
Sai da tayi mai isarta sannan ya duka ya rikota suka zauna saman gado, fuskarta ya rik'a,
“Dubi yadda kika bata fuskarki da kuka kamar karamar yarinya, wane Mak'aryacin ne yace na daina sonki?”
“Haka ne mana Saif”
“A'a ba haka bane Huda har gobe ina sonki sakin da nayi miki sheɗan neda kuma halin nan naki dan ki chanja, kuma babu wata yarinyar da nake so banda huda”
Ya k'arasa maganar yana jan hancinta,
Sai a lokacin ta tsagaita kukan “Toh mi kaje yi new york?”
“Mamanta ce tace na taimaka mata kar ta rasa yarta”
“Ni dai na daina bana so”
Murmushi yayi “Toh shi kenan na daina”
Da sauri ta kalleshi “Da gaske?”
“Eh mana tunda uwargida na bata so ai dole na daina abun har da su kuka ba zan sake ba tunda Huda ta bata so”
Murmushi tayi ta shigar da kanta cikin jikinshi, shi kuma ya shiga aika mata da sakwanni yana zolayarta.




MINAL.....
Haske ne ya doki fuskanta sakamakon buɗe labulen ɗakin da Sarah tayi,
Hakan yasa ta farka ta ja bedsheet tana lulluɓewa,
“Ohhh Sarah I'm not done yet”
Baki Sarah ta buɗe “You don't done what? Please wake-up baby you already done”
Har ta juya sai kuma ta juyo tana shafa gashin kanta “And before I forget Deen is on the phone”
Da gudu Minal ta sauka saman gadon har tana kokarin ture Sarah,
“Oh my Deen” Kamar wata karamar yarinya ta k'arasa gaban wayar ta dauka ta kara a kunne,
“Hello Deen”
Daga can cikin wayar aka amsa mata,
“Ya kike Deen ya enjoyment?”
“Komai Kalau kaifa?”
“Nima kalau Sarah tace min kina jindaɗi haka ne?”
“Eh haka ne ba nida wata damuwa a nan”
Shiru ya ɗanyi sannan yace “Baki tambayi Mummy ba”
B'ata fuska tayi kamar yana ganinta “Oh Deen please don't kasan banason maganar ta”
“Na sani Deen amman fa ta damu sosai kuma kinsan tana sonki”
Shiru tayi bata ce komai ba jin hakan yasa ya ɗauko mata wata firar,
Sun daɗe suna waya daga bisani sukayi sallama.




K'arfe 8am Saif ya shigo part ɗin Dad, faɗa sosai Dad yayi mashi sai da yaji ba daɗi daker ya samu Dad ya saurara mishi,
Hak'uri Saif ya bashi sannan ya tashi ya nufi part ɗin Momi, itama sai da tayi mishi nata faɗan kamin daga bisani ya jata da fita,
Sai uku da wani abu ya bar gidan bayan ya gama cin abinci,
Kai tsaye gidansu Minal ya nufa, da tunane tunane ya isa gida, har ya zauna parlor pictures ɗin Minal dake hannunshi yake kallo,
Bai daɗe da zama ba Dr. Salamatu ta fito yadda Saif ya ganta sai duk ta bashi tausayi, duk tabi ta rame kamar ba ita ba,
Jiki a sanyaye ta zauna ganin dawowarshi da pictures ɗin Minal a hannu haka ya tabbatar mata da baiga Minal ba,
Tasowa yayi ya karaso kusa da ita ya mika mata pictures ɗin
“Ban samu ganinta ba”
Karɓa tayi tana faɗin,
“Babu komai Saif kayi kokari Allah ya saka da alheri”
Hannayenshi yasa aljihu,
“Babu komai yima kaine ki yi ta mata addu'a shine kawai mafita”
Kai ta gyaɗa mishi ta share hawayen da suka zubo mata.
“Ba'a sameta ba ko?”
Budurwar ce ta fito tana tambaya,
“Eh ba 'a sameta ba Kairat”
K'araso tayi kusa da ita ta zauna tana faɗin
“Daman nasan ba za' a taɓa samun Sister ta sai ta hanya ɗaya”
Daga Saif har Dr. Salamatu kallonta suka,
“Ta hanyar Deen!”
“Wanene Deen?” Saif ya Tambaya,
“A bokinta ne ko kuma nace Amininta duk wani abu nata mai muhimmanci yana hannunshi ta yarda da shi sosai bata kaunar bacin ranshi ko kaɗan ina ganin ma shi ne ya shirya mata yadda tabar kasar nan”
Dr. Salamatu ta amsa mishi,
Ido ya tsurawa Kairat ɗin kamar mai karantar abu a fuskarta, can ya ɗauke kai yace
“Yanzu ya za'ayi na same shi?”
Da sauri Kairat ta tashi ta nufi ɗaki “Ina zuwa”


Bata daɗe ba ta fito rike da wani ɗan karamin kati ta mika mishi, “Wannan shine address ɗin shi”
Jimmm ya ɗanyi kamin ya mika hamnu ya karɓa, ya dade yana kallon card ɗin sannan ya tashi ya fice.




