Showing 75001 words to 78000 words out of 115850 words
Chapter 26 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt
sallame ta dan haka mu samu mai shayar da ita dan ruwan nono zaifi inganta jikinta saman da komai”
Kai ta da ɗaga
“Wannan ba matsala bane zan iya shayar da ita”
Nasir yayi mata wani kallo,
“Zaki iya Kairat budurwa face ke?”
“Toh miye a ciki ba yata bace sai miye dan ina budurwa?”
Saif ya nufo su yana faɗin
“Safiyyah ma tace zata iya i think...”
“You think what?!”
Ta faɗa kamar a tsawace tana kallon Saif daya karaso gurin kamar a kasale,
“Babu wanda zai shayar da ita sai ni ni zan shayar da yata okey”
Saif dai bace mata komai ba ya kalli Nasir, Nasir ya kalleshi, tana ganin hakan ya juya fuuu ta bar ɗakin.
Bata daɗe ba sai gata ta shigo ɗakin tare da Mummy da Dr isma'il.da Dr Humaira, cikin ladabi Nasir da Saif suka gaida Mummy sannan suka gaisa da Dr isma'il, daker Mummy ta iya ɗaga idonta ta kai dubanta ga Baby, wani irin faɗuwa gabanta yayi ta daɗe tana kallon baby kamin ta kauda idonta da suka cika da hawaye. Kairat ta kalli Dr Humaira
“Dr nice wanda zan shayar da baby i....”
Nasir ya tari numfashinta
“Dr budurwa ce”
Dr tayi murmushi
“Budurwa ce bazara ce tsohuwa ce wannan duk ba matsala bane ni zan rubuta mata magnin da zata sha ruwan nononta ya kawo da kuma abubuwan da za ci”
Mummy ta girgiza kai
“A a Kairat ba zan barki kiyi hakan ba ke budurwace”
“Yes ni budurwa ce Mummy amman ba budurci na zan zubar ba ba mutunci na zan yaga ba shayarda ita ne kawai zanyi na kuma kula da ita kamar yadda Minal ta bukata”
Ajiyar zuciya Saif ya sauke ya ce
“Wannan ba matsala bane Safiyyah ma tace zata iya babu wani damuwa game da wannan”
“Wace irinnSafiyyah wai?”
Kairat ta nufo shi da masifa
“Idan har Safiyyah zata shayar da ita toh babu wanda ya dace ya shayar da ita sai ni dan babu abinda ta haɗa da Safiyyah Safiyyah ba zata shayar da yata ba i won't allow it”
“Safiyyah yar uwata ce Kairat wannan babyn kuma yata ce dan haka Safiyyah na da alaka da ita”
Ido ta tsura masa kamar mai karantar abu a fuskarsa sannan ta juyo gurin Mummy
“Mummy karki juya min baya karki bar wani ya shayar da ita sai ni please mummy”
“No Kairat ba zanyi miki haka ba”
Mummy ta faɗa tana jan hannunta. a nan Kairat ta fashe da kuka ta durkushe a gurin.
Dr. Isma'il ya kalli Mummy yace
“Gaskiya duk kika hana Kairat shayar da yarinyar nan baki mata adalci ba a ganina babu wanda ta dace ta shayar da ita irin Kairat ko dan ke ki rika ganinta kusa da ke kuma itama Kairat ɗin ta samu sassauci”
Saif zaiyi magana Nasir ya rike hannunsa ya rigashi
“Babu komai in dai ta ɓangaren mu ne mun amince Kairat ta shayar da ita”
Baki Sake Saif ya kalli Nasir da mugun mamaki, sai dai ba damar ya musa ma amininsa a gaban wasu sai kawai ya fisge hannunsa daga rikon da Nasir ya masa ya fice daga ɗakin.
Sai a lokacin Kairat ta tashi tana share hawayenta tana kallon Mummy dake hawayen. Nasir yayi fuskar zolaya yana kallonta
“Shi kenan daga magana sai ki faɗi kina kuka kamar wata yarinya, har da zuwa ki kira Mummy dan ta shigar miki ko?”
