Showing 57001 words to 60000 words out of 115850 words

Chapter 20 - BABBAN GORO Complete by Khadeeja Candy .txt

02 Dec 2024

5676

a ɓace Cikin muryar kuka tace


“Ba kada hankali Saifullahi daga wani can yaje ya zugo ka sai ka ɗauka dan kawai ka raina yarinyar nan, nasan baka sonta amman ba zaka ɗauki karan tsana ka ɗora mata ba akan me yarinyar nan bata da Uwa ba uba amman kabi ka takura mata me ta tare maka ne? ba zan yarda kana ci mata zarafi ba kabar ganin kai ka ɗai na haifa namiji kana yi mata yadda kake so ina kyale ka, ba zan sake bari ka ci amarta ba ba zaka sake cutar ta ba”


“Momi ina da hujja akan hakan .....”


Ta katse shi,


“Rufe min baki fool wani ya isa ya kawo maka wata hujja ne bada idonka ka kama Minal ba yanzu ka dawo kace wai Safiyyah ce, ɓace min da gani fita kabar ɗakin nan”


Bai iya musu da Momi ba tun tasowarsa, hakan kuma bata taɓa bashi umarni yaki bi ba, yasan wacece uwa dan haka baya son ɓacin ranta, ganin hawayen dake zuba a idonta yasa shi saurin ficewa daga ɗakin,
A harabar asibitin ya fito yana sauke ajiyar zuciya, ya ɗan samu sarari tun da ya bugi Safiyyah har ya sumar da ita duk da ba hakan kawai yaso ba, Huda ce kawai ba zai taɓa sama hannu ba dan yasan maganinta daya tabbatar da zarginsa zai yanka mata ticket.




_KUYI HAK'URI DASHI ZAMA NE BANA SAMU AMMAN IN SHA ALLAH ANJIMA ZAKU JINI LOVE YOU ALL_
[9/17, 10:22 AM] Auntie Candy: BABBAN GORO


NA


KHADEEJA CANDY



®
NAGARTA WRITERS ASSOCIATION (NWA)




*38*


Ya daɗe a harabar asibitin kamin ya nufo gida,
Ko da ya shigo sha-ɗaya saura kwata, ganin kofar Parlour a buɗe ya tabbatar masa da Huda bata gidan,
Kai tsaye ɗakin sa ya wuce, ringing ɗin wayarsa ne ya amsa masa sallamar da bai yi dan karar wayar ce ta tarbe shi, kamin ya karasa ya ɗauka kiran ya yanke, ɗaukar wayar yayi yana dubawa kusan twenty something miss calls ya tarar, Abban Huda ne da Umma ta sai kuma Nasir da wasu two numbers da bai sani ba, tsaki yaja ta wurgar da wayar yasan duk maganar Huda ce zasu masa shi, kuma a yanzu bata gabansa wani haushin ta ma yake ji, yana kokarin cire jallabiyar dake jikinsa aka kara kiran a nan ya ɗauki wayar yasa ta silent, ya ɗaura tawul ya shiga bathroom ya sakar ma jikinsa ruwa.


Ya daɗe a banɗakin daga bisani ya fito rayuwarsa a jagule ya rasa inda zai sa kansa yaji sanyi, Shi tun da yayi aure baya iya cewa ga ɗauraren lokacin da ya kasance cikin farin ciki, duk da auren so sukayi da Huda amman kullun cikin samun matsala suke, idan wannsan ta kare wannan ta taso, ya kara da Minal ita kuma aka zo aka mata wannan sherin, shin sai yaushe zai san jindaɗin rayuwar aure ?
Gashin kansa ya shafa a dai-dai lokacin da ya zauna gefen gado,

“Mi yasa irin waɗannan abubuwan suke faruwa da ni ne? Komai na duniya Allah ya ban amman banda wannan oh god!”


