Showing 9001 words to 12000 words out of 115850 words
Chapter 4 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
sauya min tunani da zancen Aure_
_Banyi mashi musu ba na amince dan kawai na faranta musu rai,”_
Shiru ta ɗanyi sannan ta cigaba,
_“A haka Abbana ya bani damar zaɓen duk mijin da nake so, ni kuma duk tarin samarin da suke zuwa kawo min harin banga wadda nake so ba hakan yasa na bawa iyayena zabi duk wadda sukaga ya dace dani. Sun ji daɗe sosai yadda nayi musu sukayi farinciki_
_Bayan kwana biyu dayin maganar mahaifina ya kawo min wani saurayi son kowa kin wadda ya rasa wato mahaifinki kyakkyawa ne sosai fari fes yadda kika ganki babu abunda kika rage a kamaninshi, naji daɗin zaɓin da iyayena sukayi min saboda duk a samarina banga irinsa ba a ɓangaren kyau da iya wanka_
_Wata biyar Abbana yasa na Aurena, duk wani abu da ake bukata na Aure Abbana ya rik'a siya yana aje min_.
_Soyayyah ce ta shiga tsakanin mu sosai idan yazo fira kamar kar muyi sallama, idan abu ya same shi kamar ni ya sama, Wata rana rashin lafiya ta kama shi har aka kwantar da shi asibiti mukayi ta yawon zuwa ganinshi har Allah ya bashi sauki aka sallameshi, bayan ya dawo sai ya dinga fushi dani wai banje gida na duba shi ba, Duk Wani far'ar shi da nake gani sai ya daina na rasa gane kanshi gashi kullum cemin yake ciyon shi karuwa yake,_
_Hakan yasa na yanke shawarar kai mishi ziyarar, duk da nasan Addinina na ya hana banyi tunanin wani abun ba kuma ni a tunanina kamar ba komai bane mace ta kaiwa namiji ziyara tunda naga a makaranta ma friends ɗina suna kaiwa samarin su ziyara_
_Nayi Mamakin yadda na same shi dan ya banbanta da yadda kullum yake faɗa min sam babu alamun ciyo a jikinshi, da kanshi ya buɗe firij ya ɗauko lemu ya zuba min sannan ya dawo kusa dani ya zauna muna fira muna shan lemun, daga nn ban sake sanin inda nake ba”_
Lumshe ido tayi wasu hawaye masu zafi suka zubo mata, bayan kamar minti biyar ta buɗe ta cigaba da maganar,
_“Koda na farka ya aikata alfasha dani! Nayi ta kuka yana bani hak'uri, nayi bakin ciki sosai a hkan na lallaɓo na nufo gida”_
(Daya daga cikin illolin ziyarar ɗakin saurayi ke nan shiyasa duk abunda musulunci ya hanemu dashi toh barinshi shi yafi Allah ya tsare mu da zuri'armu AMIN)
_“Sam ban bari mahaifana sun gane halin da nake ciki ba har na tsayon sati biyu, tun lokacin da abun ya faru Alhasan ya dinga jigilar zuwa gidan mu yana bani hak'uri, ni kuma na juya masa baya naki kulashi hakan yasa sai shi kuma ya daina zuwa, haka sai yasa na kara tsanar shi sai na ɗinga tunanin ko auren shi nayi wulakanci kawai zai biyo baya kuma wata kila ya rik'a neman matan banza maybe ma halinshi ne akan wannan dalilin yasa nace wa mahaifina bana son shi sai mahaifina ya taramu a parlor yana tambayar ko wani abun ne ya shiga tsakanin mu nan nace mashi babu komai shi kuma yace shi dai idan bana son shi zai iya janyewa dan yaga yaga take take na kuma daman mutanen unguwa sunce bana da mutunci bansan girma ba. Bakin cikin furucinshi yasa na tashi tsaye gaban mahaifina na nuna shi da yatsa nace, Eh bana son ka duk abinda kasan ka kawo ka faɗa a biya ka,_
