Showing 114001 words to 117000 words out of 124539 words

Chapter 39 - LALATA BOOK COMPLETE DOCUMENT By Sadnaf .txt

Sadnaf   

11 Dec 2024

9277

ne yasa yace tahau sutafi,ta hau dasauri suka dau hanyar rijiyar zaki,gani tayi kamar mai adai daita sahun,baya sauri dan ayanda take jin zuciyarta in ba ganinta tayi agidan izzadeen ba hankalinta ba zai taba kwanciya ba,tafiyar minti 6 ne yakaisu kofar gidan izzadeen tayi sauri ta fito ta sallami mai adaidaita sahun tayi cikin gidan izzadeen, buga kofar palon tayi da Iya karfinta dayasa suhaima mikewa Daga kwance ba shiri,izzadeen dake bandaki ya wular da abun dibar ruwan dayake wanka dashi, ya fito waje dasauri ya zura doguwar Riga ya dauki ya dauki wani wuka daya ajiye akarkashin gado yyi waje dan duk atunaninsa el Bahrain ne yadawo,turus yayi dayaga Fateema Ce atsaye ta rike kugu,tana harare,daura fuska yayi,ke lafiya mai kike nema agidana,dalla jaki rufemin baki,ingaya maka abinda yakwoni dan bakada gidan dazanzo,wato sabida akuyanci irin naka kana da guts din da Aunty tasleem ma tayi aure,bazaka kyalleta ba ka cigaba da bibiyarta,kai wane irin dabba ne Ka wargatsawa yayata rayuwa amma duk hakan bai isheka ba,tayi auren ma kanaso ka Kara wargatsa mata rayuwa,izzadeen wlh zan maka rashin mutunci tunda naga alamar kwakwal kifi Ce dakai,ke juya kibarmin gida kafin in hambarar dake, dama abinda yakwo ki gidana kenan,na bibiyeta din sai ma na kashe mata aure hankalina zai kwantar,karya kake wlh sai dai auren uwarka ya mutu badai na yayata ba,fita kibarmin gida kafin naci ubanki,babu inda zanje dan ubanka,har kai kanada gidan dazanzo zua nayi namaka gargadi da babbar murya wlh kafita harkar yayata in bahaka ba,in bahaka ba mai zakiyi, izzadeen yace yana nufar inda take tsaye, kifadamin inbhaka ba mai zakiyi,ke inaga dan bantaba cin ubanki ba shiyasa kike min rashin kunyar dakika ga dama, amma yau zan miki akuyancin da inkika gani ahnya sai kin gudu,yau zan sauke miki fitsarar dakike ji dashi,kirjin Fateema ne yafara dukan Tara Tara,ta wayance kai din banza dazaka ci ubana sai dai muci uban juna dan ni ba tsoronka nakeji ba,to shikenan,zakici ubanki,ya wurgar da wukar hanunsa ya damko hanunta yafara janta zaiyi hanyar dakinsa da ita, duka Cizo da yakushi tafara kai masa da daya hannu yaki yacikata yacigaba da janta,suhaima dake tsaye abakin kofa, tun lokacin dasuka fara musayar kalmomi ta yi folding hanunta tana kallonsu,ganin yayi hanyar dakinsa da ita ne yasa tayi sauri tasha gabansa ina zaka kaita, mai tayi maka Ture ta yayi Daga gabansa,yaja Fateema dakarfi yasata adakin ya kullo kofar Fateema tasa ihu, suhaima tayi waje da gudu,tanufi gidan el Bahrain ba dankwali ba takalmi




tasleem tun lokacin da Fateema takashe wayarta hankalinta ya tashi,tafara sintiri adakinta dan Neman ciwon kan datakeyi tayi ta rasa,dan tasan tunda Fateema ta kashe wya ranta bakaramin baci yayi ba,takua san in haka ne Fateema sai ta dau mataki adaren nan nan,bata bari ya kwana,dan bakaramar zuciya ne da ita, ganin zirga zirgan ba amfani zai mata bane yasa tashiga bandaki dan ta watsa ruwa dan wani zafi zafi taringa ji