NEW YORK.....
Babu abinda suke sai ciye ciye sun cika ɗaki da waka suna ihu kamar wasu sabbin mahaukata,
Sam basu lura da Telephone ɗin dake ringing ba, sai da suka je chanja waka,
Da sauri Sarah ta nufi gurin wayar,
Tana ɗauka ta kwalawa Minal kira da gudu ta k'araso jin ance Deen ne ya kira,
Tana kara wayar a kunne kamin tayi mishi magana yayi mata cikin wata irin murya tana karkarwa,
“Minal kiyi min wani taimako karna rasa raina Please”
“Miya faru Deen?”
“Ina son ki bar New York yau yau ki dawo Nijeriya idan ba haka ba zan iya rasa raina”
“Miyasa Deen mi yake faruwa?”
“Kawai kizo idan baki son na rasa raina kinji?”
“Ok gani nan zuwa”
Nan ta aje wayar ta nufi bedroom, Sarah ta rufa mata baya tana tambayar ba'asi,
Cikin yan mintuna ta ɗauki Passport dinta da Atm ta fito, sosai Sarah taso ta hanata zuwan amman sam taki yarda, ganin haka yasa dole tayi Driving ɗinta Airport,




6:24AM......
Ta iso Nijeriya ta tari taxi, bata ajeta ko ina ba sai Gidan Deen,
Fita tayi tana faɗin “Ina zuwa kaji?”
Kai kawai ya ɗaga mata ta nufi cikin gidan,
Ko ina sai da ta duba cikin gidan amman bata ga Deen ba balle alamunshi,
Tsoro ta soma ji , da sauri ta nufi gurin da tasan ya saba aje wayoyin shi, ɗaya gada cikin wayoyin ta sauka ta danna mushi kira,
Ringing ɗaya aka dauka amman ba'ayi magana ba,
“Deen gani gidanka kana ina?”
Ya ɗan daɗe kamin ya amsa mata “Ok gani nan zuwa”
“Ok”
Na aka katse wayar, ido ta tsurawa wayar, ta zauna saman kujera dan sam ta manta da mai taxi dake waje,
Bayan wasu tan mintuna taji parking ɗin mota, tashi tayi ta nufi kofar fita,
Kamin ta k'arasa Saif ya shigo tsaye tayi tana kallon shi har ya k'araso kusa da ita sannan ta shiga leka bayan shi,
Ganin ba Deen yasa ta tsara gefenshi da niyar fucewa,
Fisgota yayi da karfi ya dawo da ita,
“Ina zaki.?”
Yana tambayarta ta tambayeshi,
“Ina Deen”
Fuskar Saif a haɗe yace,
“An salami mai Taxi”
“Bashi na Tambayeka ba ina Deen?”
Baki ya taɓe yasa hannunshi aljihu ya ciro wayarshi ya danna kira, nan da nan akayi picking, Hands-free yasa ya mika mata wayar,
Deen ne cikin rawar murya yake magana,
“Please Deen duk abinda yasa ki kiyi rayuwata na cikin haɗari”
Jikinta a sanyaye tace “Ok Saif mi ya faru da kai?”
Kamin yayi magana Saif ya fisge wayar ya kashe,
Nan ta kalleshi
“Mi kayi mishi?”
“Banyi mishi komai ba yanzu dai zanyi mishi idan baki yi yadda nake so ba”
Ido ta tsura mishi wani irin tsanar shi take ji amman babu yadda zata yi dashi sai ido,
Badan taso ba tace “Na amince zanyi yadda kake so amman Please kada ka cutar dashi”
“Bani Atm ɗinki da passport” Da sauri ta girgiza kai “A'a bazan maka haka ba ask something else”
Kujera ya nuna mata alamar ta zauna, tana juyawa ya fisgota yasa hannunshi aljihunta ya ciro Atm da passport har da wasu yan kananan takardu, ya jefar da ita saman kujerar.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!


NA


KHADEEJA CANDY




_Ina godiya gareku sosai masoya na da makaranta da kuma marubuta yan'uwana Na samu sauki ALHAMDULILLAH_






BABI NA GOMA___10




Cike da nauyin baki Mummy ta soma magana,
_“Asalina ni yar garin Kwara ce ni ibira ce shine yare na kuma yaren iyayena da yan'uwa na, Alhaji Abubakar shine mahaifina ma aikacin banki ne Mahaifiyata kuma Hajiya Amina malamar makaranta ce nice first born a gurin iyayena Kanne na huɗu uku maza mace ɗaya dukan mu iyayemu suna bamu kyakkyawar kulawa da tarbiya baya wasa da karatun mu musamman na addini._
_Daga garin Neja akayi ma Mahaifina Transfer zuwa Yola, nan muka dawo da zama gaba ɗayan mu, koda muka dawo Yola na gama Secondary school, sai mahaifina yasa nati jam cikin sa'ah naci sai ya nema min admission a university,_
_Kamar wasa na fara karatun sai gashi na kusa kammalawa da yake mace ce ni mai maida hankali ga abunda na sawa gaba hakan yasa ban taɓa faɗuwa a jarrabawa ba hakan kuma yasa na samu masoya saosai sai dai bana kula kowa har na kammala karatu na._
_Bayan results ɗina ya fito na sami mahaifina da zancen zan koma makaranta nayi mastas shi kuma ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login