_Baki da da kunya baki da tarbiya a fasa ɗin idan an fasa waye a matsala abun ya fito bakinshi kenan yana rawar kai, a nan ni kuma nace mishi ina da tarbiya alhasan kaine dai baka da ita kuma baka haɗa hanya da ita ba wulakantacce dan karin girma_
_Nan take mhaifina ya watsa min mari yana faɗin taya zamu tsaya gaban idon shi muna faɗin waɗannnan kalamai idan bama son junan mu ai sai mu faɗa ba sai an kai ga haka ba, sai da yayi mana tas daga ni har shi sannan yace idan baya sona ya aiko a karɓar mishi kayanshi, haka ko akayi kamar mai jira sai ga iyayen shi ya aiko wai shi ya fasa Auren kuma duk abinda ya kawo ya yafe Allah ya haɗa kowa da rabon shi, nima ban damu ba dn banyi tunani ina ɗauke da cikin ki ba,_
_Da wani Cousin ɗina Abbah ya haɗa mu, ya saka lokacin Auren mu Wata biyar kamar yadda yasa ni da Alhasan, Wata biyu da faruwar hakan rashin lafiya ta sameni mai tsanani har ta kai bana iya tashi nan mahaifina ya sani a mota da mahaifiyata muka je Asibiti, a nan aka tabbatar min da ina ɗauke da cikin ki_
Nan kuka ya yaci Karfin ta ta kasa k'arasawa, Wani irin sanyi jikin Minal yayi nan itama ta fara zubar da hawaye.
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!
NA
KHADEEJA CANDY
BABI NA TARA___9
BAYAN KWANA UKU.......
Zaune take a parlor tana shan wakar Rahama _(you can in the emergency room)_
Sai ruwan hawaye take tana shafa gashin kanta,
Bugun kofar da taji anayi ne yasa ta share hawayenta ta tashi ta nufi kofar, ta buɗe. Ganin Saif yasa tayi juya zata rufe kofar,
Cikin wani irin zafin nama ya tura kofar ya fisgota abun ka da marar jiki haka ta tafo suww ta faɗo saman faffaɗan kirshinji,
Da sauri ta ɗago tana kallon shi gabanta sai bugawa yake da karfi, cikin ɗaga murya tace,
“Mi ya kawo ka nan bayan duk abunda kake so ka samu ko ko kazo kaje da raina ne?”
Glasse ɗin idonsa ya cire suna haɗa ido tsigar jikinta ta tashi, da sauri ta kawar da nata idon tana haki,
Cikin sanyayyiyar murya ya soma magana,
“Minal banyi duk abunda nayi dan na cutar dake ba nayi ne dan kawai na taimake ki da kuma mahaifiyarki,
Minal tun lokacin da kuka faɗa min dalilinki na yin haka sai tausayinki ya kamani na kasa samun sukuni, ban laifin abinda kika aikata ba dan nima kaina idan haka ta same ni kwatankwacin abinda zan aika ta kenan”
D'ago kai tayi ta kalle shi idonta cike. Da kwallah,
Handkerchief ya ciro ya mika mata yana faɗin,
“Am ready to help you ki gane ko kuwaye iyayen ki Minal nayi miki alkawari zan shige miki gaba har sai kinsan suwaye iyayenki”
Yanayin kalaman shi yasa ta kalli kwayar idonshi, duk da kwarjinin da idon nashi suke mata bai hana ta ganin tsantsa gaskiya dake shinfiɗa cikin idon ba,
Babu alamar wasa ko yaudara a idon shi balle a kalaman shi shima ɗin baiyi kama da masu irin wannan halin ba,
Hakan yasa ta karɓi handkerchief ɗin ta share hawayenta tace,
“Thank you Saif amman am sorry bazan iya ganin Mummy a yanzu ba”
“I know Minal kawai ina son ki je ki tambaye ta yadda akayi kika zo hannunta, kiyi tunani Minal har ba wadda zaki aura ya guje ki saboda haka miyasa ba zaki so sanin wacece ke ba! Ya akayi kika zauna hannun Dr. Salamatu miyasa iyayen ki suka barki wace ce Dr. Salamatu a wajenki duk baki son waɗannnan amso shin Minal?”