Bangaren el Bahrai kua bayan ya kwashe aman yakoma dakin Yusrah yaje yasameta ta rufe ido tana ta mayar da numfashi,zama yayi agefenta yaringa mata sannu, minti biyar da zamansa yaga har bacci yayi awon gaba da ita, girgiza kai yayi dan tunda tasamu ciki take yawan bacci dan sai kuna hira da ita sai tafara gyangyadi kafin Ka ankara bacci yayi awon gaba d ita,kiran sallahr isha dayaji ne yasa ya tashi yayi alwala yayi waje dan yatafi massalci,yana dab da zua gate, yaga suhaima ta bude kofar tashigo aguje,ke lafiya yace atsorace yana ja da baya dan haka kawai yakewa suhaima kallon tababbiya,nuna mishi waje taringayi da hannu tana magana da kyar,kanwar matarka tasleem izzadeen yakamata yasata adaki zai mata fyade, What el Bahrain yace yana zaro ido,Fateema kike nufi gyada masa kai tayi,waje yayi dasauri suhaima tabi bayansa,tasleem da tana fitowa Daga bandaki jikin window taje ta tsaya tana shan iska dan jitayi duk datayi wanka zafin takeji,ganin suhaima tashigo dagudu el Bahrain yayi waje da gudu suhaima tabi bayansa ne yasa tafara Jan innalillahi wa inna ilahi rajiun dan tasan koma mai yke faruwa Fateema taje gidan izzadeen.
[2/26, 7:18 PM] My Mom: πŸ‘„LπŸ…°LπŸ…°TπŸ…°πŸ™Š




*written by*
πŸ’…πŸ’… *sadnaf*πŸ’ž








Page 154


Fateema kua dakarfi taringa jijiga kofar tana ihu,izzadeen ya damkota ya watsar da ita akan gado,bake karamar er iska ba kibiyoni har gida sabida bakida mutunci,yau sai na koya miki hankali dan dama nadade ina jin haushinki,in ahanya kika gani aka Ce ki Daga ido ma ki kalleni bazaki Iya ba ballanta yakai ga ki min rashin kunya,kokari cire doguwar Riga jikinsa yafarayi,tana ganin rigar yarufe masa fuska ta dira cikin zafin nama ta tureshi hade da kamo fuskarsa da rigar yanda bazai Iya cirewa ba,kokawa suka farayi sosai inda yasamu ya Ture Fateema ta fadi akasa ya maida rigar jikinsa ya kamato ya kwada mata mari,yafara kicin kicin cire mata hijabi,baki tasa ta gartsa masa cizo ta rike fatar taki cikawa,ya saki ihu da Iya karfinsa yaringa ball da ita taki cika mishi hannu,dan so take sai ta cire fatar,daya hanun yayi amfani dashi yakamo nononta,itama ta saki ihu adai dai lokacin da el Bahrain suka karaso yafara buga kofar da karfi,izzadeen kana da hankali kua? kasan mai kake shirin aikatawa kua,ihun Fateema daya kara juyowa ne yasa yafara bugun da karfi,suhaima tayi dakinta da sauri ta daukowa el Bahrain bunch of keys din gidan yakarba cikin rawar jiki yafara gwadawa






