Showing 18001 words to 21000 words out of 115850 words
Chapter 7 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
my special good friend of mine, Sweetheart you can do it no wrong, my happiness is all yours._
_More grace to your shining star's ROSE OKAFOR Rosy Lurv_
WATTPAD @khadeeja_candy
BABI NA GOMA SHA BIYAR__15
Tana shiga ta faɗa saman gado tana kuka,ta tsora ta sosai da yadda taga Saif irin wannan ranar take gudu, daman hausawa suncd rana dubu ta ɓarawo,ɗaya ta mai kaya.
Wayarta dake saman kujera ta baɗo mata a rai,cikin rawar jiki taje ta ɗauka, ta shiga neman number Mummy. Sai da tayi mata kira biyu sannan ta ɗauka,
“Dan Allah Momi kizo gidan nan yanzu ki ceci raina”
Cikin kuka take maganar tana gurfane a kasa kamar mai rokon gafara. banji mi akace mata ba na dai ga tana girgiza kai
“Eh Momi Saki zaiyi dan Allah kizo yanzu”
Nan ta kashe wayar, ta faɗi kasan carpet gana kukan dake zuwa mata har cikin ranta, ko kaɗan Huda bata son taga Saif yayi fushi da ita, musaman yanzu da take fushin nashi har a fuska, Saif mutun ne mai hakuri duk abunda take masa yakan shanye ya kyale ta idan har taga fushinsa a fili toh lallai ranshi ya ɓace sosai.
Cikin mintuna Ashiri da wani abu Momi ta iso gidan,Huda najin tsayawar Motar ta ta fito da gudu daga ɗakin ta nufo downstairs, Saukowarta yayi dai-dai da shigowar Momi falo, faɗawa Huda tayi jikin Momi tana kuka
“Faɗa min mi kikayi masa miya haɗa ku?”
Momi sai Tambayar take abunda ya faru,ita kuma ta kasa magana sai kuka take, duk hankalin Momi ya tashi,
“Saif ɗin yana nan ne?”
Daker ta iya ɗagawa Momi kai sai wani kara narkewa take kamar wadda akayi mutuwa
“Saifullah! Saifullah!!”
Kira Momi take kwala mishi kamar zata tada gidan,
Yana daga kwance ya soma jin kiran bai amsa ba dan bai ɗauka Momi bace duk da yaji kamar muryar ta, Sai da yaji kiran ya tsanan ta sannan ya tashi a kasale ranshi kuma aɓace ya nufi kofar fita,
Tsaye Yayi bakin Stairs ɗin yana kallon Momi da ke lallasar Huda tana harararsa, haka ya nufo downstairs yana mamakin abunda ya kawo Momi yanzu a gidan dan ba kasafai take zuwan gidan ba. Wata zuciyar tace masa Huda ce ta ta kira ta, Baki ya ɗan tsosa a ransa yana zata iya tunda ba kunya ne da ita ba,
Har ya Karaso Momi bata daina Harararsa ba, cikin girmamawa ya gaisheta
“Momi ina wuni”
Bata amsa masa ba sai kawai ta haushi da masifa,
“Mi Huda tayi maka da zaka sake ta?”
Zaunawa yayi saman kujera yana maida numfashi, ganin hakan yasa Momi ta katsa masa tsawa kamar wani karamin yaro
“Ba da kai nake magana ba kayi min shiru ko nima shashancin zaka yi min?”
D'agowa yayi ya kalleta,
“Momi..-”
Sai kuma yayi shiru, Kallonsa Huda tayi da jajayen idanunta kamar munafuka wani ɓangare na zuciyarta tsoron abunda zai fito bakinsa take dan tasan Momi ma bazata raga mata ba sai tayi mata nata faɗan,
Ido cikin ido ya kalleta yana magana da Momi
“Momi matsalar mu ce da kika sani ta baya Huda ba zata taɓa chanajawa ba sam,nayi faɗa har na gaji bata ji ni kuma na gaji gaskiya da halinta kuma nasha faɗa miki tun baya yau ba”
Zaunar da Huda Momi tayi saman kujera sannan itama ta zauna tana kallonshi
“Saboda ba kasan Miye Aure ba ko? Shiyasa kake son saki a rayuwar ka nayi bakin cikin jin haka daga gareka Saifullah ban taɓa sanin cewa bakan mutucin Aure ba sai a yau,
Duk abunda zaisa Namiji ya saki matarshi Babban abun ne, Amman kai ka ɗauke shi ba komai ba miyasa kake son maida kanka wani irin kalar mutun ne?”
