Showing 63001 words to 66000 words out of 124539 words
kua,ni ai na gida ne,koma na dakine ni kadai zanje, uhmm basa bamba,anyi Amarya sai rawar kai ake,kanka akeji,gobe nazo naci girkin amarya ko shima kar nazo,hmm kai kasani fa ni bari inje inyi wanka kana batamin lokaci,ya tashi yashiga bandaki,yabar Izz atsaye shima hanyar waje yayi, yaja motarsa yatafi,el Bahrain na fitowa Daga wanka, shiryawa yayi cikin green din shadda yakafa hula kana ganinsa kaga ango,gidansu yaje,dan alhajinsu nata kiransa,yana zua palon alhaji yaje yasamu alhaji da abban Yusrah ,sai hajiya da Auntyn Yusrah, durkusawa yayi ya gaishesu,alhaji ne yafara masa nasiha daya rike Yusrah da amana,Yakuma zama adali,kar yasake yayi rashin adalci inya auri tasleem, haka dai dukansu suka mishi nasiha,suka Ce ya tashi yatafi,godiya ya musu, ya tashi yayi waje, sai dayaje bangarensa,yadauki abubuwansa masu mahimmanci irinsu litattafan adduoinsa,yafito ya nufi mota yadau hanyar sabuwar gandu inda ake siyar da Kazan amare,ya siyo guda hudu yace a ware masa guda biyu,yabiya kudin,yanufi hanyar super market, dake kusa da gurin yasiyo manya many an yoghurt da lemona masu sanyin gaske,yasa abayan seat din motar yadau hanyar Jan bulo,kiran tasleem yayi awaya yace gashi nan zua,tasleem kua tace yabari gobe yazo, yace bai yarda ba yau zaizo, ya katse wayar, tashi tayi dasauri tayi kwalliya tasaka wani Riga da skirt black and pink bakaramin kyau tayi ba,bata fesa turare ba dan tunda Umma tafara mata gyaran jiki,tadaina fesa turare dan jikinta kamshi yake na musamman,kiranta yayi yace mata yakaraso,ta mike takara kallon kanta amudubi,ta gyara mayafinta ta fita gurinsa,yana zaune yana yana yiwa Yusrah TeX akan gashi nan zua tashigo,amsa sallamar data masa yayi, bai dago ba sai daya yi sending,yadago,tasleem kua zuba mishi ido tayi taga yanda yayi masifar kyau,take taji wani masifaffen sanshi da kishinsa yakamata, yana dagowa murmushi yasakar mata,ya zuba mata ido,yaji wani Santa na ratsa shi...
[2/20, 3:53 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 89
Ganin yanda ya tsura mata ido ne yasa ta sunkuyar dakai ta gaishe shi cikin sanyin murya,takowa yayi yazo ya zauna akasan carpet yana fuskantarta ya tallafa fuskarsa da hannu biyu yana kallonta,mayafinta taja ta rufe fuskarta,yau kuma rowar fuskarki zakimin heart beat,to bakaine kake ta kallona ba kamar baka sani ba,tace ashagwabe,murmushi yayi yana kallon kunshin hamunta,heart beat kinga yanda kikayi kyau kua,dan Allah gayamin sirrin,bawani kyau danayi zolayata kake,am serious,hmm duk kyauna ai ban kai aunty Yusrah ba,kyalkyalewa yayi da dariya wai aunty,hmm dan Allah ki bude fuskarki mana inganki sosai inji dadi,zame mayafin tayi Daga fuskarta ta sunkuyar dakai,murmushi yasakar mata dasuka hada ido,yabi tabon sallahnta da kallo,gaskia heart beat ina mutukar kaunarki arayuwata,wlh na matsu naga lokacin aurenmu yazo dan naga izzadeen yafara kawo min hari tunda yazo yau kuma kin fita,daura fuska tayi wlh da sunan dan makarantarmu yazo shiyasa na fita bantaba tunanin shi bane,nasani heartbeat ina tsoron izzadeen nasan halinshi kar yazo ya