Harara ta ɗan watsa masa
“Toh ai bata shigar min ba”
Mummy tayi murmushi tana share hawayenta. sun ɗan daɗe a ɗakin kamin daga bisani Kairat tabi Dr Humaira office ɗinta ta rubuta mata maganin da zaisa ruwan nononta yayi saurin kawowa ta kuma faɗa mata abubuwan da zata rika ci wanda zai karawa ruwan nonon inganci.
Saif na zaune parlour ya haɗe rai sosai sai kwafa yake, Momi dai kallonsa kawai take tana mamakin abunda yasa shi yin hakan. Nasir na turo kofar parlour yayi cikinsa da matsifa daman shi yake jira.
“Saboda me zaka min haka Nasir ko an faɗa maka ni bana son kaina ne ko bana sonta ai saboda ina son kusance na da ita yasa nake son a kawo ta a nan gidan a shayar da ita”
Dafa shi Nasir yayi
“Weather you like it or not Kairat ce tafi dacewa ta shayar da yarinyar nan kodan Mummy”
Ya buge masa hannu
“Na nesa da kai ka sani ba kasan na kusa da kai ba, toh ka koma ka faɗa musu ka canja shawara a nan gidan za a shayar da ita”
A nan Momi ta tambaya
“Wai meke faruwa ne?”
Nasir ne yayi mata bayanin komai, Safiyyah dake taɓe ta fito tana murmushi
“Oh Ya Saif daman saboda wannan ne kake ta fushi na na ɗauka ma wani abun ne daban wannan ba matsala bane Yaya da ni da Kairat duk ɗaya muke yadda kaƙe ganin nan gidan ka ne can ma gidan ka ne zaka iya zuwa ka wuni can zaka iya ɗauko yarka kazo nan da ita tun da dai shayar da ita ne kawai Kairat zatayi”
Ka rasasa zancen daidai lokacin da ta karaso kusa dashi, a nan Momi tasa baki
“Haka ne kuma kaga idan aka yayeta ko kuma ta ɗanyi wayo zaka iya maiɗota nan a ciki gaba da bata madara”
Safiyyah tace
“Idan ma hakan baiyi maka ba Yay zaka iya rokon Mummy akan ta bar Kairat ta dawo nan gidan dan Baby kawai nasan Mummy zata yarda dan bata cika matsala ba”
Ajiyar zuciya ya sauke ya zauna saman kujera yana nazarin maganganun. A hankali Safiyyah ta kai dubanta gurin Nsir da ya kafe ta da ido yana mata wani wawan kallo, suna haɗa ido tayi saurin kawar da nata idon ta nufi ɗakinta.
Tana shiga ɗakinta ta maida kofar ta kulle tana safa da marwa, can ta nufi wyarta ta ɗauka ta nanna kira bugu biyu aka ɗauka cikin sauri tace
“Hello Shafa kina ina?............”
*** *** ***
Saif kwana yayi yana nazarin maganar Safiyyah, daga karshe dai ya yanke shawarar zuwa ya samu mummy da maganar Kairat ɗin ta dawo gidan su da zama ɗin dan shi dai baya son yayi nisa da LIL MINAL kamar yadda yake kiranta.
Safiyyah ce zaune a parlour su Shafa tana labarta mata halin da take ciki, Shafa ta kalleta
“Amman Safiyyah miyasa kika bashi shawarar ya bar ta acan a shayar da ita beside miyasa ma kike son shayar da ita?”
glass cup ɗin dake hannunta ta ajeye
“Saboda shi da Momi su yarda da gaske nayi nadama kuma na cire Saif zuciyata su yarda ina son abunda Minal ta haifa, abunda yas nake son shayar da ita saboda a yanzu babu abunda Momi da Saif suke.so kamar wannan yarinyar idan ina shayar da ita dole zai rika kula da ni zai rika tausayina kuma zai ga girma na yace ya shayar da yarsa ta hakan zan samu kansa har sona ya shiga zuciyarsa”
Kai Shafa ta ɗaga alamar gamsuwa sannan tace
“Toh yanzu ya kike so muyi da maganar Kairat?”