Tasleem kua Riga ta zura jiki na rawa,tasa hijabi,tanufi kofa taji akulle wajen side bed tayi dagudu,ta dauko mukullaye tazo tayi ta gwadawa har sai datasamu Wanda ya bude,tayi waje dagudu ba takalmi,tashiga gidan izzadeen, adai dai lokacin el Bahrain yayi nassarar bude kofar, tasleem tasaki ihu dan duk atunaninta izzadeen yagama da Fateema,izzadeen kua alokacin yayi nassarar cire mata hijabi ya wurgar dan so yake ya tsoratata bawai wani abun zai mata ba,dagudu el Bahrain yafada dakin ya kamo izzadeen yakwada masa mari,kan ya sauke hanunsa shima ya zuba mishi nashi Marin,kokawa suka farayi,tasleem tayi wajen Fateema dagudu data rike kirjinta tana maida numfashi,dagota tayi ta kwada mata mari, kinada hankali kkua Fateema mai yakawoki wajen izzadeen da yanzu yamiki fyade fa mai yasa bakida hakuri ne arayuwarki,tasleem tace cikin muryar kuka hawaye na zubo mata,haba aunty tasleem abinda izzadeen yake mana ya isheni,aunty abin dayake mana yayi yawa, mai mukayi mishi dayakesan ganin bayan mu,tace tare da fashewa da kuka,ihun el Bahrain dasuka jiyo ne yasa suka juya sukayi gurin dasuke suna fada,dan izzadeen shima dagewa yayi yaringa rama dukan da el Bahrain ke kawo mishi, inda el Bahrain ya fusata yakai mai bugu ahanci izzadeen shi kuma yakamo hanun ya ciza,suhaima rike izzadeen tayi tana jansa tasleem ita kuma tarike el Bahrain,Fateema kuma tayi waje dagudu tadauko wukar da izzadeen ya wular dazu,tayo ciki dagudu,suhaima kua ganinta datayi da wuka ne yasa,tasaki ihu,wuka wuka wuka,izzadeen shima daya hangota cika el Bahrain yayi,yayi bandaki dagudu,Fateema ta bishi aguje,el Bahrain da tasleem suka bi bayanta aguje,tasleem ta damketa,el Bahrain kuma ya kwace wukar da karfi,ni ku kyalleni in kashe shi in huta,izzadeen yahana mu zaman lafiya ku kyalleni dan Allah in kashe shi,jijigata tasleem tafarayi tana cewa " kishiga hankalinki Fateema mai ya ke damunki ne" tasleem duk laifinki ne dan dabaki gayawa Fateema abinda ke faruwa ba,babu yanda zaayi hakan tafaru ke da kikasan halin kanwarki,el Bahrain yace cikin bacin rai,Ku wuce mutafi,yace yana nuna musu kofa,Daga tasleem har Fateema kuka sukeyi,sukayi waje,yabisu abaya,suna zua waje fateema amadadin tabi tasleem cikin gidan ,hanyar tafiya tayi,el Bahrain ykira sunanta ta tsaya,tasleem taje ta tsaya agabanta,kzo ki wuce mutafi,aa gida zan wuce dan su Umma basu san nazo nan ba, Fateema yanzu kina nufin Umma batasan kinzo nan ba,maiyasa bakida hakuri ne,yanzu badan muna nan ba,da Allah ne yasan abinda zai faru,el Bahrain yace cikin takaici jirani indauko mota inkai ki gida yajuya yayi cikin gida,