kwace min ke,Allah ya sauwake,ni tunda kace kana sona na cire shi Daga raina,haka nakeso and pls kicewa su fatima su fita daga harkarshi,dan naga kamar tafiki daukan zafi bata da hakuri, insha allahu zan mata magana, wai kana nufin har yanzu izzadeen bai san ni zaka Aura ba,baisani,meyesa bazaka fada masa ba,zan gaya masa ba yanzu ba sai lokaci yakusa,toh shikenan, yauwa kicewa Umma ran lahadi su Aunty luba zasu kawo lefe,dan inaganin jibi zasu dawo Daga Dubai, zan fadamata insha allahu,kazo muje in rakaka ka tafi kabar auntyna ita kadai tace tana mikewa,kice dai kin gaji da ganina bahaka bane wlh,kasan irin wanan ba dadi,abar sabuwar Amarya tayi ta jira,hmm to shikenan muje kirakani,waje suka fito suka karasa inda yayi parking, ya bude bayan motarsa yafito da kaza guda biyu nan da aka ware yahada da lemona da yoghurt ya mika mata,kin karba tayi ta tsaya tana kallonshi,dan jitayi zuciyarta namata zafi sabida kishi,karbi mana yace yana kara mika mata,mai wanan din? Ki karba mana kiga mene aciki,ai basai na karba ba nasan menene,bana bukata,Amarya tafini bukatarsa, dariya yayi dan yagano kishi takeyi,nasan da amaryar ai nasiyo miki,itama ganata nan Zan kai mata, indai ba kishi kike ba ki karba dan Allah, haba dai ba kishin danakeyi,au bakya sona shiyasa bakya kishina,nidai kabani kana Jana da hira ta karbi ledan hanunsa,ta juya tana tafiya,heartbeat ba sallama,ka gaida Amarya sai dasafe tace batare da ta juyo ba,tayi sauri tashige dan wani kuka ne yake neman kwace mata,girgiza kai yayi dan yasan kishi ke damunta,kuma hakan ya nunawa tana sanshi murmushi yayi yashige motarsa ya mata text mai dadi,yaja motarsa ya tafi,Yusrah kua gajiya tayi da jiransa bayan ta karanta text din daya mata,ta mike tashiga toilet dan Tayi alwala tayi sallah,dan su Nabeela sun dade da tafiya,tana idar da sallahr akan sallaya bacci yadauketa,el Bahrain nakarasowa dakansa yasauka ya bude gate din ya shigar da motarsa,yadauki ledojin Daga bayan motar,yanufi palon Yusrah,sallama yayi tare da lumshe ido sabida wani kamshin turaren wuta daya bugi hancinsa,ganin bakowa afalon kuma bai juyo hayaniya yasa,yasan bakowa agidan dasauri yayi hanyar dakin Yusrah dan wani tausayinta ne yakamashi dan bai taba tunanin ita kadai bace yadauka kawayenta zasu tayata zama,tura kofar yayi tare da sallama,hangota yayi akwance akan sallaya,ajiye ledar hanunsa yayi yakarasa gurinta,tsugunawa yayi agabanta yakura mata ido,baccinta take peacefully murmushi yayi yace sleeping beauty yashafo fuskarta,firgigit ta mike tazauna,yaya kadawo? gyada mata kai yayi yana murmushi, yi hakuri nabarki ke kadai am sorry,sunkuyar dakai tayi bakomai yaya,Amarya kinyi kyau,rufe fuskarta tayi alamar kunya,tashi muje kirakani dakina inyi sallah dan naga alama ke kinyi sallarki,ya mike tsaye yaya sai na wani raka ka,wai Dan karna barki ke kadai shiyasa amma tinda bakyasn kirakani yi zamanki inje inyi sallar indawo,aa muje yaya,tace tana mikewa,ta gyara mayafinta,ke mai haka,cire mayafin nan ki ajiye sai kace unguwa zakije,yaya dan Allah kabarni insa, aa ni banyarda ba Ciro min mayafinan ki mikomin ko nacire miki dakaina...
