Showing 81001 words to 84000 words out of 124539 words
dakin tasleem yanufa dan ya tasheta tayi sallah dan duk da abinda tayi mishi,hakkinsa ne yatasheta tayi sallah,dan jiya dayasamu yayi en nafiloli yadan ji zuciyarsa tayi sanyi akan abunda tasleem tayi mishi,tura kofar yayi hade da sallama,akwance take ta kudundune,akasa tana bacci,kau da kansa yayi daga kallonta,"tasleem tasleem" tashi kiyi sallah,yace yajuya yabar dakin,kamar amafarki taji sunanta,mika tayi tace alhamdulillahi lazi ahayana ba,ada ma ama tana wa ilahi nushur,ta mike tana mamakin kiran sunanta da el Bahrain yayi dan tunda suke bai taba kiran sunanta ba jikinta ne yakara sanyi,ahaka tayi alwala tazo ta tada sallah tana adduar Allah yabasu zaman lafiya mai dorewa tsakanin ita da el Bahrain, el Bahrain na sauka dakib Yusrah yanufa ya tura kofar hadi da sallama,tana kwance akan gado tana rungume da pillow,tana baccinta cikn kwanciyar hankali ,karasawa yayi kan gadon ya kwanta agefenta,yana kallonta,hura mata iska yayi a fuskarta,ta bude idanta ahankali,kamar amfarki taga el Bahrain agefenta,dasauri ta mike ta zauna tace yaya,naam swthrt, waro ido tayi tana mamakin sunan daya kirata dashi,ganin tana mamakin sunan daya kirata dashi ne yasa ya gyada mata kai you deserve it Yusrah, so don't be surprise,tashi kiyi sallah lokaci na tafiya,yace yana sauka Daga kan gadon,yabar dakin,bin bayanshi tayi da kallo har sai daya bar dakin,murmushi tasaki a filli Swt hrt tace tana girgiza kai,waw nafara samun matsayi gaba heart beat ma zai samin,to mai yakawo sudden changes din,kodan jiya nabarshi yayi yanda yake so Dani, shiyasa nasamu wanan mukamin,waw inko hakane,inya dawo dakina zan rufe ido in bashi hakkinsa watakila inzama heart beat,dinsa,tace ta mike tsaye tana murna,tab nidanayi tunanin inya auro tasleem bazai kara kallon inda nake ba,Ashe abun ba haka bane matsayi ma nasamu agurinsa,tab aunty tasleem bakida wayyo ahaka kamar mai wayyo,yanda naga yaya nadokinki kamar zai cinyeki agabana kika kwapsa masa,duk girmanki nan Ashe ke matsoraciya,aikuwa nidai ina karbi girki wlh zan daure dan nasan duk zafin dazanji ba zan mutu ba tace tana nufar bandaki,alwala tadauro,tazo ta tada sallah bayan ta iddar,taringa addua Allah yakuma karkato da hankalin el Bahrain gurinta,bayan ta Shafa mikewa tayi ta nufi kitchen, tafara kokarin hada musu breakfast,tana gab da gamawa,el Bahrain yashigo,dan har zai haura sama, yajiyo buruntun ta a kitchen,rungumota yayi ta baya,alokacin tana kwashe dankalin daya mata saura,lumshe ido tayi, yace swthrt da asusuban nan bakya bari gari ya waye inzo in tayaki yace mata da sanyin murya,aa wlh yaya nama gama kaga yanzu nahuta tunda nagama da wuri,kaga yanzu wanka ne ya ragemin sai inkoma baccina inyaso inkuka tashi sai nakawo mana,breakfast din muci lailai an gaisheki kinyi kokari,bari toh naje na kwanta inyi bacci dan jiya bawani ishasshen bacci nasamu ba,ya juyo da ita, yamata kiss, yacikata yayi waje, murna ne yabi ya ishi Yusrah tana mai godewa Allah daya karkato mata da hankalin mijinta,ahaka takarasa gama abunda takeyi tadauki kulolin takai dining,ta wuce bandaki dan tayi wanka.