“So nake kije gidan iyayenta da suka haife ta ki faɗa musu tana nan ta shirya shan magani dan ta ba yar Minal nono nasan ba zasu yarda ba tunda budurwa ce ba ta taɓa aure daga haka nasan yar zata dawo daga gareni ni bazani ba tunda sunsan fuskata”
Kalkalewa Shafa tayi da dariya tana bugun kafaɗar Safiyyah
“Shegiya kawata baki da kyau”
Safiyyah ta kalleta
“Hmmm ai kowa yaci tuwo dani miya yasha”
*** *** ***
Yadda suka tsara haka kuwa sukayi Shafa ita ta shirya da kanta ta shiga motar ta ta ɗauki hanyar gidan Ibrahim Ahlam.
Bata sha wahala gurin shiga ba dan masu gadin kallo ɗaya sukayi mata ganin ba yar kananan mutane bace suka buɗe mata gate, a natse tayi parking ta fito ta nufi cikin gidan,
Cikin sa'ah ta tarar da Hajiya Suwaiba zaune parlour ta ita kaɗai, guri ta samu ta zauna bayan anyi mata iso, sannan ya gaishe ta cike da ladabi, da far'ah Hajiya ta amsa tana faɗin
“Ban gane ki ba”
“Eh ba zaki gane ni ba saboda baki san ni ba amman nazo miki da maganar ne mi muhimmaci”
Hajiya ta gyara zama
“Wace magana nace haka?”
“Nasan baki san Kairat tana shan maganin kowowar ruwan nono ba dan ta shayar da yar da Minal ta bari, idan kuma har kin sani kika kyale ta to gaskiya kinyi kuskure dan Kairat budurwa ce ba matar aure ba hakan zaisa duk namijin da zai aureta ya rika mata wani kallo, gaskiya ku canja shawara ku samu wata ku biyata tayi muku wannan aikin ba Kairat ba”
Tana kai aya Hajiya ta kalleta ta mugun mamaki tace
“Wallahi bata faɗa min ba ban ma san me ake ciki ba taya zan yarda Kairat tayi haka”
Shafa ta tashi tsaye tana faɗin
“Zaki iya kiranta ki tambaye ta dan nasan ba zata ɓoye miki ba sai an jima”
Bata jira abunda Hajiya zata ce ba ta juya da sauri ta fice daga parlour. Hajiya da kallo ta bita tana mamakin maganar. kasa natsuwa tayi sai nazarin maganar take wata zuciyar nace mata karya ne can dai ta tashi ta nufi part ɗin Abbah.
Cikin sa'ah ta tarar ya tashi daga bachin da yake yana zaune rike da carbi da aƙlama lazimi yake. Sai da ta jira ya shafa sannan tace
“Har ka tashi a she”
“Eh tun ɗazu”
Ya faɗa yana kallonta dan yasan bakinta da magana, tashi tayi
“Bari na kawo maka abinci”
“A a zauna tukuna naga bakin ki da magana ya akeyi.?”
Ajiyar zuciya ta sauke ta shiga kura masa bayani. Kai Abbah ya gingina yana murmushi
“Kairat tana da tunani da hangen nesa yarinya ce mai kaifi basira, tun a bukatar da ta farko na gane hakan”
Hajiya ta kalleshi
“Haba Alhaji budurwa fa ce ba zaura ba ina zan yarda da hakan sam ba zan barta ta aikata wanna kwaɓa ba”
Abbah yayi yar dariya
“Haka zaki gani zaki ga kamar tana shirme amman daga baya zaki gane tana da tunani dan nima haka nayi lokacin da tazo min da zancen Auren Salamatu...!”
Abbah bai ko kai aya ba Hajiya ta daki kirji ta tashi tsaye tana zaro ido,
“Na shiga uku ni suwaiba Kairat ce tace maka ka auri Salamatu? anya Kairat cikin hankalinta take kuwa inna illahi”
Abbah yayi mata wani kallo
“Miye na ɗaga murya haka daga magana Salamatu ce fa sai kace wata bakuwar ki”
“Toh in salamatu ce fa ai daman nasan daga kai Har Kairat ɗin ba banza ta barku ba tun da kurciya ba ayi abu ba yanzu za ayi oh wato ta kwace min miji ta lalata min rayuwar ya ko? tunda ita bata da makoma Toh Wallahi ba zan yarda ba”
Haka ta rika matsifa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, Abbah dai in banda kallonta babu abinda yake har ta gama bururutan ta, ta fice.