[2/20, 3:54 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 90
Rike mayafin tayi gam dan Allah yaya kabarmin mayafina,hannu yakai dan yacire mata mayafin dan yaga tana bata masa lokaci,fusgo mayafin yayi,tabi mayafin sai akan kirjinsa,saurin cika mishi mayafin tayi tana kokarin ja dabaya,ruko ta yayi ya cire mayafin,kirjinta ya bayyana,idansa ne yasauka akan kirjinta,yaji wani irin Abu ya ziyarceshi,itama hakan taji dan tunda take ba namijin daya taba rike mata hannu ballantana ya rungumeta,cikata yayi ya ruko hanunta,mu tafi,yaja hanunta suka bar dakin, bangarensa suka nufa,suka shiga dakinsa sukayi sallama,bandaki yashiga ita kuma tazauna akasan carpet, tahada kai da gwiwa, dan duk atakure take,ta lumshe ido tana shakar kamshin turaren el Bahrain,fitowa yayi daga bandakin,jekiyi alwala ina jiranki,yaya nayi sallah fa har shafaii da wutr nayi,nasani kije kiyi alwala ina jiranki bana san musu,mikewa tayi tanufi bandakin tana kare kirjinta,murmushi yayi yafita yaje yadauko mata hijabinta,ya ajiye akan gado,ya tayar da sallahr isha fitowa tayi taje tadauki hijabin daya ajiye mata tasa tazauna akasa tana jiran ya iddar,alama yamata ta zo,ta tsaya Daga bayansa,rakaa,biyu yayi asujadar karshe sai daya Dade bai dago ba,yana ta adduar zaman lafiya atsakaninsu da samun zuria dayyiba,yaroki Allah ya mallaka mishi tasleem yadago yakara addua yashafa itama Yusrah tashafa tana hamma dan bacci takeji sosai,kallonta yayi yunwa ko?aa bacci dai,banyarda ba jirani ina zua,yaya bari inje dakina wlh bacci nake ji,wani kallo ya watsa mata wai meyesa kike da gardama ne,kinga Daga yau inayi miki magana banaso kiringamin musu kinji ko,gyada masa kai tayi,ya fice Daga dakin,bayan minti uku yadawo dakin hanunsa rike da plate da leda,daya hanun kuma yariko sleeping dress,ajiye sleeping dress din yayi akan gado yadawo yazaune akasan carpet, ya juye kajin akan plate,yazuba yoghurt din atumbler cups din daya dauko akan fridge din dakinsa,matso muci,ba musu taje tazauna dan tunda yamata warning tayi alkawarin daina masa gardama,yanda tazo tazauna dasaurinta ne yasa yaji tausayinta,zo ki zauna anan in baki dakaina,yace yana nuna mata cinyarsa,kallonsa ta tsaya yi har zatayi magana ta tuna,ta mike ahankali taje kusa dashi ya ruko hanunta ya zaunar da ita akan cinyarsa yacire dankwalin kanta,kananan kitson da aka mata 2 step ya zubo,waw kitso nan yayi kyau, yace yana Shafa mata kai, bata Ce komai ba illa rawar da jikinta yake, kamshin turarenta dayake Shaka ne yasa yaji hankalinsa yafara tashi,ganin inba sauketa yayi ba,za asamu matsala yasa yasauketa,kodayke yi zamanki anan bari na baki,naga kamar tsorona kike,yadauko cinyar kaza yakai bakinta,budewa bakinta tayi ta yagi kazar ahankli tafara taunawa,ahaka yaringa bata har sai daya tabbatr da ta koshi, shima yaci kadan yakai sauran fridge, yadawo yadauki plates da cups din dasuka bata yakai kitchen,yadawo,tashi kishiga