Showing 69001 words to 72000 words out of 115850 words

Chapter 24 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

5657

awo uku a ɗakin suna yi mata tiyata, cikin nasara aka yi mata aikin suka fito baby girl sai dai bata da lafiya sosai dan duk a takure take numfashinta ma sai a hankali. suna fitowa da ita Kairat ta nufo su da sauri da nufin karɓar yarinyar jiki har karkarwa yake kamin ta mika hannu Doctor ya rike ta a nan ta kalleshi ta kalli baby,


“Sorry Kairat ba zaki iya taɓa ta yanzu ba bata da isassar lafiyar da za'ayi mata haka a yanzu zamu sata cikin kwalba ne zuwa wani lokaci saboda yar bakwai nin ce”


Ya faɗa yana kallon Baby dake hannun wata nurse, karasa tayi kusa da baby ta tsaya tana kallonta sannan ta risina ta manna mata kiss a goshi. a nan Dr ya ɗaga ma nurse ɗin kai ta wuce da ita, haka Kairat ta bita da kallo har ta ɓace mata da gani. kafaɗunta Dr ya dafa ya juyo da ita ta yadda zata fuskance shi ya soma mata magana a hankali


“Kairat dole ne ki zama mai hakuri you are the only person da Dr.Salamatu zata gani ta jidaɗi sai kuma baby da Minal ta bari,
Dr Salamatu da daɗe da sanin Minal ba zatayi rayuwa mai tsawo ba tana yawan bincika ta akan ciwon ta ni kuma ban taɓa ɓoye mata komai ba duk mai rai dole ne ya yarda da mutuwa ko da kuwa kafiri ne balle musulmi sai dai hanyar da zata zo maka ɗin zata girgiza ka,


Kairat kece zaki cire ma Dr Salamatu kewar Minal dan ke kike zama da ita bai kamata ace ke kika kuka ita tana yi ba mamaci baya son haka addu'ah ku take da bukata idan ke kika kuka waye zai lallaɓa ta ya nuna mata hanyar yin hakurin? you have to be strong nasan ke da Minal tare kuka tashi dan tun lokacin dana fara kula da Minal tare na ke ganin ku tun kuna kanana nasan zaki ji zafi sosai but dole ne ke ki ɓoye naki kukan ki haɗiye damuwarki for the sake of Mummy”


Hannu tasa ta share hawayenta tana kallonsa cike da fahimta, ganin hakan yasa shi cigaba


“Nasan yanzu ta farka dan alluran da nayi mata na awa biyu ne please stay with her wipe her tears”


Kai ta ɗaga masa tana sauke ajiyar zuciya, shi kuma ya sake ta ya nufi hanyar waje. Sai da tayi ta sauke ajiyar zuciya ya fi goma tana share hawaye ya fi a kirga sannan ta nufi hanyar da zata sada ta da ɗakin da Mummy take ciki.


Zaune ta tarar da ita tana murza wata munduwa dake hannunta hawaye na mata zuba, har Kairat ta zauna kusa da ita bata ɗago ta kalleta ba, a nan Kairat ta kai hannu ta ɗago Fuskarta, Mummy kamar mai jira sai ta fashe da kuka tana faɗin


“Lokacin da nayi birthday Minal ta bani wannan abun hannun tace min tana son na sashi a hannuna na rika tunawathat do you remember?”


“Yes i remember Mummy ta baki shine dan ki rika tunawa da ita kiyi mata addu'ah ba kiyi mata kuka ba please Mummy karki ce min baki shirya ma zuwan wannan ranar ba ke da kanki kike faɗa min wata rana Minal zata tafi ta barki har a gabanta kin faɗa ita ma ta sha faɗa miki haka,
ta kan ce miki ko da bata nan ni ina nan kuma nima nace miki haka Mummy ba Minal kawai kika haifa ba har da ni why you behaving like this ko da yaushe sai kice baki da kowa sai ita mi yasa kike min haka? mi yasa kike yi ma Minal kuka a lokacin da take da Bukatar addu'ar ki bata sha faɗa miki ba karki mata kuka idan ta rasu ko bata faɗa miki ba kuma bata tafi ba Mummy sai da ta bar miki copy ta”


Cike da natsuwa Mummy ta kalleta sai ta jata jikinta ta rumgume still tana hawaye


“Kuka shine yake yin kansa Kairat ba sai ana kirasa ba but I will try”


Kamkame ta Kairat tayi tana nata kukan a hankali yadda Mummy ba zata ji ba.