Gashin kansa ya shafa daman yasan indai faɗa ne sai Momi tayi masa musamman yanzu da take ganin Huda bata daɗe da dawo ba. ɓangaren Huda kuma daɗi takeyi tana hamdala da Saif bai faɗi dalilin faɗan nasu ba, ita kanta tasan tayi sa'ar miji dan ba kowa ne Namiji ne zai iya ɓoye sirrin matarsa ba, duk da a koda yaushe Iyaye sukan faɗa mana idan faɗa ya shiga tsakanin ka da Iyalinka toh ka barshi tsakanin ku, dan idan kuka faɗa ma Iyaya koda ku kun shirya kanku ko an shirya ku zaku iya manta abun ammman Iyaye basu manta ba.
A hanlaki ya furta,
“Momi bafa sakin ta zanyi ba kawai ina bata tsoro ne wasa nake mata”
Nan Momi ta saki baki
“Wasa kuma au shi sakin har wasa ake dashi? kasan mi kake faɗa?”
Salon faɗan da take masa sai ya chanja, Shi dai kanshi na kasa har tayi ta gama sannan ya shiga bata hakuri
“Naji duk abunda kika faɗa Momi kuma hakan ba zai sake faruwa ba In'sha Allah Allah ya huci zuciyar ki”
Tashi tayi tana faɗin,
“Kowa dai yayi na gari dan kansa kuma duk abunda kayi wa yar wani sai anyi ma taka, ya dai kamata kayi ma kanka faɗa kasan ciyon kanka ka rika Y'ar mutane da mutunci ba ka wulakanta ta ba”
Juyowa tayi gurin Huda,
“Ke kuma duk abunda kika san yana kawo miki matsala da mijin ki ki daina ki guji ɓacin ransa idan zaki iya kunga tafiya ta”
Bata tsaya jiran mi zasu ce ba tayi tafiyar ta suna mata a sauka lafiya,
Bayan Fitar Momi Huda ta nufo Saif da nufin masa magana ,sai kawai taga ya tashi tsaye yasa hannayensa aljihu ya nufi upstairs,
A hankali ta jingina da kujera tana kallonsa har ya shiga bedroom ɗinsa.
Yana shiga sai yaji duk wani haushi na Huda da yake ji ya karu, ba damar ya sake mata faɗa yasan kiran Momi zatayi ta faɗa mata shi kuma sam baya son Momi taga kamar bai ji maganar ta ba. Can guraren Azahar ya shirya cikin manyan Kaya ya ɗauki makulin motarsa ya bar gidan.
***** ***** *****
Bai shigo ba sai dare. a falo yaci karo da ita kwance saman doguwar kujera sanye da wata rigar bachi mai ɗaukar hankali, baibi ta kanta ba duk da tayi masa sannu da zuwa, haka ya nufi ɗakinsa ba tare daya amsa ba.
WASHE GARI.................
Tun takwas da rabi ya bar gidan dan kwata-kwata baya son huda ta sashi a ido danshi fushi yake da ita bilhakki.
Huda kan bata ma san fitarsa ba dan bata tashi ba sai goma na safe, tana tashi ta nufi kicin ta haɗa masa karrin kummalo dan a zaton ta yana nan tunda bai saba fita da wuri ba. Bayan ta kare ta nufo ɗakinta tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga ta feshe jikinta da turare, sannan ta nufo ɗakinsa,
Haka ta fito sululu kamar hawainiya ta koma ɗakinta idon cike da ruwan hawaye, Tana shiga ta faɗa saman kujera tana share hawaye, wunin ranar wuni tayi cikin ɗaki, Sai kusan La'asar ta fito koshi dan yuwar da taji tana matsa mata lamba ta nufi dinning,ruwan tea ɗazun ta zuba tasha ta sake koma wa ɗakinta.