wanka,ga wanan rigar sai kisa kizoki kwanta yace yana mika mata sleeping dress din daya dauko mata,karba tayi gabanta nafaduwa ta nufi bandaki,tana shiga bandakin ta rufo kofar bandakin harda murza key,ta dafe kirjinta,nashiga uku ni Yusrah,Ya zaayi na Iya sa kayan nan agaban yaya,tace tana Daga rigar, farin sleeping dress ne Iya kacinsa cinya,wai ya zanyi yanzu,haka tayi ta mutsu mutsu,ta ajiye rigar ta tari ruwa dan tayi wanka, el Bahrain naganin tashiga bandaki yadauki wayarsa yadawo falo,ya kira wayar tasleem,tasleem kua tunda el Bahrain yatafi tashige daki tana kuka,Allahn daya taimaketa Fatima tana wajen Umma,tana nuna mata videon gidan Yusrah, haka kawai taji tana tausayin kanta,ga kishin daya dameta, dan tasan dole yau Yusrah da el Bahrain zasu mallaki juna,tasan Yusrah virgin Ce,el Bahrain zai kara Santa ya darajata,haka tayi ta kuka tana tsinewa izzadeen,ji tayi wayarta ringing,tashare tacigaba da kukanta,sai daya mata 5 misscall tadaga,heart beat kinfara bacci ne
[2/20, 3:54 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 91
Toshe bakinta tayi dan kukan daya taho mata,taji sansa nakuma ratsata,duk da yau aka kai masa Amarya,sai dayazo ya ganta,yakuma kirata awaya duk da ya je gida,tace azuciyarta,ban fara bacci ba kaina ke ciwo,assha so sorry heart beat kinsha magani,ee nasha,amma yanaji muryarki haka ko kuka kike,aa bakuka nake ba,kifadamin gaskia,dagaske nake,kinci abinci naci,ina amaryarka ne ka kirani baka tsoron taji haushi,hmm tayi bacci,bawani nan,kai mai yahanaka baccin? sabida banji muryarki ba,to yanzu ai kaji sai kaje ka kwanta, toh naji zakiyi mafarkina,hmm zanyi,yauwa heart beat shiyasa nake sanki wlh,jin karar bude kofar bandakin dakinsa ne yasa yace bari naje na kwanta love you,love you too,ya kashe wayar gabadaya ya mike yatafi daki,tasleem haka kawai ta tsinci kanta da farincikin el Bahrain yace mata Yusrah ta Dade bacci kenan ba abinda ya shiga tsakaninsu,rungume wayar tayi akirjinta take taji duk damuwar datake ciki ya ragu,ta kuma gamsu da irin san da el Bahrain yake mata,tana kuma adduar Allah yakawo lokacin aurensu,Yusrah da ta Dade da wanka tasa rigar baccin akwai body spray da dama a bandakin ta fefesa,tarasa yanda zata fito Daga bandakin,sai data Dade,Daga baya ta leka ta inda ake zura key,taga el Bahrain baya dakin ta fito da gudu tasa hijabinta ta kwanta akan kujerar dake dakin,jin el Bahrain ya turo kofar yashigo ne yasa ta rufe ido takara kundunduna murmushi yayi dayaga yanda ta kudundune gefe daya azuciyrsa kuma yana kaunar yanda take da kunya,bandaki yashiga dan yayi wanka,minti goma yadauka yana wanka,yafito ya shirya cikin farin gajeren wando da farar vest,yaje ya kuna A C,yanufi kujerar data kwanta "Yusrah" yakira sunanta,shiru tayi gabanta na faduwa,kara kiran sunanta yayi still tayi shiru,dagata sama yayi ya nufi kan gado da ita,ya zaunar da ita,yana kokarin cire mata hijabin ta rike gam,kinsan