Tasleem goge hawayen dake zubo mata tayi,ta rungume Fateema,kiyi hakuri sis duk ni najanyo miki,da ban fadamiki ba dahakan bata faru ba,hakika kin nuna min kauna,sis banida sama dake, amma pls kiringa kokari kina kai zuciyarki nesa pls,insha allahu sis zanyi kokari,amma Aunty abinda izzadeen yake mana yayi yawa,dafarko ya LπŸ…°LπŸ…°TπŸ…° miki rayuwa yanzu kuma yanaso ya KπŸ…°SHE miki aure abin nasa yayi yawa,hakane sis kiyi hakuri izzadeen bai isa ya kashemin aure ba,sai dai in lokacin mutuwar auren ne yayi,ba ma zai mutu ba insha Allahu Aunty, tace tana share hawayen dasuke zubo mata, kishigo mutafi el Bahrain yace alokacin daya tsaya agefensu da mota,jeki sis, kina isa gida ki kirani, to aunty tace alokacin data shige motar, tasleem ta karasa wajen el Bahrain ta rukufa,tace kamal adawo lafiya Allah ya kikaye hanya,dagowa yayi yana kallonta wani so da tausayinta na ratsa shi,yace ameen yaja motar suka tafi, tun amota yaringawa Fateema nasiha data ringa hakuri har suka karaso kofar gidansu yana mata nasiha,godiya tayi mishi,tace yaya kamal dan Allah dan Annabi karinga hakuri da aunty tasleem wlh izzadeen so yake ya rabaku,dan Allah Ka rike ta da amana, dan wlh farincikin aunty tasleem shine nawa, dan haka kawai tunda muka taso da aunty tasleem take ban tausayi dan batada baki,duk abinda aka mata shiru takeyi tace hawaye na zubo mata,karki damu Fateema zan kular miki da tasleem dan ke farincikin ki Ce nikua rayuwata ce, dan haka ki kwantar da hankalinki,wani irin Farinciki ne ya lullube Fateema ta rusuna tana mishi godiya, ahaka sukayi sallama, yaja motarsa ya tafi ita kuma tayi cikin gida.
[2/28, 6:06 AM] My Mom: πŸ‘„LπŸ…°LπŸ…°TπŸ…°πŸ™Š




*written by*
πŸ’…πŸ’… *sadnaf*πŸ’ž








Page 155


Tana shiga cikin gida parking space tafara dubawa taga Abba bai dawo ba, hamdala tayi, tayi cikin palo, Umma ta tarar tana ta zirga zirga apalo,kirjinta ne yahau dukan uku uku dan bata san karyar dazata shararawa Umma ba,sallama,tayi atsorace Umma ta juyo dasauri,"Fateema ina kika tsaya tundazu Daga siyan magani sai da kika samu awa daya duk kinsa hankalina ya tashi,ina tunanin ko wani abun ne yafaru," Umma wlh kaina ne ya matsamin da ciwo lokacin Dana fita shine na shiga gidan aunty Bilki na aiki almajirinta ya siyo min maganin,Dana sha bacci yadaukeni sai da aunty Bilki ta tasheni," ajiyar zuciya Umma tayi tace Allah ya sauke dadin danaji ma abbanku bai dawo ba,wuce kije kici abinci ki kwantar,dakinta ta wuce umma ita kuma ta zauna ta kamo tashar Arewa 24 tana kallo,tana shiga dakin ta dauki wayarta ta kunna takira tasleem,bugu daya ta dauka,"sis kun karasa gida ne cewar tasleem," ee Aunty mun karaso ya ma tafi," hope Umma batayi miki fada ba," batayi min ba,gidan Bilki nace mata na shiga,yauwa haka nakeso sis kiyi sallah ki kwantar gobe zan kiraki,yauwa Aunty inataso in tambayeki hope Yusrah batasan abinda ya faru ba? Batasani ba gaskia kuma bana jin el Bahrain zai fada mata,Allah yasa bata sani ba dan kinsan inta sani akwai Matsala, karki damu batasni ba,to shikenan aunty sai dasafen Allah ya tashemu lafiya ameen ta katse wayar ta ajiye agefen side bed ta zauna agefen gadon ta rike kanta, tana tunanin abinda yafaru,kwalla ne suka zubo mata,afili kuma tace Allah ya isa tsakaninmu dakai izzadeen.






