Showing 102001 words to 105000 words out of 124539 words
tsoron Allah kayi adalci atsakanin matanka dan kasan dai Yusrah marainiyace bata da kowa sama damu,to Aunty luba tace miki nayi mata wani abun ne,aa batace min kayi komai ba fadama maka dai nayi dan naga kanka na rawa akan amaryar taka, goben kazo Ka dauketa,to shikenan Allah yakaimu goben, ya katse wayar wani irin haushin Yusrah da aunty luba ne ya rufeshi dan gani yake kamar akwai abinda Yusrah tafadawa aunty luba, sanan dan yace karta kwana shine tasa Aunty luba takira shi,tsaki yayi yace azuciyarsa gwara ma ta kwana dan dama banasan abinda zai rabani da heartbeat ko na minti daya ne,lafiya nocsol md kake tsaki,bakomai dear nida aunty luba ne wai Yusrah kwana zatayi gobe inje indauketa,yanzu kwana zatayi, ee haka tace, kinga ta hutasheni ba inda zanje, mutafi kitchen intayaki girki,yace yana mikar da ita, hanyar kitchen sukayi dan su Dora girkin dare
Izzadeen kua suna zua gida yafito Daga motarsa afusace yajanyo suhaima Daga motar yayi cikin gida da ita,apalo ya watsar da ita, yafara kokarin cire belt din wandansa,dagudu tayi hanyar dakinta,yabita da saurinsa,kafin ta rufe kofar ya shiga ya rufo kofar,bake er iska ba wlh mai kwatarki ahanuna yau sai Allah, dan Allah Kayi hakuri karka dakeni,da belt din hanunsa yafara dukanta,sosai tafara ihu,ganin yana dukanta baji ba gani yasa tadauki kofin data sha shayi dashi dasafe, ta kwada masa agoshinsa,sakin belt din hanunsa yayi,yadafe goshinsa dake zubar da jini,zubewa yayi akasa dan wani irin jiri ne yaringa kwasarsa,nashiga uku na lalace izzadeen tace tayi kansa dagudu,ganin idonsa na rufewa yasa tayi waje dagudu ta nufi gidansu el Bahrain.
[2/20, 6:12 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 140
Alokacin tasleem tagama girki kenan,el Bahrain na tayata wanke wanke,suka ji ana kwankwasa gate dakarfi,to waye haka yke buga gate haka ko ina mai gadi,el Bahrain yace yana dauraye hanunsa bari naje na duba,to shikenan bari nkarsa wankewa,saukowa yayi yanufi gate ya bude,ja da baya yayi dasauri dan suhaima nema take ta bangajeshi,subhanallahi ,suhaima lafiya kua naganki afirgice,nashiga uku el bahrain ka taimakeni izzadeen mutuwa zaiyi, mutuwa kuma suhaima ee dan allah kazo muje kafin jininsa ya kare tace tana kokarin kamo hanunsa,baya ykarayi dasauri kefa suhaima bakida hankali meyesa bakida nutsuwa ne,haba dan Allah nace ma abokinka na can jinin jikinsa zai Kare Ka tsaya kana min tambayoyi haba dan Allah tace tana fashewa dakuka,to yna ina? yana gida mana,eee nasani agidan a ina,kai nashiga uku adakina dan Allah muje kar ya mutu,wuce muje bari inkira tasleem muje dan bazan iya binki nikadai ba,yajuya yayi saman benen dasaurina,apalo ya tarar da tasleem tana sa turare wutan,tasleem yi sauri kidauko hijabinki ki rakani,ina zamuje? Kiyi sauri dan Allah yace yayi hanyar dakinsa ya canza kayan jikinsa yadauki mukullin motarsa yafito waje da gudu,atsaye ya Tarar da tasleem da dogon hijabi har kasa yace yauwa wuce muje,wai nocsol md mai yafaru ne wlh duk Ka Daga min hankali,bai kulata ba illa ma hanunta daya ja,suka sauka dasauri kicibis sukayi da suhaima dake kokarin hawo wa sama,ganin suna saukowa yasa tajuya tayi waje dasaurinta,aa kamal wanan ba matar izzadeen bace wai mai yake faruwa ne? Bai kulata ba har suka karasa kofar gidan fusge hanunta tayi da Iya karfinta mai yakawomu gidan izzadeen kamal,dan Allah wuce mutafi bana san shiga ne nikadai,izzadeen bashi da lafiya,suhaima data dade da shiga ciki dawowa tayi gurinsu dasaurita ta zube akasa ta Dora hannu aka,nashiga uku na lalace,izzadeen