bana san gardama ko,yana fadar haka ta cika hijabin ahankali,ya cire hijabin,ta runtse idanta da karfi jikinta yafara rawa,bin koina na jikinta yafara yi da kallo,yadawo da idansa kan kirjinta,daya fi tafiya da imaninsa,ji yayi hankalinsa yafara tashi,kiran sunanta yayi can kasan makoshi,tare da ruko hanunta,bata amsa ba illa ma kara runtse idon datayi gabanta na cigaba da faduwa,Yusrah inaso ki Saki jikinki Dani, ba abinda zanyi miki kinji, am straight forward duk abinda yake cikin raina zan gaya miki,nasan bazaki Iya sakin jiki dani ba,zan baki time har zua lokacin dazaki saki jikinki dani,kuma inaso ki rage kunyan nan dakike,dan yanxu ni mijinki ne,amma dan nace zan baki time bashi yake nufin bazan karbi hakkina agurinki ba,so nake ki saki jikinki ki daina tsorona,duk da nasan zan cutu,amatsayina na Wanda yakai stage dinan bantaba sanin mace ba,kinsan dole inyi sha awa amma banaso ki cutu, shiyasa ina kuma La,akari da kankntarki,amma badan nace miki bazan kusanceki ba kiyi tunanin bazan ringa wasani dake ba,kinji mai nace ko,kace haka mana tinda dama baso na kake ba tasleem kk so,tace azuciyarta,afili kuma kara sunkuyar dakai tayi,gadon ya hau,ya kwanta, yajanyota tafada jikinsa,yafara aika mata da sakoni jikinsa na rawa,dan bakaramin kai zuciyarsa yayi nesa ba,badan haka ba,ba abinda zai hana ya kusance ta,sai daya kwashi awa uku,yana wasa da ita,sanan ya cikata yanufi bandaki yasakrwa kansa ruwa Dan hka shine mafita agurinsa,Yana sakinta bacci yayi awon gaba da ita,ahaka yakara wani wankan, yafito yashirya yanufi kan gadon ya kwanta tare da rungumota bacci yayi awon gaba dashi,bangaren izzadeen kua ahanyarsa nakomawa gida bayan yabar wajen el Bahrain yahango wata tsalelliya atsaye abakin titi,hijabinta har kasa fara Ce tas,amma inbadan farin fata datake dashi ba kwandala bazaka siyeta ba,bazata wuce shekara 16 17 ba,tsayar da motarsa yayi agabanta yayi mata sallama ta amsa tana kau da kai,fitowa yayi Daga motar, ranki yadade,inbazaki damu ba,dan Allah kihau mota ta in kai ki,inda zakije,dagowa tayi ta harareshi,haka kawai bansanka ba,sai nahau motarka,taja tsaki tayi gaba ta tare adaidaita sahu tahau ta tafi,saurn hawa motarsa yayi yabi bayansu,ahaka har suka karaso unguwar sabuwar gandu,suka shiga wani lungu,yasauka Daga motar yabisu abaya sabida mota bazata Iya shiga cikin lungun ba,adai dai,wani kwarababen gida aka sauketa ta fito tabawa dan sahu kudinsa ta shige gidan,yana ganin gidan data shiga yaje yasamu wasu yara dake wasa a kofar gidan,ya tambayesu sunan yarinyar data shiga cikin gidan yanzu,suka Ce masa sunanta suhaima,ya nanata sunan nice name,yabawa yaran kyautar dari,yakoma wajen dayayi parking yaja motarsa yatafi gida yana tinanin yanzu ne yasamu matar aure, dan tana da nutsuwa bakamar Nabeela ba,dan Nabeela akwai rawar kai,da ita yace tahau yakaita gida jiki na rawa zata hau,amma suhaima sabida kamun kanta taki hawa motarsa..