***********
Saif bai shigo gidan ba sai da ya tabbatar da ta isa yin bachi, rashin ganinta a falo ya tabbatar masa da hakan. wutar falo ya kashe ya wuce ɗakinsa,
Washe gari ma haka yayi mata koda ta tashi ya ficewarsa duk da yake ta tashi da wuri yau, abunka da wadda bai saba ba sai duk tabi ta shiga damuwa, sam baya son Saif ya fita safgarta dan ya riga ya saye mata jiki da zama tare dashi,daga iya zuwa yau duk ta wani chanja ta koma wata kala har da yar ramar rashin cin abincin da take dan iya karta ruwan tea,
Tunani take tayi yadda zata filloma lamarin, Dan tasan haka ɗin da Saif yake mata ba karamin fushi yake da ita ba, kuma shawo kansa sai ta shirya, bayabda saurin fushi kan amman kuma idan yayi yayi kenan sai kuma wani ikon Allah.
***** ***** *****
MINAL............
K'is! k'is!! k'is!! kake ji taunar cingan ɗin da Minal take tana danne-dannen wayar dake hannunta, Kairat na zaune kusa da ita tana rubuce-rubuce jin abun yayi yawa yasa taja tsaki,
“Haba Minal dan Allah ki jefar da cingan ɗin nan tun ɗazu kin damu mutane da taunar cingan kamar wata tsohuwar karuwa”
Harara Minal ta watsa mata,
“Wadda ya raina tsayuwar wata a hawa yake ya gyar idan zai iya ko idan kuma bazai iya ba sai ya zuba ido”
Kairat zatayi magana Talatu ta shigo Gardem ɗin tana faɗin
“Minal ga abokin ki can harabar gida yace a kira ki”
Da sauri ta tashi tana faɗin,
“Toh nama bar miki wajen ci tsinci abinda zaki tsinta”
Tsaye ta tararda shi jikin Mota yana dannar waya, Rumgume shi tayi kamar yadda ta saba,
“I miss Deen?”
Lumshe ido yayi naɗan mintuna ya buɗe ya shafa kanta,
“I miss you too Deen you look so pretty”
Murmushi tayi ta sake shi,
“Thank you ina ka fito?”
“Gida nayi miss ɗin fita dake ne kwana biyu bamu fita ba”
“Oh Deen shekaranjiya fa muna tare”
“Eh but a gida ba waje ba yawo fa nake nufi”
Hannayenta ta ɗaga sama
“Fine indai wannan ne karya dame ka shiga mota muje indai yawo ne”
Murmushi yayi ya buɗe Motar ya shiga, ita kuma ta zagaya mazaunin gaba ta shiga ya kunna motar suka kama hanya.
#Oneheart
_SHOW ME WHAT I WANNA SEE YOUR VOTE AND COMMENT AND DON'T FORGET TO SHARE_
[9/13, 11:19 PM] Auntie Candy: BABBAN GORO...!
NA
KHADEEJA CANDY
_Another one for you ROSY LURV my shinkafa jallof_
WATTPAD @khadeeja_candy
BABI NA GOMA SHA SHIDA__16
Basu dawo gidan ba sai bayan Isha'i, da sauri ta fito Motar ta tana masa sallama ta shiga gida.
Yanayin yadda ta shigo yasa Kairat da tsohuwa dake zaune falo suka tsora ta, Kairat ta dafe,
“Oh Sister miye haka dan Allah zaki shigo ba ko sallama ji duk yadda kika tsorata mu”
“Mtwsss, toh idan kun tsorata sai what ni banda lokacin ku”
Bata tsaya jiran abunda Kairat zata ce ba ta nufi Upstairs da gudu, Tana shiga ta cire kayan dake jikinta ta ɗaura tawul ta shiga banɗaki, cikin yan mintuna tayi wanka tare da alwala ta fito.
Wani ɗan karamin tawul ta janyo ta shiga goge jikinta, a gaggauce ta nufi gaban madubi ta shafa mai, bayan ta kare ta ɗauki wani zane tare da Hijab ta saka ta shiga Sallar magariba da Insha'i,
Tana karewa ta nufi wadurof ta ɗauki wata Night gown ta saka black colour, ta dawo gaban madubi ta shiga gyara gashin kanta, gafe ɗaya tayi da gashinta ta kala masa wani ɗan farin abu tare da ribon, sannan ta ɗauki hoda ta shafa bayan nan bata shafa komai ba sai man baki.