*** *** ***
Mummy na cikin bachi ta rika jin hayani ni tun tana ɗaukar mafarki ne har ta farka taga da gaske hayaniya ce ake ko kuma nace faɗa, jin kamar muryar Hajiya Suwaiba yasa tayi saurin saukowa downstairs. Tana kawowa Hajiya ta nuna da yatsa tana hantarar fuska
“Ke kuma munafuka macuciya daga yau sai yau babu ke babu yata bari mijina azzaluma dan kinga baki da makoma ko shiyasa kike son ɓata tawa rayuwar ko wato ki malleke min miji yata kuma ki lalata mata rayuwa to kinyi ƙkaɗan, ni ban taɓa tunani zaki aikata abunda kika aikata ba wallahi”
Ta juyo kan Kairat dake kuka
“Ke kuma kinji na faɗa miki ki haɗa duk abinda kika san naki ne ki bar gidan nan ina xaune na aka zo aka faɗa min komai dan haka ki bar nan gidan tun wuri”
“Haba Hajiya Mummy fa uwata taya zatayi abunda zai lalata min rayuwa ? ba itace tasa ni ba nice nasa kai na”
Kairat ta faɗa cikin kuka,
Hajiya ta hantareta ta hannu
“Aikan ba uwarki bace tun da tayi nufin ɓata miki rayuwa babu ke babu ita daga yau nice uwarƙki nina haife ki”
“Ita kuma ita ta raine ni Hajiya tun ina karama a hannunta na tashi”
Hajiya ta saki baki
“Laaaaa ashe da gaskiyar Zainab au haka ta koya miki ki bata muhimmaci sama da ni dana haife ki?”
Dr.Salamatu da tun ɗazu kallonsu take ta karaso kusa da Hajiya tana faɗin
“Wai me yake faruwa ne ni ban gane kan wannan maganar da kuke ba?”
Hajiya ta watsa mata harara,
“Kin fi kowa sani tun da ke kike shirya komai ni nayi mamakin abunda kike kokarin wallahi wai har ki yarda Kairat tasha maganin nono bayan kinsan budurwa ce koda yake banga laifin ki ba tunda ba Minal bace ai ita tattalinta kike da yake ita ce yar ki Ke kuma na faɗa miki ki haɗa kayanki ki dawo gida in har ba so kike duniya ta juya miki baya ba”
Tana kaiwa nan ya juya a fusace ta fice. Mummy ta kalli Kairat
“Kin gani ko ɗaya daga cikin illar da nake gudu kenan kinga tun ba a kai ko ina ba mun fara ko?”
“Ba haka bane Mummy kishi ne ya rufe mata ido kuma nasan zata sauko”
Kairat ta faɗa tana share hawayenta Mummy tace
“Kishi kamar ya?”
“Saboda naje na Samu Abbah da maganar ya aure ki shine take ganin kamar ƙkece kika tura ni”
Tassssssss! Mummy ta watsa mata mari idonta jawur tace
“Fita ki bar min gida”
Dafe kunci Kairat tayi kamin ta juya da gudu ta nufi Garden.
Tsugunawa tayi gurin tayi ta kuka, sai da tayi mai isar ta sannan ta tashi ta shiga cikin gidan ta ɗauki key ɗin motar ta ta fice daga gidan.
*** *** ***
Ko da Saif ya shigo ya tararda Mummy zaune a parlour jugummm kamar marar lafiya ta tsura ma tv ido duk da hankalinta ba a nan yake ba,
Sai da yayi sallama kusan uku sannan ta ɗago ta kalleshi ta amsa mushi ciki-ciki, bayan sun gaisa ya koro mata bayani akan kudurinsa.