Bangaren el Bahrain kua ahanya ya tsaya ya musu takeaway,yakarasa gida,bangarn Yusrah ya nufa,yana shiga dakinta yaje ya tarar still baccinta take bata tashi ba,kan gadon yakarasa ya zauna yafara tashinta,bude idanta tayi tana kallonsa,murmushi yayi yace na tasheki ko?girgiza kai tayi,yace tashi kiyi sallahr isha, nasiyo mana abinci, inkin idar kizo muci abinci,nima bari naje nayi alwalar ,to yaya tace tare da mikewa,tayi hanyar bandakin,mikewa yayi shima yayi yafita waje, dakinsa ya nufa ya daura alwala, yayi sallah,sai daya Dade yana. Musu addua zaman lafiya tsakaninsa da matansa yakuma roki Allah da ya karesu daga Sharrin izzadeen,sanan ya Shafa ya mike yayo waje,bangaren tasleem ya nufa,apalo yaje ya tarar da ita azaune ta zuba tagumi tana kallon waje daya da alama tunani take dan batasan da shigowarsa,sallama yakarayi akaro na biyu da karfi,tayi firgigit ta dago ta amsa,sannu da zua tace tana sunkuyar dakai,amsawa yyi yana Daga bakin kofa,zo muje muci abinci,mikewa tayi tace lah na manta ban Dora ba dan Allah kuyi hakuri, bari na dafa mana ko indomie ne,tace tana yin hanyar kitchen, kibarshi nayo mana takeaway,kizo mu tafi yace tare da juyawa," kamal" tsayawa yayi cak batare da ya juyo ba,takarasa gabansa ta durkusa dan Allah dan Annabi kayi hakuri bazan kara kwatanta fita batare da izininka ba,dagota yayi yace karki damu nahakura,wuce muje, yace tare da riko hanunta,palon Yusrah sukayi,suka tarar da ita azaune da hijab ajikinta ta dauko plates ta juye abincin tana jiransu,dagowa tayi ta amsa sallamar dasuka mata tasaki murmushin jin dadi data ga hanunsu arike Dana juna dan tasan sun shirya,tasleem zama tayi agefen Yusrah,el Bahrain shi kuma ya zauna agefen tasleem,atare suka fara cin abincin inda el Bahrain da Yusrah ne kawai ke cin abincin,tasleem tsakura kawai take bawani ci take ba, sai daya mata magana tafara cin abincin sosai,ahaka suka kamalla cin abincin,tasleem ta kwashe plates din takai kitchen, tadawo ta zauna, el Bahrain mikewa yayi yatafi dakinsa,Yusrah da tasleem suka bishi da kallo,tasleem saurin goge hawayen dake Neman zubo Mata tayi dan tasan el Bahrain kawai cewa yayi ya hakura amma da wani Abu azuciyarsa,Yusrah dawo da kallonta kan tasleem tayi, tace" Aunty tasleem wai mai kikayi wa yaya ne? hawayen datake ta boyewa ne suka zubo mata tarasa amsar dazata Bawa Yusrah, yi hakuri Aunty tasleem bansan tanbayar Dana miki zai bata miki rai ba,girgiza Kai tayi tace baki batamin rai ba,tace tana goge hawayen dasuka zubo Mata, bari nje na kwantar sai dasafe,Allah yakaimu Aunty tasleem,tayi waje, Yusrah ta girgiza kai tace Allah ya sasanta ku,ta mike tayi hanyar dakinta








Bangaren izzadeen kua sai daya tabbatar da tafiyarsu ya fito,suhaima dake tsaye adakin ta kwashe da dariya,tace Ashe mijjn nawa matsoraci ne har tsoron mace yake, azuciye yayi gurinta tana kokarin guduwa ya damkota ya rufeta da duka sai daya mata lilis ya watsar da ita waje,ya rufo kofar dakinsa,suhaima taringa jera masa Allah ya isa,izzadeen kua zama agefen gado,yana daya sani bai tari tasleem ba,gashi abubuwa sun kwabe, gashi jibi ne daurin aurensu da Mufeeda bai so suka samu sabani da el Bahrain ba,haka yazauna yanata tunane tunane,yaga ba tunanin ne mafita ba ya mike yje ya dauro alwala,yazo ya tayar da sallah