Black Tom's ta ɗauko tasa bayan tasa awani kyakkyawan agogon hannu,
shikan turare bansan iya adadin da ta saka ba, ta daɗe tana kallon kanta a madubi sannan nufo downstairs. Talatu ce ta fara yi mata magana
“Masha Allah Minal kinyi kyau”
Murmushi Minal tayi tayi mata godiya, Tsohuwa ma ta kalleta gana murmushi bata ce komai ba,
“Koma baki ce nayi kyau ba nasan nayi”
Minal ta faɗa tana kallon Tsohowa, dariya Kairat tayi
“Wallahi kuwa Minal kin kyau sosai”
“Thank you sister karku cinye ni”
Dariya sukayi har ita,nan ta zauna suka dasa fira cike da nishaɗi duk da zuciyar ta ta tana can wani guri,
SAIF.................
Kwance yake rairai saman gado, idonsa a lumshe kamar mai bachi ya rumgume hannayensa a kirji yana sauke a jiyar zuciya,
Can kuma ya buɗe ido ya tashi zauna yana duba a gogon hannunsa goma da rabi ya gani, tsaki ya ɗan ja ya tashi tsaye yana mika ya fice.
Zaune take cikin ɗakinta tana rera kuka a hankali kamar karamar yarinya, can kuma taga abun bayayi ta share hawayen ta, ta tashi ta ɗauki makulin Motar ta nufo downstairs, takun tafiyar talkaminta yasa Kairat ta lekowa daga ɗakinta, kamin ta karasa sauka Kairat tace,
“Bai zo ba ko?”
Tsayawa tayi Cak ba tare data juyo ba tace
“Eh kuma kinsan babu abunda na tsana irin Disappointed”
Busar da iskar bakinta Kairat tayi,
“Toh yanxu ina zaki?”
“Clup”
A takaice ta bada amsa still bata juyo ba, Kairat batayi unkurin hana ta duk da bata jidaɗin zuwan da zatayi ba, Sai ma rakata da tayi. bakin kofar falo ta tsaya yana kallonta har ta tada motar ta fice.
Dawowa Kairat tayi cikin falon ta zauna, ta ɗauki rimot ta danna Zeeword. bata daɗe da zaman ba taji ana buga kofa, banza tayi sai da taji an sake bugawa sannan ta tashi ta buɗe, Saif ta gani tsaye jikin kofar hannayensa sanye cikin vaki ya gumɗe baki, kofar tsaki tana kallonsa
“Sannu da zuwa”
Kai ya ɗaga mata,
“Ina Minal.?”
Bai bata amsa ba ya sake yi mata tambayar
“Ina Minal?”
“Ta gaji da jiranka yanzu ta fita”
“Ta fita? Ina taje?”
Ya tambaya yana mamakin fitar ta yanzu cikin dare tana mace,
“Club”
Kairat ta bashi amsa,
“Club”
“Daman tana zuwa Club ne?”
“Eh can ne gurin zuwanta musamman idan tana cikin bacin rai”
Ya mutsa fuska yayi,
“Wane Club.?”
“Club ďin take haďe da hotel ďin City People”
Bai Sake cewa komai ba ya buďe Motarshi ya shiga. Kairat na tsaye tana kallonshi har ya bar harabar gidan.
***********************
Tana isa ta nufi gurin kar6ar tiket kamar yadda ta saba, bayan ta kar6a ta kunna kai cikin Club ďin. Guri ta samu ta tsaya tana kallon mutanen dake kai da kawo cikin Club ďin, bata jin shiga can ciki yau hakan yasa ta jingina da jikin ginin gurin tana wasa da makulan dake hannunta,
Ta daďe a haka sai da taji wakar Rihanna ta tashi _We Find a Love_ Sannan ta ďago da niyar shiga cikin hall ďin sai kawai taji an fisgota da wani irin karfi har sai da bangaji wani akayi waje da ita, Sai a lokacin ta kalli fuskarshi cike da mamaki tace
“Omg kardai kace min kai ma kana zuwa nan”
Hannunta kawai yaja, bai tsaya ko ina da ita ba sai gurin da yayi farkin ďin Motarsa, bayan ya sake mata hannu ya haďe fuskarsa,
“Miya kawo ki Club Minal.?”
“Just to have some fun”
“Fun?”