A fili ya faɗa yana matsar gashin kansa, zuwa can ya tashi ya saka kayan bachi ya kwanta saman gadon a rairan yana kallon sili,
Tunanin Huda yake gani yake kamar ba gaske ba ne baza ta iya yi masa haka ba, a nan take zuciyarsa ta soma karanto masa wasu abubuwan da take ɓoye masa da kuma waɗanda ya gani yake kuma zarginta,


“Innalillahi wainna illaihi raji'un”


Wannan shi ake kira da ana zaton wuta a makera sai aka same ta a masaka,
Miyasa bai yi ma Minal uzuri ba? Miyasa bai saurareta ba? Miyasa bai yi bincike akan hakan ba?, Sai a lokacin ya soma tunanin irin kuka da Minal ta rika yi da kuma yanayin fuskarta,


“Miyasa kika amsa kin aikata Minal? Bayan baki aika ta ba? Miyasa?”


_Saboda ba zaka yarda ba,_
Wata zuciyar ta bashi amsa,
Da a'ce tun farko kayi mata uzuri ka saurareta ka kuma yi bincike da duk hakan bai faru ba, da yanzu ka gano gaskiya an wuce gurin, yau gashi har tana asibiti da cikin ka cikin da ka daɗe kana nema cikin da family ka suke so cikin da za'a haifa naka magaji ka samu ɗa ka zama mutun kamar kowa amman aka saka maka shakku a akansa ka kasa bashi kulawar da ta dace,


“Noooooooo!”


Da wani irin karfi ya faɗa ya kai ma katifar gadon wani mugun bugu, wanda na tabbatar da mutum ne sai ya suma,
Fillo yaja ya rumgume yana kuka,


“Oh Minal oh Minal”


Kwakwalwarsa ta cushe tunaninsa ya bushe, wani kara tsana ya ɗorawa kansa da kansa a yanzu, shi kansa yasan bai kyautawa Minal ba sai a yanzu yake ganin laifin kansa. Tashi yayi zaune jin yayi babu wanda yake son gani idan ba Minal ba, A gogon ɗakin ya kallah,
Karfe ɗaya da minti talatin da bakwai ns dare haka a gogon ya nuna, bai damu ba ya tashi ya canja kayan dake jikinsa daga na bachi zuwa kananan kaya, ya ɗauki makullin motarsa ya fice.




*** *** ***


Ko shakku babu kai tsaye ya nufo asibitin, duk da yana tsamanin tayi bachi, amman shi dai ko fuskarta ya kalla ya samu sauki dan jin yake yau idan bai sata Minal a ido ba ba zai iya bachi ba.
Abunda bai yi zato ba ya hanga kamin ya karasa bakin kofar Emargency, Deen ne a jingine da kofar ya rumtse ido fuskarsa a takure,
Toh mi yazo yi asibitin? Kar dai ace gurin Minal ya zo?
Ita ce tambayar da Saif ya rika yima kansa har ya isa kusa dashi Fuskarsa a murtuke kamar bakin kumurci,


“Mi kazo yi asibitin nan ɗan iska matar mutunci”


Ba shakka wannan muryar Saif ce hakan yasa shi buɗe ido ya kalleshi, kamar bakin hadarin gabas haka yaga fuskar Saif babu annuri yana mashi wani kallo irin zan iya ɗaukar ranka,


“Kaji haushi Deen ɗan cin amana mayaudari ɗan shaye-shaye”

Irin wulakantaccen kallon nan yake mashi yana faɗa mashi waɗannan kalaman,


“Na cancanci ko wane irin Suna Saif sai dai ba kai ya kamata ka kira ni da shi ba Minal ce kuma ta ki ta kirani taki ta saurare ni”


“Akan me zata saurare ka banza kawai wulakantance wanda bai san hallacin ba, ai daman baka cancanci tayi abota da kai ba mace da yar uwarta mace musulunci ƴa yarda tayi abota da ita ba irin ku ba”