Silent readers run da ba Ku votes ban ya ban ya... 😹


Dear, Readers still a'ce dogon suma tayi? waiting for your comments




BABBAN GORO 43






“Kuka kike yi ko Kairat?”


Mummy ta tambaya jin hawayen Kairat na mata zuba a bata,
Batayi magana ba sai kawai ta kara kankanme Mummy tana cigaba da kukan, a hankali Mummy ta ɗagota ta rika fuskarta ta hannayenta tana murmushin karfin hali


“Ki daina kuka kinji ki daina mata kuka lets go home”


Ta faɗa tana kokarin saukowa saman gadon cikin da karyayyar zuciya.


***


Ganin yadda Saif yake kuka yasa Momi ta haɗiye nata kukan tasa hannayenta biyu ta tado da shi zaune ta rika fuskarsa ta yadd zai fuskance ta


“Kayi hakuri haka Allah ya kaddara maka haka yaso ya kasance a gareka kuka ba naka bane Saifullahi, ka zamo na miji ka yarda da kaddara mamaci baya son kuka musaman ita da ba a ko kai ta makwancintaba addu'ah ce kololuwar soyayyar da zaka nuna mata ka daina mata kuka”


Bai dai na kukan ba sai dai ya sassauta muryarsa ta yadda ita kaɗai zata iya jinsa sai Lubna dake kusa da ita,
Wayarsa ce dake aljihu ta shi ga ringing alamar kira, bai kula wayar ba ya haɗe yawun dake bakinsa ya unkura da nufin tashi Momi tayi saurin rike shi ta zaunar ta kalli Lubna


“Dauko min ruwan sanyi”


Tashi tayi tana share hawaye ta nufi firijin, ta ɗauko mata tare da kofi ta kawo.
Buɗewa Momi tayi ta zuba masa ruwan a kofi ta kai masa a baki. da wani irin karfi yake shan ruwa kamar wanda yayi wata bai sha ruwa ba, yana gama sha ya sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ya ɗosa kansa kan cinyar Momi ya lunshe ido.
Hannu tasa tana shafa kanshi a hankali a zahiri tana tausayin ɗan ta ganin duk yadda ya birkice lokaci ɗaya ya koma kamar karamin yaro.


Taɓa kofar da aka yi yasa Momi ta ɗago ta kalli Nasir da ya kunno kai cikin falon kamar marar lakka jikinsa babu kuzari, yana karasowa kusa da ita ya kai hannu ya ɗafa Saif, da sauri ya buɗe ido jajayen idanunsa ya ɗago yana kallonsa,


“I'm sorry friend”


Shine abunda Nasir ya faɗa yana matsa kafaɗar Saif hawaye na masa zuba,


“Da gaske ne ta rasu kenan!”


Saif ya tambaya idonsa taf da hawaye, kai Nasir ya ɗaga masa yana matsar kuka dake son fito masa.
Hannu Saif ya kai ya shafa gashin kansa ya girgiza kai yana kallon zoben Minal dake hannunshi, bazai manta lokacin da ya karɓe zoben a hannunta ba, tana masa matsifa da faɗar


“I hate you Saif karka cire nin zobe”


Yana dariya yace


“No Minal komai zakiyi sai na ɗauki wannan zoben yayi min kyau Minal i love you”


“Saif no please ni na siya abuna karka cire min ina son abuna Saif bana sonka”