Da sauri tace “Ina so Saif ina son sani wacece”
Ajiyar zuciya ya sauke,
“Fine jeki chanja dress ɗinki muje gurin Dr. Salamatu”
Kallon jikin nata tayi wata t-shirt ce jikinta yellow ta rufe mata jiki sai dai bata da dogon hannu, sai saket ɗin atamfa wadda ya kai mata har kasa,
Juyawa tayi ta koma ciki, a hankali ya sauke ajiyar zuciya ya jingina jikin kofar,
Bata daɗe ba ta fito sanye da gown ɗin atamfa sosai tayi mata kyau sai dai kanta ba ɗankwali, tsaye tayi bakin kofar tana kallon shi kamar mai tunani hakan ya tabbatar mishi da kwankwanto take,
Hannunshi ya mika mata,
“I can trust me Minal”
Sai da ta haɗi muyau sannan tace “Ina bukatar nayi shawara da Deen”
Kai Saif ya girgiza mata, “Baki bukatar kowa a yanzu kina tare da Saif just trust me”
Shiru tayi tana kallon hannun nashi kamin ta mika mashi tana hannun,
Sai da yasa a front seat sannan ya saki hannunta ya zagayo ya shiga driver seat,
Hannu ya kai ya kunna wakar TAYLOR SWIFT _(the story of us)_, ya fara driving.
A hankali take satar kallonshi a zuciyarta tana mamakin abunda yasa yake son yi mata wannan taimako ko kuma sanya kanshi cikin sha'aninta,
Wannan duk plan ɗin Mummy ne dan gata na dawo a gareta, haka wata zuciyar tace mata,
Can kuma ta jefama kanta wata tambayar, amman taya Saif zai bar Mummy tayi using dashi? Bayan mutum ne mai akida ɗaya kuma babu wadda ya isa ya sa shi abinda bai tashi ba babu kuɗin da Mummy zata nuna mishi har yaja ra'ayinshi ya mata wannan aikin Saif mutum ne mai zaman kanshi da kanshi how....
“Minal tun lokacin dana barki nan kika kwana?”
Tambayar daya jefa mata ne ya katse mata tunani,
Sai da ta shafa wuyanta sannan tace “Eh a nan nake”
“Kuma shima Deen ɗin a nan yake kwana?”
“A'a baya kwana a nan sai dai yana tayani fira sai dare ya raba sannan yaje ɗayan gidanshi ya kwana wani lokacin kuma ya kan kwana nan”
Shiru yayi wani abu ya tsaya mishi a wuya duk sai yaji ba daɗi, ko babu komai yar uwarshi ce musulma yana kishin yadda take sakin jikinta tana mu'amala da maza yana bakin cikin yaga mace musulma a irin wannan halin,
Kallonshi tayi “Miyasa ka tambaya?”
Shima kallonta yayi ya ɗan sakar mata murmushin gefen fuska “Babu komai”
Daga nn bai sake cewa komai ba ita bata sake cewa ba har suka isa.
Yana yin parking gabanta yayi dakan uku-uku, bai ce mata komai ba ya buɗe motar ya fita,
Bayan kamar minti biyar ya fito ya nufo motar, koda ya buɗe motar baiga kowa ba, nan ya rufe motar ya nufi wajen gidan, sai da ya fita harabar gidan gaba ɗaya sannan ya hango ta jinkine da bangon gidan tana kallonshi.
K'arasa yayi kusa da ita “Mi yasa kika fito? Baki yarda dani bane?”