A nan take idonshi suka cika da hawaye, daman tuni kukan zuci yake a gurin


“Nayi mata butulci Saif na raba ta da farincikin ta nayi sanadiyar tashin ciwon ta, nayi hakan ne da zaton idan na aikata zaka rabu da ita ni kuma na aure ta sai gashi hakan bai samu ba, Safiyyah ta yaudare ni Saif Ita ta zugani na aikata komai ta nuna min idan nayi hakan zan samu yadda nake so, idan mutun nason abu duk hanyar da zai bi ya samu abin zai bi sai idan ba dama ta hakan ne ta ci riba a kaina har ta sani na amanar aminiyata”


Saif ya taɓe baki cike da tsanar Deen


“Bazan taɓa yafe maka ba Deen, ba zan taɓa yafe maka ba”


“Bana son ka yafe min ba yafiyar ka nake so ba wanda nake son ta yafe min ta ki ta kalleni balle ta yafe min ɗin,
Saif ina son kayi min wani abu ɗaya ka rike Minal da amana ka kula da ita dan Minal tana son haka tana son a ko yaushe taji ta jikin wani, Minaƙ bata taɓa ba bada kanta ga wani namiji ba Trust me Saif kai ne farin cikinta”


Yana kaiwa nan bai jira abunda Saif zai ce ba ya share hawayen idonsa ya kama gabansa,
Da kallon tsana Saif ya bishi yana nazarin maganganunshi har ɓace masa da gani, lallai akwai alamar nadama a fuskarsa da kuma hawayen da yaga ni a idansa ga kuma kalamanshi, sai dai har yanzu wata irin tsanar sa yake ji marar musaltuwa, zuciyarsa ta nuna masa Deen babban makiyinsa ne da idan zai samu dama zai iya kashe shi, nikan nace har da dai zafin kishi.

***
Ya daɗe a tsaye yana sauke ajiyar zuciya kamin ya kai hannu ya tura kofar ɗakin,
Mummy da Kairat suka juyo suna kallon shi,
Ras! Ras! Gabanshi ya faɗi dan bai yi zaton suna cikin ɗakin ba, Dakewa yayi kamar ba komai ya gaida Mummy yana kallon Minal fuskarsa ba walwalah,
A maimakon ta amsa mashi sai kawai ta tareshi da waɗansu maganganun


“Saif. Minal tana da bukatar Hutu a yanzu bata son damuwa da duk abunda zai ɗaga mata hankali,
da zaka hakura ka tafi da zaifi kwanciyar hankali tun da kaga bachi ma take”


Dimmm! Yaji ransa ba daɗi duk da ba'a cikin faɗa tayi masa maganar ba, amman yasan me take nufi basa da bukatar shi a kusa dasu,
Ya ɗan karasa shigowa yana faɗin


“Ko da ba zaki barni naga matata ba, nasan ba zaki iya hana ni duba babyn daƙke cikinta ba”


Kairat ce ta yari numfashinshi tana mishi kallon uku saura kwata,


“Minal ba matar ka bace Saif zata dai haifa maka ɗan ka ta baka”


Maganar ta soke shi, sai dai bai ce mata komai ba dan yasan shi ɗin mai laifi ne, dan idan ba haka ba, Kairat bata isa ta tsaya tana faɗa masa waɗannan kalaman ba,
Ganin sun fice yasa shi karasa kusa da ita yana kallon fuskarta kamar a lokacin ne ya soma saka ta a ido,
Hannu ya kai ya shafa cikinta, yanzu fa ajiyar sa ce a ciki wani irin kalar daɗi ya ziyarci zuciyarsa, sai a yanzu yake jin tausayinta yake kuma kara tabbatar da lallai ita ce matar da ta dace dashi tun da gashi an shiga tsakanin su amman sun kasa rabuwa har gaskiya ta baiyyana, gashi kuma just one night Allah ya bashi abunda yake nema,
Wani dogon numfashi yaja ya sauke hawayen dake makale a idonsa suka zuba saman hancin Minal, hannu ya kai ya shafa fuskarta yana murmushi yaja hancinta tunawa da yadda suke wasa lokacin da kazar na da gashi, yasa babban yatsan sa yana shafa gashin girar ta.