ya mutu,dagudu el Bahrain yayi cikin gidan yayi dakin suhaima kasancewar ginin gidansu iri daya bai sha wuyan ganewa ba,tasleem matsowa tayi ta dafa suhaima,wai mai yake faruwa mai yasamu izzadeen ne?cemata tayi dukanta yake batare da ta masa komai ba shine tsautsayi yasa ta kwada masa Kofi tafasa masa goshi,bata rufe bakinta ba,el Bahrain yafito da izzadeen akafada,yayi waje dasaurinsa,suhaima tabi bayansa,tasleem ma hka,kushiga muje alokacin daya kwantar da izzadeen abayan motar,suhaima bayan ta shiga dasaurinta ta Dora kansa akan cinyarta tana kuka,tasleem kuma tahau gaban motar,a360 yaja motar,in less than 5 minutes suka karasa asibitin getwell,el Bahrain yafito da izzadeen sukayi cikin asibitin,emergency suka kaishi dan su bashi taimakon gaggawa,dan goshinsa sai zubar da jini yake,bayan minti goma sha biyar da shigar likita yafito yasamu el Bahrain dake ta sintiri yace yasameshi a office, dasaurinsa yabi bayansa suhaima da tasleem dke zaune akan bencin suma suka mike,suhaima tabisu,tasleem takoma tazauna tana tabe baki,yanashiga office din likitan,likitan yazauna yajanyo wani farar takarda yayi rubuce rubuce,yamika wa el Bahrain takarda,siyo magungunan nan nakarin jini ne, dan yazubar da jini dayawa sundai yi mishi dinki sunyi mishi allura nan da hour daya zai tashi,el bahrain yace to shikenan, bari yasiyo magungunan,yafita dasaurinsa,abakin kofa ya tarar da suhaima atsaye,mai likita yace dan Allah, bai cemata komai ba,yawuce ta dasauri yayi hanyar waje,asanyaye takoma wajen tasleem tazauna tana hawaye,tasleem matsowa tayi ta dafata,kidaina kuka ba abinda zai sameshi,kinji ko,gyada mata kai tayi tana goge hawayen fuskarta,tashi muje muyi sallah naji anfara kiran sallahr magriba,kije kiyi sallarki inaje gida zanyi,tabe baki tasleem tayi, tayi waje dan tayi alwala tayi sallah
El Bahrain kua yana siyo magungunan sai daya tsaya yayi sallahr magriba,sanan yadawo asibitin,office din likitan yakoma ya nuna masa magungunan daya siyo,likitan yace zai Iya shiga yaga izzadeen an maidashi rest room,fitowa yayi yabawa suhaima ledar maganin yace su tashi suje suga izzadeen, suhaima dasaurinta ta mike,tasleem kua ta juyar dakai dan ko fuskar izzadeen batasan gani,dakin da aka kwantar da izzadeen el Bahrain da suhaima suka shiga,suka tarar yana bacci,kansa yasha bandeji,tausayin izzadeen ne yakama el bahrain dan har ya rame,suhaima kuma tafashe da kuka,juyawa yayi ya kalleta,wai mai yafasawa izzadeen goshi ne? Kasa bashi amsa tayi tacigaba da kukanta,toh tunda kin kasa magana Ki wuce muje in saukeku agida dan ba yanzu zai farka ba sai anjima,kije ki dafo masa wani abun,watakila ma yau zaa sallamemu,da gardama zatayiwa el Bahrain ganin ya tamke fuskarsa ne yasa tajuya tayi wje el Bahrain yabita abaya,tasleem yayiwa magana data tashi sutafi yakaisu gida,dasaurinta ta Mike dan dama zaman asibitin ya gundureta,cikin en mintina yakaisu gida,yace suhaima tashiga gidansa,suyi girkin tare zai dawo yadaukesu inkuma an sallamosu shikenan, suhaima tace to shikenan,har yayi reverse tasleem ta tsayar dashi,takarsa gurinsa ta sunkuya tariko hanunsa nocsol md dan Allah Ka kular min da kanka Ka kuma kwantar da hankalinka pls,murmushi yasakar mata yajanyo fuskarta yamata kiss akumatu,insha allahu everlasting one,tnx for your caring, duk halin da ake ciki zankiraki, to shikenan take care taja da baya yaja motarsa yatafi,sai data daina hango motarsa ta juya,suhaima kua zuba musu ido tayi tana ayyanawa dama ita da izzadeen ne ke soyewa haka,mushiga ko tasleem tace tana bude kofar gate din,tashige suhaima tabita abaya.