El Bahrain kua na hawa sama apalo ya Tarar da tasleem azaune,tahada uban tagumi,sallama kawai yayi,yashige dakinsa bai jira tagama amsawa ba,tashi tayi tabi bayansa,ta tura kofar tashiga da sallama,amsawa yayi adai dai lokacin dayake cire doguwar rigar jikinsa,durkusawa tayi ta sunkuyar dakai,alokacin shikuma yazauna agefen gado yazuba mata ido,dagawo tayi da hawaye afuskarta,dan allah dan Annabi kamal kayi hakuri da abinda nayi maka nasan ban kyauta ba,murmushi, yayi yace karki damu tasleem dama nasan zaayi haka dan saurayinki yagamin,yace gangar jiknki na aura bkya sona shi kikeso,yacemin yamiki training din da inzan kusanceki sai kin tuna shi kin gujeni,kuma nayarda da zancensa tasleem bakya kaunata dan da kina kaunata bazaki min abinda kika min ba jiya,innalillahi wa inna ilahi rajiun,wlh Bahaka bane kamalπ,ina mutukar sanka,ina tsoron inka kusanceni ka tsaneni shiyasa nayi haka jiya,bangane in tsaneki ba tasleem yace atsawace,kinsan nasan komai akanki na yarda zan aureki,in zan tsaneki tun alokacin Dana gnki da izzadeen yakamata in tsaneki ban tsaneki ba sai yanzu,tasleem tashi kitafi dakinki,banasan raina yacigaba da baci magana zatayi yakuma daka mata tsawa kibarmin dakina nace, dagudu tabar dakin tana kuka,shikuma ya kwanta yarufe ido,soyayyar taslem tausayinta da sha,awarta na damunsa,ji yayi kamar yaje ya rarrasaheta,har ya mike,yatina abinda tayi mishi komawa yayi ya kwanta tare da Jan tsaki..
[2/20, 4:30 PM] My Mom: πLπ
°Lπ
°Tπ
°π
*written by*
π
π
*ssdnaf*π
Page 114
Da gudu tasleem takarasa dakinta ta fada kan gado ta rushe da uban kuka,tana salati,innalillahi wa inna ilahi rajiun,allahuma ajirni fi musibati wa aklifnin khairan minha,nashiga uku na lalace ni tasleem,yaushe zanji dadin rayuwata,yaushe zanji dadin da kowace mace keji,mai kaunata ma ya juya min baya,ya Allah ka dubeni da idan rahama ka ka jibanci al amurana,nasan nayi kuskure aruyuwata,nakuma yi nadamar abinda nayi,ya Allah ka yafemin,nasan abinda na aikata shi ke bibiyata,yanxu wanda nake tunanin ya yarda dani yana kaunata yajuyamin baya,Allah kai ka jarrabceni dan nasan kowane Bawa da irin jarrabtarsa Ya Allah zuciyata tayi rauni ka taimaka min in cinye wanan jarrabawar ka bani ikon hakuri da juriya,ranar Dana tare agidan mijina nafara fuskantar bakinciki amadadin farinciki ya Allah Kaine maji rokon bawansa,Ya Allah kai samiu dua ne ka amsamin adduata,tace tana fashewa da kuka mai cin rai,wayarta ne yafara ringing,tana Daga kwance takasa tashi haka yayi ta ringing bata Daga ba,el Bahrain kua da bacci yafara daukarsa,wayarsa dake side bed ne yafara ringing, yadauko wayar yaga Fatima ke kira,kin dagawa yayi,sai dayaga ta kuma kira sanan yadaga,sallama tayi mishi ya amsa,yaya kamal ina kwana lafiya lau,ya su Umma,suna nan kalau,ya gajiyar jiya,aikune da gajiya shiyasa ma nakira in gaisheku,inata kiran Aunty tasleem bata Daga ba,tana ina ne? Bacci takeyi,Allah Sarki auntyna gajiya Ce tasa takoma bacci,amma agida intayi sallar asuba,bata komawa bacci,inta tashi kace nakira in gaisheta dama missing dinta nake danaga hijabinta Dan jiya uwar haka muna tare da ita,fatima tace kamar zatayi kuka,zan gaya mata insha allahu inta farka zata kiraki,to