Ya faďa yana mamakin abunda ta furta,
“Did you hear yourself.? a nan zaki samu Fun Minal kina musulma ďiyar musulma.
idan har wani abun ne yake damunki ai sai ki ďauki Qur'ane ki karanta amman miye Amfanin zuwa Club kina mace musulma kuma cikin dare.?”
Busar da iskar bakinta tayi tana soshe-soshe, yana son kawar da maganar
“You know what yunwa nake ji sosai bari naje gida”
Tana juyawa ya katsa mata tsawa,
“Shiga Mota zamu yi magana”
kallonsa tayi
“Nace maka ina jin yunwa ina son naci wani abu”
Ido ya zaro mata,
“Do as i say”
Da sauri ta nufi Gaban motar ta shiga, dan tsorata da yadda ya ďan zare mata idon da yayi. sai da ta shiga ta zauna sannan shima ya shiga, ba tare daya kalleta ba yace
“Mi yasa kike son ganina?”
Kallonsa tayi,
“Nace maka ina jin yunwa”
“Mi yasa kike son gani na bani amsa”
Jim tayi kamar ba zatayi magana ba, can kuma ta murza hannunta
“I just miss you and..-”
Sai kuma tayi shiru, kallonta yayi
“And what.?”
“Ba komai amman daga zuwan ka sai min tsawa kana min faďa bayan ni babu wadda yakr min haka”
Ido yatsa mata yana kallon fuskarta, ta wani mararaice tana son maida kwallar data zubo mata, murmushi yayi yana mamakin yadda Minal take ďaukar kanta karamar yarinya, gatane yayi mata hawa ko tsabar iskanci ne? tambayar da yayi ma kansa kenan still yana kallon fuskar ta, ta wani turo baki tana sharar kwallah kamar karamar yarinya, murmushi ya sake yi a karo na biyu ya rufe motarsa ya tada,
Fita yayi daga harabar Club ďin gaba ďaya ya nufi wani ristoran dake kusa da gurin, yana yin fakin ya buďe Motar yana faďin
“Fita muje”
Banza tayi masa har ya fita daga motar, sai da taga sai da taga ya buďe ganbun ristoran ďin sannan ta fita ta rufa mishi baya,
Koda ta shiga har ya kama gurin zama, dube-dube take har ta hangoshi, gurin ta nufa,
zaman ta yayi daidai isowar mai wani ma'aikacin gurin,
A hankali Saif ya kalleshi
“Cope only”
Juyowa yayi gurin Minal
“And you Mrs?”
Kallon Saif tayi suka haďa ido, ko wane fuskarsa ba yabo ba fallasa, ďauke idon ta tayi ganin shi yaki ďauke nashi idon tace da mutunen,
“No need”
Kai ya gyaďa mata, Bayan ya wuce Saif ya kalleta,
“Amman kinsan saboda ke nazo nan ko? ke kika ce yunwa kike ji”
“Yes ina jin yunwa amman ba zan iya cin abinci a nan ba”
“Why?”
“Because I'm human”
Kallon mutane dake gurin yayi,
“Su kuma waďan nan mutanen fa?”
“Ba mutane bane”
“And me?”
A nan ta ďanyi murmushi,
“You are human too”
Fuskarsa ya shafa har zuwa saman kansa ya ta6e baki,
“Maybe i m not dan banga banbancina da mutanen da suke wannan gurin ba”
Murmushi tayi mai sauti,
“If not toh miye kai?”
Kafaďunsa ya ďaga
“Ban sani ba nima what i'm?”
Yanayin yadda ya mayar mata da tambayar yasa ta dariya, dariyarta yasa duk mutanen da suke gurin hankalinsu ya dawo gare ta, da sauri ta rufe baki tana matse dariyar,
“What is funny.?”
Saif ya tambaya,Cikin dariyar tace
“You are such an angle Saif”
Lumshe ido yayi ya buďe
“Angle Minal kinsan abunda Angle yake nufi kowa?”
Dai-dai lokacin mutunen ya iso, tashi Saif yayi tsaye ya ciro kuďinsa ya ďora saman tebur ďin ,
“We all done here”
Ganin hakan yasa Minal tashi tana wani abu da baki,
“Minal...”
Daidai lokacin da suka kai bakin kofar fita akayi