[2/20, 3:54 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 92
Fatima kua tunda tashiga dakin Umma Take nunawa Umma video gidan yusrah,tana zuba,murmushi Umma ke tayi tana cigaba da hada turarukan da hadin gyaran jikin dazatayi wa tasleem,dan duk daddare take Shafa mata tabi ta mulke mata Zuma ajiki,sabida hadin yazauna afatarta,sosai musamman ta siyo zanuwan gado masu araha,tasleem take shimfidawa ta kwanta, in gari ya waye sai ta cire ta wanke,banda wani tsumi mai uban yawa data hada akatuwar jarka datake sawa tasleem tasha sau uku arana,Umma kinyi shiru sai murmushi kike,to mai zance miki,rabon Yusrah kenan addua zakiyi Allah yakawo kudi musiyawa tasleem kaya masu kyau,amma batun musiya mata Wanda yafi na Yusrah kyau,bai taso ba,kike abinki ma baffa( yayan abbansu tasleem) kasancewar suna da zumunci sosai kuma shine kusan mai kudin gaske afamilysu, yabada odan kayanta tuntuni amma naji abbanku yace kujeru set daya yabada odansa,sai gadaje biyu,tinda abun yazo dahaka Palo biyu ne dakuna uku,mu sai musiya mata wani set din kujerun,daya dakin kuma abarmin nizan hada,wani uban tsalle fatima ta daka waw mumyna shiyasa nake sanki wlh,dan nasan tunda baffa ne zai siya mata kayan nasan kayan zasu hadu,kinga yanda nakeso naga aunty tasleem tazama on top kua,hmm banda dai san zuciya,Allah Umma,yauwa Umma dan Allah in Abba yadawo kice mishi yabamu kudi,zamu fito da anko gobe zamuje kasuwa,aa inkun matsu Ku fito da anko kuje Ku shiga aljihun ango amma ni mijina bashida kudi,kai Umma kwanan nanfa yagama hidima,ke ni tashi kije kicewa tasleem tagama abban datakeyi,ina nan zua,abbanku nake jira yadawo in sallameshi,inzo in mulkamata wanan hadin danayi dan ni kadai nasan kudin Dana kashe,tana rufe Baki abbansu tasleem nashigowa dakin da sallama,sannu da zua sukayi mai fatima ta mike tabar dakin,ta nufi dakinsu tayi sallama, tasleem ta masa tana murmushi ,"aa any news wanan murmushi haka aunty,tace tana zama akusa da ita,idanta ne yasauka akan ledar dake ajiye akan side bed,aa wanan ledar fa,tabude sauri mhmmm aunty tasleem waye yakawo miki tace tana kai cinya baki,ango ne yakawomin,wasa kike, wlh dagaske,waw waw inason haka aunty, duk da ankai masa Amarya sai dayazo yaganki,yakuma kawo miki kazar amarci,kai Aunty this guy love you ooo,kinga tunyanzu zakisan yafi sanki akan Yusrah,to ai baki san wani Abu ba yanzunan yakirani,muna gama waya kika shigo,kai dan Allah shiyasa kike ta murmushi Ashe,Allah yabani mai kaunata haka aunty,inaso inga namiji na balain sona haka,Allah yabaki sis, ameen,aunty albishirinki,goro, Ashe baffa ya miki odan kayan daki,waro ido tayi ta damke hanunta dakarfi dan Allah da gaske,wlh, kai amma naji dadi wlh,nasan dole yazama mai kyau,dan latest kaya baffa kesawa ayi,ee wlh Aunty shiyasa dadi yabi ya isheni,Umma ma tace zata Hada bedroom daya,kai haka nakeso wlh,Aunty gobe fa zamuje kasuwa mu fitar da anko,kinga lokaci na matsowa,nifa ba event din dazanyi gaskia wlh nima Iya mother's night din da Umma zatayi ya wadatar,kanbu fatima tace tana ajiye ledar dake hanunta ta mike,yayar fatima designer guda zatayi aure ayi event daya,tab Allah yasauke,ai zamuyi sister's Eve insha allahu, kuma kasaitattun en mata zamu gayyata,high class babes,ba low class babes da Yusrah ta gayyata