El Bahrain kua nakoma asibitin dakin da aka kwantar da izzadeen yakoma,ya zauna agefensa,yazuba mishi ido,minti goma da zamansa izzadeen yafara motsa hanunsa,ahankali ya bude idansa,innalillahi wa inna ilahi rajiun yace yana dafe kansa,dan jiyayi kamar kansa ba ajikinsa yke ba,sannu izzadeen kanka kema ciwo, sauke hanunsa yayi Daga kansa, ya Kalli el Bahrain hawaye na zubo mishi,kamal ina cikin wani hali tun ba,aje ko ina ba hakkin tasleem yakamani,bngane ba mai yafaru ne,kuka yafashe dashi sosai dakyar yayi shiru ya kwashe komai yafadawa el Bahrain,mikewa yayi yace innalillahi wa inna ilaihi rajiun,cikin shege fa kace,ba Iya wanan ba kamal tahadani da mahaifiyta wanan wane irin masifa ne,wlh nasan hakkin tasleem ke bina,narokeka kamin izni na nemi yafiyar tasleem dan wlh hakkinta ke bibiyata,ruko hanunsa el Bahrain yayi yace karka damu,zanyiwa tasleem magana ta yafe maka,yanzu wane mataki zaka dauka akan suhaima,cije lebe yayi,yace Umma tace sai na maidata dakinta bata kuma yafemin ba ina wulakantata,to ai ba aure atsakaninku,zaman haramci zakuyi,yanzu abinda zaayi hakuri zakayi har ta haihu,inyaso sai musan matakin dazamu dauka,Ka kwantar da hankalinka kafita harkarta kaji,aure nakeso nayi kamal ko akwai wacce zaka Iya hadani da ita dan Allah, karka damu zamuyi maganar in mun koma gida,bari naje nasamu Dr nagaya mishi Ka farka,yazo ya sallamemu,ya juya yayi waje.
[2/20, 6:14 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 141
Likita zua yayi ya duba izzadeen ya tabbatar babu wani matsala ya sallemeshi,suka dawo gida, sai daya raka izzadeen gida,yace masa yana zua,shiga da motarsa yayi cikin gida,yahau sama,apalo ya tarar da tasleem da suhaima azaune,suhaima tahada kai da gwiwa,tasleem na jingine ajikn kujera tana karanta 40 rabbana taci kwalliya da wani doguwar Riga English wear,tayi rolling din kanta da mayafi,palon sai kamshi yake,dagowa sukayi suka amsa sallamr da ya musu,suhaima ta mike dasauri,yajikin nasa, dasauki an ma sallamoshi yana gida,heartbeat ki hada min a abinci aflask inkai mishi,hope suhaima taci abinci,gyada masa kai tayi,yauwa wuce muje ki hadamin,hanyar kitchen tayi yabita abaya suna shiga yarungumeta,heartbeat kinyi balain kyau,murmushi tayi tace ngd,tafara zuba abincin aflask,tadauko basket tasa flasks din ta mika mishi yayi waje,suhaima kua tana ganin sun shiga kitchen tayi waje,tabe bakinsa yayi dayaga bai ganta apalo ba,aa suhaiman ta tafi ne,watakila ta tafi tunda baki ganta ba,bari nakai mishi abincin nan in dawo,to sai Ka dawo,yafita waje dasauri,yana zua apalo ya tarar da suhaima axaune akasa tayi tagumi,ina izzadeen din? Yana sama dan Allah Ka tayani bashi hakuri yana ganina yatashi yahau sama ya kullo kofar,bai kulata ba yayi upstairs, kwankwasa yayi, izzadeen yace waye,ni ne,bude kofar yayi,el Bahrain yashiga,ya ajiye basket din hanunsa,ga abinci nan zokaci kasha magungunanka,zanzo gobe muyi magana dan gida zan koma nagaji,ngd kamal Allah yabar zumunci,Ameen sai dasafe Allah yakaimu,yayi waje izzadeen ya kulle kofar dan bayasan suhaima tashigo masa daki,dan indai yana ganinta zai Iya jimata rauni,bude flasks din yayi yaga cous cous ne dayaji kayan hadin lambu,da miyan jajjage yaji naman rago,lumshe idonsa yayi yace I miss everything about you tasleem dan ko ba afada min ba nasan ke kikayi abincin nan,Ciro flask din yayi yadauko cokali yafara ci yana santi,dan rabonsa da abinci mai dadi irin wanan ya manta