El Bahrain kua bayan yaje yayiwa tasleem sai da safe yadwo ya kwantar, tunanin yaringayi yanda zai nisanta tasleem daga wajen izzadeen,dan ya tsorata da kalmomin da izzadeen dan yasan halinsa tabbas zai Iya rabashi da tasleem, juyi yayi ya rungume pillow,Yusrah kua dama ba bacci take ba itama dan haka kawai taji bata jin bacci,yaya Ka kasa bacci ko,tace tana kallonsa,girgiza mata kai yayi tare da kara kankame pillown ya rufe idansa mirginawa tayi kusa dashi ta cire pillown ta maye gurbin pillow ykua rungumeta,aikua nan da nan bacci yayi awon gaba da ita,shikua ba bacci ne yadaukeshi ba sai daya samo wa kansa mafita,bacci ya daukeshi,karfe biyu da rabi ya mike afirgice yana sallati,dan mafarki yayi izzadeen yashiga dakin tasleem yadaukota akan kafadarsa ya gudu da ita,tasleem tana ihu tana Neman taimako,durowa yayi Daga kan gadon ya yi bangaren tasleem aguje,Yusrah ta mike tana sallati,dakinta ya shiga dagudu,tasleem dake zaune akan sallaya,ta mike tana sallati,nocsol md lafiya,maida numfashi yaringayi daya ganta,bakomai yace mata ya rufo mata kofar,ya koma bangaren Yusrah yaje a tarar da ita abakin kofa,yaya lafiya mai yafaru,bai Ce mata komai ba yayi hanyar bandaki yaje ya dauro alwala,yazo ya tarar da ita atsaye a inda ya barta,ki koma baccinki bakomai ya hau kan sallaya ya Tayar da sallah, Yusrah takoma ta kwantar tana tinanin mai ya tsorata el Bahrain,aranar kwana yayi yana nafilfili tare da adduoi na kada Allah yabawa izzadeen ikon cin galaba akansu,haka ma tasleem tarunga adduar zamn lafiya atsakaninta da el Bahrain Yakuma kare ta Daga sharrin izzadeen.
[2/28, 6:41 AM] My Mom: πŸ‘„LπŸ…°LπŸ…°TπŸ…°πŸ™Š




*written by*
πŸ’…πŸ’… *sadnaf*πŸ’ž








Page 156


Washegari da sassafe el Bahrain ya tafi gidansu yaje yasamu alhaji,yace mishi yana so yabashi mukullin gidansa dake Jan bullo yana so tasleem takoma can da zama,inda alhajin mamakin maganar da el Bahrain yagaya mishi ya rufeshi,tambayarsa yayi dalili,yace haka kawai, yakeso tasleem takoma can da zama,ganin maganar babba ne dole sai hajiya tashiga zancen ne yasa yakira hajiyar el Bahrain yakora mata maganar da el Bahrain yazo da ita,daka tsalle tayi tace akan me zai raba musu gida,fada tasleem da Yusrah sukeyi dayake so ya raba musu gida, yace aa haka kawai yake so ya raba musu gida,anan suka Ce indai ba fada sukeyi ba basu ga dalilin dazai sa yace zai raba musu gida ba,suna cikin zancen aunty luba tazo dan tayi musu sallama zata tafi abuja,tazo ta tarar da zancen da el Bahrain yazo dashi, daka tsalle tayi ta dire tace bai isa yaraba musu gida ba akan me,zai raba musu gida,ga laulayin da Yusrah ke fama dashi inya raba musu gida waye zai cigaba da dawainiya da yusrahn sanan inya raba musu gida rashin adalci zai ringayi atsakaninsu,Abu kamar wasa fa yazame gaske,dan luba fada taringayi sosai,inda el Bahrain yace shi yake da iko da gidansa shi yaga dama yahadasu aguri daya,yanzu kuma shi yaga damar rabasu,ganin abun na Neman zama fada ne yasa alhaji ya tsawatar musu yace su tsaya su saurareshi,wayarsa yadauka ya kira izzadeen yace yazo yana san ganinsa yanzun nan,gaban el Bahrain ne yahau dukan uku uku,dan baisan mai yasa Alhaji ke kiran

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login