yaya kamal nagode,yauwa ki gaida su Abba,ya kashe wayarsa, yana tunanin mai yahana tasleem Daga wayar fatima,ko sana,arta take ne kuka,tabe baki yayi ita tasani dan koma menene ita taja,yakoma yacigaba da baccinsa,tasleem kua sai datayi awa daya tana tana kuka,sanan ta mike tashiga bandaki,tayi wanka,ta fito ta zura doguwar Riga,tadauko magani ajakarta tasha dan kanta kamar yafado sabida ciwon dayake mata,bayan tasha maganin,Quraninta ta dauko,tafara karantawa ahankali taji zuciyarta namata sanyi,karfe goma dai dai Yusrah tahau sama ta tura kofar palon hadi da sallama,el Bahrain ya amsa, yana zaune yana kallon tashar sunna TV yana sanye da Jan Riga da bakin wando,zuba mata ido yayi har takaraso ta ajiye katon train din dake hanunta,sanye take da wata atamfa,brown da baki,anyi mishi dinkin doguwar Riga,dan Yusrah tana san dinkin doguwar Riga,takashe dauri,bawani makeup tayi ba amma tayi kyau,kusa dashi dataje ta tsuguna ta gaishehi amsawa yayi yana murmushi ya ruko hanunta,dasauri ta kalleshi,ta kalli kofar dakin tasleem,tafara kokarin kwace hanunta,dariya yayi dan yasan tsoro takeji kar tasleem ta fito taganta,cikata yayi tayi sauri ta mike,"yaya Aunty tasleem bata tashi bane?inaga bata tashi ba jeki duba kigani, ko ta tashi,dakin tasleem ta nufa,ta tura kofar hadi da sallama,amsawa tasleem tayi tana murmushi, ta rufe Qur'anin, Aunty tasleem ina kwana,tace tana dan rusunawa,lafiya lau Yusrah,ya gajiyar biki,bawani gajiya Aunty ai kece da gajiya,Aunty tasleem ga breakfast nakawo mana,toh Yusrah kin kyauta gani nan fitowa Bari nayi wanka,to Aunty afito lafiya,ta juya tabar dakin,tasleem jitayi Yusrah nakara burgeta,dan duk abinda sukayi jiya tana jinsu,anan takara ganin mutuncin yusrah,mikewa tayi ta shirya da wani material bki mai adon ja anyi mishi dinkin Riga da skirt,tayane Jan mayafi akanta wet lips kawai tasa batayi kwalliya ba tafesa turare,tafito dan alkawari tayi bazata taba bari Yusrah tasan suna fada da el Bahrain ba, fitowa tayi ta nufi palonta,anan taga Yusrah azaune akasa ta tankwashe kafarta,el Bahrain akan kujera yana zaune yana Jan Yusrah da hira,sallama tayi suka amsa gabadaya,suka juya suna kallonta,itama zama tayi akasa tana gaida el Bahrain amsawa yayi da murmushi afuskarsa,heart beat sai yanzu kika tashi,kallonsa tayi dasauri suka hada ido,tana mamkin sunan daya kirata dashi, sunkuyar dakanta tayi tace nadade da tashi,Matso to muyi breakfast,yace yana saukowa Daga kan kujera , yusrah bude kulollin ta zuba musu dankali da. Kwan aplate daya, tasa musu fork guda uku,ta zuba musu ferfesun rago, tahada musu tea,tace bismillahnku,kufara ci ko namuku dure, yace yana daukan fork,atare suka sa hannu suka fara ci,el bahrain yaringa satar kallon tasleem, haka kawai yaji tausayinta ya lullubeshi,idanta kawai yagani yasan taci kuka,ahaka suka kamalla breakfast Yusrah takwashe kulollin tayi waje,tasleem itama ta mike tayi hanyar dakinta,tasleem el Bahrain yakirata ta tsaya cak,Fatima takirani dazu tace ki kirata tana ta kiranki bakiyi picking ba nace mata bacci kike inkika tashi zaki kirata,to zan kirata insha Allah, tanufi Dakinta,bin bayanta yayi da kallo har tashige,lumshe ido yayi yanajin sha,awarta...