“Really! Bana damuwa da rashin son da kike min ni ina sonki Minal sosai kuma yanzu ne zan nuna miki son”


Ya faɗa yana kara fisge zoben daga hannunta, ganin yadda ta haɗe tai yasa ya rika fuskarta zaiyi mata kiss ta buge masa baki da karfi,bai damu ba ya ya rike fuskar nata da karfi yayi mata kiss ɗin sai kawai ta fashe da kuka, ya rumgume ta tsamtsam kirjinsa yana shafa kanta da bayanta alamat rarrashi, sannan ta kai hannu tana taɓa zoben nata dake hannunsa.


A-hankali ya rika murza zoben yana tuna abunda ya faru hawaye na masa zuba yana sauke ajiyar zuciya.
Ganin hakan yasa Nasir ya rumgumoshi yana buga kafaɗarsa, a nan Saif ya fashe da sabon kuka bakinsa na rawa,
Kiran wayoyi ne keta shigowa ba kakkautawa daga wayar Saif har ta Momi da Nasir duk cikinsu babu wanda ke da damar ɗaga wayar balle har yayi magana,


*** *** ***


Cike da Mutane Mummy ta tararda gidan, da alama sun samu labarin abunda ya faru, bata kula kowa ba ta shiga falonta idonta cike da hawaye. Kairat kan kasa shiga tayi a gurin ta durkushe tana kuka kamar ranta zai fita,


☆ ☆ ☆
☆ ☆



Ko da karfe biyu tayi anyi mata sutura kamar yadda addinin musulunci ya tana da an tsaftace ta an saka ta cikin makara.
Bayan masu yi mata wanka sun fito Mummy ta tashi ta nufi kofar ɗakin tana tafiya kamar ta faɗi, da sauri Hajiya Suwaiba ta rike ta tana faɗin


“A a karki shiga Salamatu karkije ki faɗi kar kije kina kuka kan gawarta kuma kinga ba a son haka”


Hannu mummy tasa ta ɓanɓare hannunta tana haɗiyar yawu,


“Zan iya Suwaiba ba zan faɗi ba, babu abunda zanyi insha Allahu dan Allah karki hani gani Minal”


Sakinta tayi ba dan taso ba sai dan ganin hawayen dake kwance a idonta.
Cikin rashin kuzari Mummy ta karasa kofar ɗakin ta tura kofar bayan ta sauke ajiyar zuciya ta shiga, a bakin kofa ta tsaya tana kallon gawar Minal, Kwance take cikin karaga an naɗeta da farin likkafani, Minal da bata son takura yau gata guri ɗaya ba motsi, yarinyar dake saka tufafi a mai tsada gata a cikin likkafani.
Kau da ido Mummy tayi tana girgiza kai, can kuma ta juyo ta kalleta


“Minal......”


Ta kirata a hankali idonta cike da hawaye, sannan ta karaso kusa ita ta risina ta girgizata, gani take kamar bata mutu ba, ji take kamar ta tashi tayi mata magana. Hannu tasa ta shafi fuskarta zuwa kanta


“Yau na kira ki Minal baki amsa min ba, na girgiza ki baki motsa ba, kaico mutuwa! yau Minal kece a nan kwance kece a cikin wannan shigar,yau zaki kwana ba a gidan duniya ba yau zaki kwana gurin da ba gado ba katifa ba shimfiɗa yau zaki kaɗaita ke kaɗai, shikenan bazan sake ganin ki ba ba zaki gani ba,
Wayyo Allah manzon mutuwa mai gaggauwa mutuwa mai yankan kauna lallai yau ta bakunci gidan mu yau kin tafi kin barni Minal, daman kin daɗe kina faɗamin wannan ranar kin daɗe kina jiran wannan ranar,
Ya Allah ga yata nan Allah ka zama shaida na yafe mata duk abunda tayi min Allah ka yafe mata kurakuranta Allah ka yalwanta makwancinta Allah ka faɗaɗa mata kabarinta Alllah ka karɓi bakoncinta”


Daga nan ta faɗi zaune ta ɗora hannu saman kai tana kuka mai karfi,


“Wayyo ni Allah Wayyo Ni Salamatu farinciki na ta tafi ta barni Wayyo ni Allah na”


Da gudu matan suka shigo suka fita da ita suna bata hakuri aiko kamar suna kara mata kukan sai zo mata yake, har tasa mutane da yawa suma suka rika kukan.