“Na yarda da kai kawai dai am not ready to meet her”
Ajiyar zuciya ya sauke,
“Minal karki manta badan taji daɗi zakije ki ganta ba no saboda kina bukatar wasu amsoshi ne right?,
Ko bayan haka matar nan bata chanchanci haka daga gareki ba she's take good care of you for more than twenty years duk wani jindaɗi ta baki babu wata ya mace da zata nuna miki gata kina ganin idan kika mata haka kin kyauta kenan after that baki san uzurinta ba”
Kasa tayi da kanta, tana lumshe ido,
“Wannan dama ce a gareki Minal karki bari ta wuce ki”
Hannu ta mika mishi tana ɗaga kai,
Badan yaso ba ya mika mata nashi hannun ta rik'e gam sannan suka nufi cikin gidan,
Rike take da hannunshi har suka isa cikin parlor,
Dr. Salamatu na ganinta ta tashi tsaye da sauri,
“Minal my child”
Bayan Saif Minal tayi ta taɓe kamar wata karamar yarinya da taga abun tsoro,
Hakan yasa Dr. Salamatu ta tsaya bata k'arasa kusa da ita ba ta rungume hannayenta,
Saif ya kalleta “Da kin zauna da yafi”
Ba musu ta koma ta zauna tana kallon Minal, shima Saif a kujerar dake kusa dashi ya zauna, ganin hakan yasa ita ma Minal ta zauna a kujerar daya zauna jikinta na gogar nashi, da yake kujerar zaman mutum biyu cikin dabara ya matsa aka samu space tsakanin su,
Mummy ce ta fara magana “Na sani Minal i hurt....”
Da sauri Minal ta tari numfashinta “Mummy I'm not here to tell me love me or hurt me I'm here to tell me who I really am who is my father and who is my real mother?”
A takaice Dr. Salamatu ta bata amsa “I'm your real mother Minal nina haifeki”
Ido Minal ta sakar mata alamar bata gamsu ba,
A hankali hawaye suke saukowa a fuskar Dr. Salamatu cikin rawar murya tace “Minal zan faɗa miki ko wacece ke a yau zan tona asirin dana shekara ashirin da uku ina boyewa”
Shiru tayi ta noce kai, ganin haka yasa Saif ya tashi tsaye da niyar fita, dan a tunaninshi bai dace yaji sirrin su ba,
Nan itama Minal ta rik'e mashi hannu ta tashi tsaye, Mummy kamar tasan abunda yake ranshi sai ta kalleshi,
“Zauna Saif duk abunda zan faɗa ma Minal zan iya faɗa maka”
Kai ya girgiza zaiyi magana Minal tace “Please Saif for me”
Kasa magana yayi sai ya koma ya zauna ita ta zauna, Sit parlor yayi kamar babu mutane har na kusan minti biyar, sannan Mummy ta ɗago ta kallesu ta fara magana...........
VOTE!
COMMENT!!
SHARE!!!
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!
NA
KHADEEJA CANDY
_Gun zance ka iyawa halshenka wani guri kuma karda ka kai kanka sannan ka zamo mai kare mutunci ka_👌🏿
_NURA M INUWA_
BABI NA GOMA SHA D'AYA___11
Kuka Mommy tayi sosai kamin ta cigaba,
_“Bakin cikin kan iyayena sun yi shi sukace sai na faɗa musu wadda yayi min cikin nace Alhasan ne, nan take suka je suka same shi da batun nan ya karya tani yace shikan ko hannu na bai taɓa rikawa ba kazafi nayi mashi har da cewa sai yayi karata daker iyayena suka samu ya hak'ura Abbah na ya sani gaba sai na faɗa mishi cikin waye na rantse mishi yaki ya yarda ni_
_Tun daga lokacin na soma fuskantar wulakanci ɗaki ɗaya aka ware min kullum ciki nake rayuwa bana zuwa ko ina har cikin ki ya kai sata tara, Ranar wata Laraba naqudarki ta taso min da taimakon mahaifiya na haife ki”_
Dagowa tayi ta kalli Minal idonta na zubar da hawaye tace “Tun da na haife Tausayinki ya kamani na rayuwar da zaki shiga da kuma zuwan wannan ranar da zaki tambaye ni waye ke”
Wata irin ajiyar zuciya Minal ta sauke ta jinginar da kanta jikin Saif. Tana kallon Mummy da ya cigaba da zancen,