[2/20, 4:31 PM] My Mom: πLπ
°Lπ
°Tπ
°π
*written by*
π
π
*sadnaf*π
*assalamu alaikum fans dina ina kuma Baku hakuri akan post din dazaku ringa gani ba kamar da,ba,yanzu zan kokarta ko page daya ne irin ga posting ko biyu,dafatan zaku min uzuri* β€β€
Page 115
Tana shiga dakinta wayarta ta dauko,taga 5 misscall din Fatima, zama tayi agefen gado,takirata,bugu daya tadauka,"auntynaaa nayi missing dinki,Fatima tace da karfi,ke zaki kashe min dodon kunne,tasleem tace, yanzu auntyna dan Allah bakiyi missn dina ba,hmm nayi mana, ina su Abba,suna nan kalau,ina Yusrah, tana nan kalau,hope ba matsala, babu Fatima,dan Allah aunty idan da matsala karki boyemin bakida sama Dani banida sama dake,wlh sai nake ji ajikina kamar you are not happy,hawaye ne ya zubo mata,dataji me Fatima tace ta daure tayi magana,am fine and happy Fatima bazan boye miki ba,kawai ina missing din gida ne,are sure? Xan miki karya ne wai,toh shikenan auntyna,karki damu,zanzo nan da one week kisaki ranki kinji,murmushi tayi tagoge hawayen daya zubo mata tace toh shikenan sis,nagode ki gaida min su Umma inayi recharging zan kirasu,to shikenan auntyna miss you,miss you too,takashe wayar,ta kwanta tana tunanin halin datake ciki,
El Bahrain kua bayan ta shige daki tunani yafarayi,aduniya bashida burin daya wuce yaga ya mallaki tasleem arayuwarshi,dan shi kadai yasan san dayake mata, amma gashi ya mallaketa,adaren farkonsu sun fara fuskantar matsala,wayarsa yadauko yashiga gallery yaringa kallon hotunanta,I love you tasleem,y don't you love me,yace yana rungume wayar akirjinsa, wayarsa Ce tafara ringing ya duba yaga izzadeen ke kiranshi,bacin rai ne ya bayyana afuskarsa yayi rejecting din kiran dan yasan bakar magana zai gaya masa,cigaba yayi da kiransa,ganin in bai Daga ba,bahakura zaiyi ba yasa yadaga afusace,mallam lafiya kake kirana,haba abokina dan nakiraka sai yazama laifi,kiranka ba alheri bane agareni,haba kamal kiranka nayi fa ingaya ma, yakamata ka shigo muhadu sabida musan shirye shiryen dazamuyi dan kasan bnida amini sama dakai,lokaci bikina na matsowa shine zaka mun rashin mutunci,kai da bikinka haka na maka,am sorry kasn wani sain kanka ba dadi,yanzu sai kafadamin maganar dazan kasa bacci,kyalkyalewa yayi da dariya,hmm angon Yusrah da tasleem, kana jin dadinka fa ga er 16 ga er 20+,kaga abinda ke hadani dakai ko,wlh zan kashe wayata,sorry abokina dama so nke nace ma gobe za,azo ayiwa suhaima Jere,inaso kasa asharemin gidan a wanke, dan wlh bnida lokaci,ba Matsala Allah ya kaimu goben,amen,ya katse wayarsa,nadauka magana zai kuma kwaba min,yace ya mike yayi hanyar dakinsa,izzadeen kua tun lokacin da aka daura auren tasleem da el Bahrain, yafara kokarin yakiceta aransa,dan yasan tariga ta mishi nisa,abinda yasa komai ma yazo mishi dasauki,sabida shima nan da kwana biyar ya angwance,shiyasa bai damu ba,dan yna kyautata zaton suhaima sai tafi tasleem niima,gata er yarinya,da wanan tinanin yasa ya manta tasleem.