Daf da za a fita da gawarta ayi mata sallah Saif ya shiga ɗakin, Nasir kuma ya tsaya daga bakin kofa.
Yana shiga ya isa gurin da take yasa hannu ya karfi ya buɗe mata fuska, ido ya kura mata yana mata wani kallo, jin yake kamar ya kira ta ta amsa ko kuma tayi masa magana amman ina ta riga ta zama gawa!


“Na yafe miki Minal na yafe miki duk abunda ke tsanin mu kuma zan cigaba da nema miki gafara kamar yadda kika bukata Allah ya jikanki ya yafe miki laifukan ki i love you so much Minal I love more than I did before I love you,
Naso na rayu da ke naso na nuna miki so kin tafi lokacin da nake da bukatar ki kince kina sona taya zan gane bayan kin tafi kin barni miyasa kika barni Minal? tell why!”


Da karfi ya furta yana shishikar kuka, hakan yasa Nasir shigowa ɗakin da sauri ya rikashi ta nufin fita dashi amman ya ki suka rika ja'in ja, sai faɗin yake


“Let me talk to her I want to tell her something”


“Something like what Saif ta riga ta rasu muje waje”


“No babu inda zanje sai ta amsa min tambaya na”


Da karfi Nasir ya kira sunansa ya fisgi hannunsa wanda hakan yasa ya dawo cikin hankalinsa,
fashewa yayi da kuka yana faɗin


“Please Nasir kace min bata mutu ba Innalillahi wa inna ilaihirraji'un”


Rumgumesa Nasir yayi sai duk suka fashi da kukan tare.



**************


Bayan anyi sallah la'asar ne, akayi mata nata sallah, manyan yan kasuwa ne da yan siyasa suka hallarci Sallah jana'izar Minal cikin su har da Alhaji Bashir Bature da Ibrahin Ahlam.
Bayan an kare aka ɗauke zuwa gidanta na gaskiya. har aka kaita aka dawo Kairat bata san anyi ba dan zaune kawai take amman hankalinta baya jikinta kallo ɗaya zaka mata ka gane hakan.
Haka aka rika zuwa ana yi ma Mummy gaisuwa da waɗanda ta sani da waɗanda bata sani ba tun daga kan talakawa har masu kuɗi abunka da mutun mai jama'ah.


*** *** ***


“Assalamu Alaikum Assalamu Alaikum”


Haka ta shigo falon tana sallama da kare masa kallo kamar wata bakuwa, sai da takai tsakiyar falon sannan taji an amsa mata, juyowa tayi tana kallon kofar kicin, Lubna ce tsaye fuskarta ba yabo ba fallasa


tace,


“Ko an sallamo ku ne?”


“Eh an sallame mu tun safe kinsan yau friday anfi sallama friday da kuma monday gidan Gwaggo Muka wuce shine yanzu ta kawo ni ita kuma ta wuce gidan mutuwa, ance rasuwa akayi a gidan ko?”


“Eh Minal ta rasu”


Lubna ta faɗa tana kokarin fashewa da kuka. Ras ras ras gaban Safiyyah ya faɗi kamar yanzu ne ake sanar mata da sokon mutuwar, kasa tayi da ido kamar mai tunani, zuwa can kuma ta ɗauke kai ta kalleta


“Ina Saif.?”