Shigowar Dr.Zainab yasa shi saurin share hawayensa ya juwo ya kalleta,
Wani murmushi tayi masa ta karaso kusa dashi tana duba Minal,


“Ina fatar Alkawari na yana nan, ɗazun matar ka ta kirani tana faɗa min ka kore ta”


Basar da maganar yayi kamar bashi dake ba,


“Mi ke damun minal yanzu?”


“Strains ne kawai sai kuma karin jinin da za'ayi mata”


“Karin jini kuma?”


Ya tambaya da fuskar mamaki,


“Yes matar ka na bukatar jini sosai kasan ciwon da yake tare da ita dole a rika mata karin jini kullum,
Dan ciwon nasu tsotse jini yake yi a ko yaushe zaka ganzu a tauye”


Wani irin tausayinta ne ya fige shi sai a lokacin yayi mata kallon tsafta, lallai tana da bukatar jini duk da shi ba likita bane amman yaga hakan a tattare da ita,


“Idan jini na zai yi zanso a ɗiba a saka mata”


Ta ɗago ta kalleshi dai-dai lokacin da ta gama bincika Minal ɗin ta ɗauki files ɗinta


“Muje Office”


Tana faɗar hakan ta fice daga ɗakin,
Shi kan ya daɗe a ɗakin yana kallon Minal yana shafa fuskarta wata sabuwar rayuwa yake ji a game da ita ya samu kansa cikin wani yanayi da shi kaɗai yasan ya ake ji ya kuma san ma'anarsa, sai da yaji ya ɗan damu sukuni sannan ya nufi office ɗin Dr.Zainab.

Kujerar dake fuskantar ta ta nuna mashi alamar ya zauna,
Ta cigaba da gyara waɗansu takardu dake gabanta, bayan ta kare ta kalleshi,


“Nayi magana da Dr Sa'adatu akan jinin da za'ayi mata kari and...-”


YA tari numfashin ta,


“Idan zai yiyu ina son a ɗibi jini na a saka mata”


“Idan muka samu hakan zamu fi jindaɗi, Sai mu auna jinin naka muga idan yazo ɗaya da nata sai a ɗiba, amman duk da hakan zamu nema wani jinin dan bana tunanin jinin ka zai ishe ta”


“Dr wannan wane irin ciwo ne haka?”


“Blood cancer ne i thing ka sani?”


“Na sani amman miyasa yake shan jini haka ne? Na kasa fahimtar wane irin ciwo ne wannan?”


Dr. Zainab ta gyara zamanta ta soma masa bayani a natse


“1 Leukaemia shine medical name na blood cancer ɗin Blood cancers affect the production and function of your blood cells. Most of these cancers start in your bone marrow where blood is produced. Stem cells in your bone marrow mature and develop into three types of blood cells: red blood cells, white blood cells, or platelets. In most blood cancers, the normal blood cell development process is interrupted by uncontrolled growth of an abnormal type of blood cell.
These abnormal blood cells, or cancerous cells, prevent your blood from performing many of its functions, like fighting off infections or preventing serious bleeding.
1. Fatigue
2. Shortness of breath
3. Fever and
4. Bruising or bleeding
5. Joint or bone pain
6. Sleeping problems
Wadannan common signs ɗinsa kenan


They're always on blood transfusion saboda yawancinsu are anaemic coz cancer cells din suna zuqe jini fiye da zato sai su hana normal cells na jikin mutum samun jinin daya kamata”


Ajiyar zuciya ya sauke ya dafe kanshi ya lumshe ido, ya ɗan daɗe a haka kamin ya ɗago ya dake kallonta


“Yanzu babu yadda za'ayi Minal ta rabu da ciwon nan gaba ɗaya?”