Tasleem kua bayan fitar el Bahrain tanufi bandaki tahadawa el Bahrain ruwan wanka,tafito dauko trayn ta jera kayan abincin takai tsakiyar carpet ta ajiye tazauna akan kujera tadauki 40 rabbana dinta dan tacigaba da karantawa,Yusrah da tunda ta kwantar take juyi tana tunanin el Bahrain dan tunda hajiya Ummi ta dirdirka mata magunguna take jin wani irin feelings, ganin bai kirata ba har karfe 9 ne yasa ta dauki wayarta takirashi dan ko muryashi taji zata ji relief,wayar el Bahrain dake ajiye akan kujera ne yafara ringing, ta dauka taga Yusrah ke kira dan taga ansa deserved one,kin dagawa tayi dan bataso ta Daga Yusrah taji haushi, kiranta ne yakara ne yakara shigowa wayar, tasleem ta Daga tare da sallama,hararar wayar Yusrah tayi ta amsa sallamar, ina yaya ne,yadan fita amma yanzu zai dawo,to
Shikenan inya dawo kice mishi yakirani,tasleem nakokarin magana taji dif, ta kashe wayar bin wayar tayi da kallo tana mamakin Yusrah ko gaisawa ai ta tsaya suyi,el Bahrain ne yashigo da sallamarsa ta amsa tana ajiye wayar,everlasting one nadawo murmushi tyi tace sannu da zua,zama yayi agefenta,wlh ngaji muje ki hadamin ruwan wanka dan ina wanka sallah zanyi inci abinci in kwantar,nahada maka ruwan wanka tundazu,that's my Bby shiyasa nake kara sanki,yakai mata kiss lips dinta, Yusrah takiraka yanzu nace mata kafita inka dawo zaka kirata,tabe baki yayi yadauki wayarsa yakashe Dan haushinta yakeji tunda zata Iya bijire masa yace karta kwana ta kwana,bazaka kirata bane naga kashe wayar,ee sai gobe zan kirata,haba nocsol Md meyesa nafa cemata inka dawo zaka kirata,pls Ka kirata, mikewa yayi yanufi dakinsa dan yayi wanka,yabar tasleem azaune,wanka yayi yadaura alwala,yazo ya tayar da sallah,bayan ya idar da sallah,palon yadawo ya zauna,minti biyu da zamansa tasleem ta fito Daga dakin, itama da alama wanka tayi dan sleeping dress ne ajikinta doguwa pink colour mai tsantsi tayi parking din gashinta,sai kamshi take,zuba Mata ido yayi harta karaso,zama tayi akasa tadauki plate tafara zuba musu abincin,heartbeat yanaga kamar ranki abace mai yafaru ne,bakomai bismillah muci tace tana tura abincin gabansa rike hanunta yayi ya mikar da ita,yadorata akan cinyarsa,everlasting one namiki laifi ne,dan naga kin canza min, sunkuyar dakai tayi tace bakai bane nace Ka kira Yusrah kace min sai gobe tace ashagwabe,murmushi yyi yace shiyasa kike daura fuska,gyada mishi kai tayi,to karki damu in gama cin abinci zan kirata shikenan,gyada masa kai tayi tana murmushi, to muci abincin,ahaka suka kamalla cin abincin tana zaune akan cinyarsa, tashi tayi tadauki trayn din takai kitchen, tadawo ta sameshi atsaye,to Ka kira yusrahn,daukar wayarsa yayi ykira layin tasleem dan yasan wayarta akashe yake yasa handsfree,kinji wayarta akashe ko,zomuje mu kwantar, ya dauketa yayi, hanyar bedroom dinsa da ita,aranar kwana sukayi suna farantawa junansu rai inda el Bahrain yake fatan dama su dauwama ahaka,dan washegari ma bai samu zua massalaci ba,a gida yayi sallah.