_“Duk wace ta haihu tana bukatar kulawa amman ni ban samu ba sai ma lokacin na gane bana da gata abinci yara ake bani ruwan nono na ya soma kafewa a haka na wata biyu ni da ke muka koma kamar masu ciyon kanjamau saboda rama ban taɓa tausayin kaina ba kullum ke nake tausayi, wata rana Abbah na ya fitar dani cikin ɗakin da nake Mamana na kuka ya sani a mota mukayi ta tafiya mai nisa sai da ya kai hanyar dake tsakanin Abuja da Kaduna ya sauke ni ya kuma yi min gargaɗin karna kuskura waiwaiya su da duk dangin su dan na riga na ja musu abun faɗi_
_A gurin ya barni naci kuka sosai na saɓaki a baya ina tafiya idan na gaji sai na tsaya na huta haka na rik'ayi har na kai wani kauye dake kusa da gurin, mutanen kauyen saun tarɓeni sosai ni kuma nayi musu karya nace yan fashi suka tare ni nayi gudu har na kawo kauyen nace musu mijina yana cikin garin Abuja, sun nuna min so sosai suka haɗa min kuɗin mota da rakiyar wasunsu aka kaini tashar garin na hau mota Abuja,_
_Dana shiga cikin Abuja sai na shiga gidajen masu kuɗi bara idan dare yayi sai naje wani tsohon shago na kwana, Wata rana ina halin baran na faɗa gidan Alhaji Mamman, yanayin halin da nake ciki ya bashi tausayi gani da kuruciyata hakan yasa ya sani gaba yana yi min tambaya dalilin baran nawa, ban ɓoye mushi komai ba na faɗa mushi labarina sosai ya tausaya min shi da iyalinshi_
_Daga lokacin ya maidani gidanshi ya rik'e ni yana nuna min gata ni dake cikin yan kwanaki mukayi bulbul bayan na yayeki yace zai maidani makaranta sosai naji daɗi kuma na Amince dan daman abunda nake jira kenan, a matarshi ya sani tare da Matarshi da yar shi Kairat muka je har yola gurin Abbah na ɗauko takarduna nan sosai ya so ya shirya ni da Abbah amman sam yak'i yarda sai ma cewa da yayi wai karuwanci zanje yi da gaggan nayi wannan cikin,_
_Ban damu da duk wani furuci nasu ba tunda ba albarka suka cire min ba kuma daman ni ke nake yima tanadi, yana dawowa ya nema min admission na shiga yin mastas ke kuma ya samo mai rainonki, ina gama mastas ya sake nema min admission na koma University nayi degree a ɓangaren Economics, ke kuma ya saki a Primary school,_
_Bayan na kare karatun ya nema min aiki a kanfanin da yaki aiki, da sannu sannu har aka bani karamar manajan kanfanin, Kina kare Secondary School, na name miki Chartere By act of Congress The American University, Maza da dama sun yita neman Aurena amman naki yarda nayi Auren dan kawai nayi miki tanadi_
_A lokacin Alhaji Mamman ya soma sani a harkokin Siyasa ni kuma na shiga gadan gadan har na samu karamar Minister man fetur, ban tsaya nan ba na shiga siyen hannayen jari ba ɗaya ba duk dan ki samu jindaɗi yadda kowa yake ji,_
_Daf da zaki gama Secondary school na koma gurin dangina ba dan komai ba sai dan nasan duk kika girma sai kinso ganin family ki, sunyi na'am dani a lokacin sai dai kece suka ce ba zasu karɓa ba dansu a dangin su babu shegen dan haka karna na kuskura nuna masu ke_
_Nayi mamakin yadda dangina suke da riko wata kila ko dan suna yare ba hausawa ba, ni kuma tun daga lokacin na yanke shawarar kin haɗa ki dasu dan karsu wulakanta ki,_
_Kina gama Secondary School kika dawo Nijeriya, ni kuma lokacin na sauka daga muka mina sanadiyar chanjin gobnati da aka samu nan ne ke kuma kikace kina son na nema miki makaranta a faransa_
_Bayan tafiyarki karatun ne wannan gobnati ta hau akamin