Mummy ta kallesa A hankalce ta soma magana,
“Saif ba zan yarda Kairat ta koma gidan ku da zama ba, Kairat ba Muharrar ka bace komai zai iya faruwa idan har hakan kake so zaka iya auren Kairat dan ta zama mallakinka kaga ita da yarka duk suna karkashin ikon ka da kulawarka,
A halin yanzu Kairat ta canja shawara ba zata shayar da Yarka ba ɗan haka sai ka nemo mai shayar da ita”
Mummy na kaiwa nan ta tashi ta shige ɗakinta, Saif ya bita da kallon na rashin fahimta da kuma mamakin maganarta.
Kamar haɗin baki wayarsa tayi kara yana duba yaga number Kairat kamar kar yayi picking sai kuma ya ɗauka
“Saif kazo ka same ni ina Happy Island”
Tana faɗar hakan ta kashe wayar.
Yana tuki yana tunanin lokacin da Minal take faɗa masa tafison zuwa Happy Island idan tana cikin ɓacin rai saboda guri ne da babu ruwa kowa da kowa ga iska yana kaɗawa babu wanda zai dame ka kayi kukan ka har ƙa gaji babu takura.
Yana yin parking ya hango ta tsaye jikin icce rumgume da hannayenta, ya ɗan daɗe yana kallonta sannan ya karasa kusa da ita, bata jira ya mata magana ba ya ta juyo ta kalleshi idon ta cike da hawaye tace,
“Ka faɗa ma Safiyyah ta fita hanya ta, ni ba irin Minal bace ta kama gabanta kar kuma ta sake taka kafa taje gidan mu dan nasan ita kaɗai ce zatayi wannan kule-kulen tun da Hajiya tace zuwa akayi aka faɗa mata Wallahi idan bata fita hanya ta ba zata san wacece ni!”
“Kaiyrat .....”
Bata amsa mishi ba ba ta kuma tsaya saurarensa ba ta nufi gurin motar ta.
Kamar walkiya, Saif ya iso gida cikin fushi ya tura kofar parlour ya shiga. duk suna zaune parlour har Momi kai tsaye ya nufo Safiyyah yana faɗin
“Me kika je yi gidan su Kairat?”
Zabura tayi dan a tsawace ya tambayeta gashi ya nufo ta kamar xai dake ta,
Cikin rawar Murya tace
“Wace Kairat kuma miye haɗina da Kairat da zanje gidan su?”
D sauri Momi ta tashi ta shiga tsakanin su ganin yadda yanayin Saif ya canja tan tambayar abunda ya faru, daker ya ita faɗa mata abunda Kairat ta faɗa masa. a nan Safiyyah tasa kuka tana rantsuwa
“Wallahi wallahi ban je gidan su Kairat ba mi zai sa naje nayi haka wallahi ban taɓa zuwa gidan ba idan har na taɓa taka kafata zuwa gidan su Kairat kada Allah yayi min rahama”
Tana kaiwa nan ta nufi ɗaki tana kuka. Momi ta kalleshi
“Saif batayi ba tun da kaji tayi wannan rantsuwar akwai dai ko wanene amman ba ita bace Safiyyah ta canja yanzu”
Zaunawa Saif yayi saman kujeara yana sauke ajiyar zuciya.
*** *** ***
Tun da uwar Safiya Talatu take safa da marwa daga bakin gate zuwa ɗakin Mummy saboda wani tsoho da ya takura sai yaga Mummy, wannan karon tana shigowa Mummy ta katsa mata tsawa
“Wai Talatu akwai wasa tsakanin mu ne na faɗa miki bana bukatar ganin kowa a yanzu kije ki faɗa mishi bana da damar ganinsa ko wanene”
Talatu jiki na rawa tace
“Wallahi Hajiya shine ya matsa har da kukansa kuma yace yana tafe da magane mai muhimmaci Hajiya da kin saurare shi ko kaɗan ne dantijo ne”
Mummy ta daɗe kamin ta bata amsa
“Je kice ya shigo parlour”
Da sauri ta tashi ta fice, mummy kuma ta tashi ta shiga bathroom tayi wanka tana fito bata ko shafa mai ba ta saka tufafinta dan bata jin zata iya shafa man, ta ɗauki