Yawun dake bakinta ta haɗiye tana kallon shi,


“Idan har za'ayi treating dinsa akan bi matakai ne guda uku


Chemotherapy-surgery-radiotherapy


Chemotherapy shine farko use of anticancer drugs knn


Radiotherapy kuma ionizating radiation ne ake using a kashe cancer cells din gabadaya kuma shine last stage and yafi tsada,
Sai dai kuma Surgery is not a common option but wani lokaci ana amfani dashi don a yi repairing bone damage”


Ajiyar zuciya ya sake saukewa a karo na biyu still yana kallon ta


“Dr I'm talking about yadda zata rabu dashi kwata-kwata ta zama normal kamar kowa”


“Shi fa cancer before ayi treating ɗinsa dole sai anyi considering abubuwa kamar haka:
- Ko kinada ciki
-Whether you've had another cancer in d past
-The cancer cell location


Kuma shima stages ne, in ya zama cronic to sai Allah‬ dan gaskiya basu cika surviving ba shi yasa zaka ga they're always depressed,
First stage is marked by an enlarge presence of lymph nodes
Second stage is marked bythe enlarged presence of spleen as well as liver
Sai third stage is marked by d development of anemia,
Na karshe 4stage din shine by a drastic full in d rate of blood platelets
D 3$4 are more risky
D 1 responded better more dan sauran”


“What do you mean?”


Ya tambaya hankalinsa a tashe, sai da ta nisa sannan tace


“Zaka iya rasa Minal a ko wane lokaci saboda ta kai matakin da ba baza a iya treating ɗin ta ba”


Dif ya ɗauke wuta na ɗan lokaci,sai da ya sauke ajiya zuciya sannan numfashinsa ya dawo normal,


“I hope kasan ba ciwon cancer bane kawai yake damun Minal, tana da sickler”


Da sauri ya tashi tsaye,


“Ya isa Dr muje kawai a ɗibi jinin nawa”


Ba musu ta tashi suka fice tare.




* * *


Bayan sun auna sun ga jinin nashi zai yi mata suka ɗibi gora uku, sun rubuta masa magani suka kuma faɗa masa abubuwan da zai ci waɗanda zasu kara masa jini,
Shi dai har akayi aka gama tunanin Minal ake hankalinsa yana gurinta ana gamawa ya nufo ICU,
Bachi take har yanzu hankalinta a kwance, ya daɗe yana kallon fuskarka daga bisa ni ya kwanta gefenta saman gadon cike da tausayinta, yasa hannunsa ya ɗan tallabo ta ya rumgume ta tsa-tsam,


“I will always stay Minal I never wanna lose you, ke ce farin ciki na,
A yanzu ke ce kaɗai fata na ba zan iya rayuwa ba ke ba I love more than I did before ko da kin guje kin ki ni Minal nothing's changed no one could take your place and I'm sorry that it's this way but I will be with you I'm here with you I will stay”


Kamar a mafarki take jin kalaman, sai dai digar hawayensa a kan fuskarta ya tabbatar mata da ba mafarki bane, cikin hanzari ta buɗe idonta sai kawai ta jita jikin mutum kam-kam ya rumgume ta, tasan Saif saboda kanshin turarensa da taji kuma tasan duk duniya shi kaɗai ne yake iya yi mata irin wannan rumgumar mai kara mata son shi,
Amman hakan bai hanata unkurin son raba jikinta da nashi ba tana ihu,


“Shiiiiiiiiiiiiii stop shouting”


Ya faɗa yana shafa gashin kanta yana kara rumgumeta ya yadda ko motsin kirki ba zata iya ba,


“Saif ne mijinki ne Minal i miss you so muchi please karki raba ni da jikin ki”


Bata saurara ba ta cigaba da kaceniyar ganin ta kwaci kanta amman ina karfin namiji da mace ba ɗaya ba gashi daman ba wani karfi ne da ita sosai ba, yi tayi har ta gaji amman ta kasa kwatar kanta shi kuma yaki ya sake sai ma kara matse ta yake da kirginsa ta a dole ta hakura,


“I hate you more than you think I

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login