Suhaima kua tun ranar dasuka je bikin tasleem,suka dawo tafara tunanin maganganun da su fatima suka gaya mata,haka kawai taji bata yarda da izzadeen ba,tabbas akwai kamshin gaskia amaganar Fatima,idan kua dagaske ne,izzadeen mayaudari ne mazinaci,yahadu da dai dai shi bai sani ba, tunda abun yazo dahaka,gwara ma takira alhaji tanimu,tace mishi suhadu,dan tana bukatar kudi,dama dan izzadeen tayi quiting,tinda yanzu abun yazo da kar tasan kar ne,tadaina wahalar da kanta tana cushe cushen iska da shaye shayen magunguna,aranar takira alhaji tanimu,tafada mishi gobe zata zo taganshi a guest house dinsa dan tana bukatar kudi,ta kashe wayar tafara lissafin abubuwan daxatayi da kudi.
*8 :30*pm
Tasleem na kwance adakinta,tana chattn da Fatima, Yusrah tashiga dakinta da sallama tace tazo su ci abinci,tace mata gatanan zua,yusrah ta juya tabar dakin,mikewa tayi ta nufi gaban mudubi takara Shafa hoda a fuskarta tashafa wet lips,sanye take da orange din skirt har kasa,da farar top mai ratsin orange ajiki,ta nufi palonta,anan ta tarar da Yusrah azaune ita kadai,zama tayi akasa itama tana kallon TV dake akunne,inda ake shirin dadin kowa atashar Arewa 24,yusrah matso da farantin dake ajiye atsakiyar Palo tayi tafara zuba musu abincin,tasleem aranta tana so ta tambayi el Bahrain amma bata so Yusrah tasan halin dasuke ciki, dan rabonta dashi tun da rana dasuka kuma haduwa suka ci abinci,dan adaki tayi ta zama,inda taringa jiyo motsinsa apalo,Aunty ki kira mana yaya yazo muci abinci Yusrah tace,gaban tasleem ne yafadi dan tana tsoron taje yakuma korota,amma dan bata san Yusrah tasan halin dasuke ciki yasa ta Mike tayi hanyar dakinsa,tura kofar tayi hadi da sallama,ya amsa, yana tsaye yana fesa turare dagani shima wanka yayi,yana sanye da kaya marasa nauyi,sunkuyar dakanta tayi,tace mishi yazo suci abinci,tunda tashigo ya zuba mata ido yna kallonta dan bakaramin kyau yaga ta mishi ba,taka wa yayi yaje har gabanta ya dago da fuskarta yace kinyi kyua,zuba mishi ido tayi itama hawaye na Neman zubo mata dan har ga Allah tana kaunar el Bahrain,girgiza mata kai yayi,karki sake hawayen nan su zubo tasleem,dan nace kinyi kyau shine zakimun kuka,bata Ce mishi komai ba illa ma sunkuyr dakai datayi,ruko hanunta yayi sukayi waje, Yusrah kua ganin tasleem tadan Dade yasa tafara jera tsaki,Daga takira yaya taje ta zauna sai abinci ya huce tukuna,tace azuciyarta,ganin sun fito ne yasa ta daidaita fuskarta tasaki murmushi, yaya har ka kwantar ne? No ba kwanciya nayi ba,wanka nayi ne,yace yana zama akasan carpet,matso musu da abincin tayi,sukayi bismillah suka fara ci,el Bahrain yana ci yasatar kallon tasleem,ahaka suka kamalla cin abinci Yusrah ta kwashi plate din tayi waje,tasleem mikewa tayi itama zata tafi dakinta ya ruko hanunta yace ta zauna suyi kallo,inyaso karfe 9:30 sai taje ta kwanta,komawa tayi tazauna,suka cigaba da kallon,inda shikuma Rabin hankalinsa na kanta,ga wani sha,awarta dayake,karfe Tara da minti goma yasauka kasa ya nufi dakin Yusrah Dan yamata sai da safe,tura kofar tare da sallama,ta amsa,tana zaune agefen gado da waya ahanunta tana Dane Dane,kusa da ita yaje yazauna,yakarbe wayar Daga hanunta yaga