“Yana can gidan tare da Momi”


Ta bata amsar tana share hawaye,


“Allah ya jikanta yayi mata rahama”


Ta faɗa kamar bata damu ba, ta nufi hanyar ɗakinta, maida kofar ɗakin tayi ta rufe bayan ta shiga sannan ta tsaya tana karema ɗakin kallo, tana wani irin murmushi na jindaɗi, daga bisa da ware hannayenta ta faɗa saman gadon tana lumshe ido,


“Mutuwar ki tayi ma Safiyyah rana AlhamdullahI Allah wani nauyin ya ragu”


Abunda ta furta kenan, taja filo ta rumgume zuciyarta ciki da nishaɗi.




WHAT NEXT?


ina Deen?


Wane nauyi aka rage ma Safiyyah?


Ya rayuwar Mummy da Kairat zata kasance ce?


Wane irin hali Saif zai samu kansa?


Ina labarin Huda?




Plenty plenty love guys😍 ku cigaba da hakuri da ni I'm still a lazy Writer, kamar ku lazy readers da basu vote 😢 please vote and comment on every line.




BABBAN GORO 44






Har a kayi sadakan bakwai Mummy bata runtsa ba ko sau ɗaya, yadda take ganin rana haka take ganin dare gaba ɗaya bachi yayi kaura daga idonta tunanin Minal ya hanata sukuni duk ta bi ta canja ta koma wata kalar mace.
Kairat kan abun ya zame mata biyu kewar minal ga kuma damuwar da Mummy take ciki, sai abun ya taru yayi mata tsaye musamman na Mummy da ita take gani yanzu, dan tasan Minal ta tafi inda ba zata taɓa dawowa ba.


Ajiyar zuciya ta sauke ta tashi daga kwancen da take ta sauko saman gadon ta nufo downstairs, a hankali take takawa har ta sauko. a kujerar dake sitting room ta hango mummy zaune ta kafe idonta da wani diary dake hannunta, karasawa Kairat tayi kusa da ita ta zauna, sai a lokacin ta lura da Album ne ba diary ba.
hannu tasa ta karba ta buɗe cike da son sani me ke ciki. hoton farko data fara gani shine na Minal tana rumgume da Mummy tana dariya! da sauri ta rufe album ɗin tana haɗiyar yawu, Mummy ta kalleta tana murmushi mai wuyar fassara


“Kin san abunda yafi damu na?”


Kai Kairat ta girgiza idonta cike da hawaye


“Minal bata taɓa ganin Familyna ba she's always like Mummy yaushe zaki kaini na gansu, yaushe zasu zo su ganni.... na kan faɗa mata ke kaɗai ce family na Minal ke zaki sake ginani kiyi min family na zama kamar kowa yanzu kuma ta tafiyar ta.....”


Dago kai Kairat tayi ta kalleta, hawayen da ta gani a idonta sun sata farinciki, don rabon da taga hawayen Mummy tun bayan an kawar da Minal, ko bata faɗa ba tasan kukan zuci ne take wanda yafi na fili haɗari.
kara matsowa tayi kusa da ita tasa hannu tana share mata hawaye


“Kar mutuwar Minal tasa ki karaya Mummy I believe kema zaki yi naki family kinsan Minal ta bar miki baya kuma nima ina nan, Mummy kar tunanin baya ya hana ki tunani gaba”


Kallonta Mummy tayi still tana hawaye


“Ba zan bari ya zame min ciwo ba saboda sune suka guje na suka wulakanta ni mahaifina na cikina ya kasa ya fahimce yayi min uzuri akan abunda ba da son raina aka aikata shi ba basu cancanci zama dake ba Minal sunce ba zasu karɓe ki ba...”


Jinginawa Kairat tayi da jikinta tana faɗin


“Na sani ko ba daɗe ko ba jima sai sun dawo nemanki sai sun zo gareki Mummy kuma sai sunyi nadamar abunda sukayi miki”


Rumgume ta Mummy tayi tana girgixa kai


“I don't need them”


“Yes Mummy we don't need them”


Sun daɗe a haka kamin Kairat ta ɗago ta kalleta


“Mummy

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login