game takeyi dan Yusrah bata chattn tun agida abbanta yahanata,swthrt Ashe kin Iya temple,na Iya mana yaya,mika mata wayar yayi, dama zua nayi namiki sallama dan kwanciya zanyi kinsan gobe zanje office gwara na Kwanta da wuri,sabida ma tashi da wuri,toh yaya sai da safen,badai wata matsala ko,babu yaya,toh shikenan ya mike tareda mikar da ita,rungumeta yayi yamata kiss agoshi,yacikata,yace sai da safe tace Allah ya tashemu,yafita waje,kwanciya tayi ta lumshe idonta tana shakar kamshin tirarensa,sanshi na ratsata,
Yana zua palon tasleem yaga bata nan dakinta ya nufa,ya tura kofar hadi da sallama amsawa tayi gabanta na faduwa,dan batasan dawace yazo ba,zuba mata ido yayi nizanje inkwanta da matsala girgiza masa kai tayi yace toh shikenan sai da safe,yajuya zai fita,kamal tsayawa yayi batare da ya juyo ba,tasowa tayi taje gabansa ta tsuguna,ta rike kafarsa,dan Allah kayafemin insha Allahu bazan sake gudarka ba nayi kuskure,nasan abinda nayi ban kyauta ba,fushinka agareni bakaramin masifa bane,tace tana fashewa da kuka,dagota yayi dasauri ya rungumeta yahada bakinsa da nata yafara kissing dinta,romancing dinta yake sosai inda yayi kan gado da ita suke zube,hankalinsa yakai kololuwar tashi,tasleem da dama agwiwa take bata Masan lokacin datafara maida masa martani ba hakane ma yakara haukata el Bahrain yacire kayan jikinsa,yayi nassarar cire mata skirt da rigar dake jikinta,yakai hannu zai cire mata pant dinta ya tuna yanda ta hanashi jiya,gudun kar tarihi ya maimaita kansa yasa yadauke hanunsa dan Daga jiya zua yau yaji ajikinsa sabanin dasuka samu da tasleem,cigaba yayi da wasani da ita har sai daya samu biyan bukatarsa yasauka Daga kanta yakoma gefe yaringa sauke numfashi,tasleem kua jindatayi yafasa cire mata pant ne yasa hankalinta ya tashi,dan tana tunanin in bai kusanceta ba ya kwareta dan takai munzalin da bazata Iya hakura ba,har zatayi mai magana, amma kunya yahanata tayi mishi magana, yana sauka Daga kanta ta juya masa baya hawaye na zubo mata azuciyarta kuma tana tunanin meyesa bai kusanceta ba,Matsowa yayi ya rungumeta,ahaka bacci yadaukeshi,tasleem kua bacci bai yi gigin daukarta ba,kwana tayi tana tunanin halin datake ciki dan tafara cutuwa,idan haka zai ringa mata,amma taya zata mishi magana..
Kuyi maneji da wanan zanyi kokari inyi typing gobe ko 2 pages ne love you ollβ€
[2/20, 5:01 PM] My Mom: πLπ
°Lπ
°Tπ
°π
*written by*
π
π
*sadnaf*π
_nasaudakar da page dinan ga dumbin masoyana masu kaunata,masu yimin addua duk da basu sani ba suna min fatan alheri,ina mutukar kaunarku yanda kuke kaunata Allah ya hada mu a aljanatul fiddausi_β€β€
Page 116
Tunda ga lokacin haka yake mata zaiyi wasani da ita sosai har yasamu biyan bukatarsa bawai dan baya sha,awar ya kusanceta ba sai dai yana tsoron abinda zai biyo ba,inda kuma yakejin dadin wasa da ita,dan fatan jikin tasleem da kamshin jikinta bakaramin za shi nishadi yake ba,inda so da kaunarta ke kara linkuwa aransa,har bayaso ya rabu da jikinta in suna bacci,tasleem kua daurewa take tana nuna masa al kunyarta dan bakaramin cutuwa take,amatsayinta na wacce tasha gyara sosai tana bukatar yasadu da ita,amma gashi ya bullo mata da sabon salo sai dai