[2/20, 6:15 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 142
Bayan yagama laziminsa kamar yanda ya saba, yace tasleem tazo su koma bacci,dan baccine a idansa,tasleem kua bata san yi mishi gardama dan so take tayi ayyukanta ta Dora breakfast kafin takoma bacci,dan tin tana gida tasaba,tashi tayi taje ta kwantar agefensa,ya rungumeta,cikn en mintina bacci yayi awon gaba dashi,sai data tabbatar da yayi nisa abacci,ta zame jikinta ahankali,ta tashi tayo waje,ayyukanta tayi kamar yanda tasaba,tayi musu breakfast,ta jera akan dining table,ta nufi bandaki tayi wanka,tafito tashirya cikin Riga da skirt en kati,ta feshe jikinta da turare,tafito tanufi dakin el bahrain tura kofar tayi ahankali dan karta tashe shi,kan gadon tahau ta kwantar kamar dazu ta Dora kanta akan kirjinsa,ahankali bacci yayi awon gaba da ita,sai wajen karfe 11 el Bahrain yafarka,tashi yayi ya ajiye kan tasleem akan pillow ya zuba mata ido,my sleeping beauty, wato sai datayi wanka tadawo ta kwantar,I love you everlasting one yamata kiss a lips dinta,ya mike yayi hnyar bandaki,wanka yayi, yafito yashirya cikin kananan kaya yafito Palo,ganin ko ina fes fes sai kamshi ke tashi yasa ya Saki murmushi azuciyarsa yana jinjina tsaftar tasleem, TV ya kunna yakamo tashar sunna TV yafara kallo,tasleem kua karan TV ne ya tasheta,ta Mike tare da salati,futowa tayi Palo,tazo ta rungume el Bahrain ta baya,shine baka tasheni ba Ka gudu kabarni,murmushi yayi yaruko hanunta ya zagoya da ita,ya zaunar da ita akan cinyarsa,banaso na tasheki ne sabida nasan bakidade da kwanciya ba tunda gashi naga alama kinsha aiki,harda min wayo kinyi bacci,Ashe jira kike bacci yadaukeni,kitashi murmushi tayi,Allah nasaba sai nayi ayyukuna,sanan nake komawa bacci bana san yi maka gardama ne,Allah Sarki heartbeat shiysa sanki ke ka ruwa araina Allah yamiki albarka,Ameen tace tana murmushi, bari nadauko mana break fast,ta mike taje tadauko abincin ta ajye akan carpet tayi serving dinsu,saukowa yayi ya zauna suna ci suna hira har suka kamalla cin abincin,takwashe plates din takai kitchen ta wanke tadawo,zama tayi agefensa tace nocsol md yakamata Ka dauko Yusrah yanzu,zan daukota sai anjima,haba nocsol md wane irin anjima dan Allah Ka daukota,yanzu 11: 40 fa,to shikenan naji zan daukota kya bari muyi hira dai ko kafin nadaukota kinsan fa yau Yusrah zata karbi girki,nasani ai karka damu inka dawo zan dawo bangarenku,muyi hirar,hmm nasanki fa tasleem ba zua zakiyi ba,dagaske nake zanzo,to shiknan,heartbeat kinsn mai,girgiza kai tayi,wlh Allah ba azzalumin Sarki bane,yanzu tun agidan duniya Allah ke hisabi,zakiyi mamakin ina gaya miki abinda ke faruwa agidan izzadeen, kwashe komai yayi yagaya mata,harda ciki tashigo gidan fa kace, ee wlh,Allah yakara saura cuta dazata samishi,haba tasleem bai kamata kice haka va ba a rama sharri da sharri,abinda yasa nagaya miki yanzu ma,ya rokeni da in nema mishi yafiyarki,dan yasan hakkinki ke bibiyarshi,inyafe mishi fa kace kamal,Ka manta abinda yayi min ne,badan Allah yadubeni da idan rahama ba,yabani kai amatsayin mijin ba,kamal da fa babu Wanda zai aureni ygani da mutunci fa,dan ko ayanzu ma ni kadai nasan bakincikin danake kunsa ina tuna,agaskia bazan Iya yafe mishi ba,tasleem inaso ki yafe mishi indai inada matsayi agurinki,am sorry kamal kana da matsayi mai girma awajena ammabazan Iya yafe mishi ba,tasleem kenan abinda nakeso kigane anan fa izzadeen yanada laifi kema kinada laifi tasleem kidaina dorawa izzadeen laifin gabadaya,dan da baki biyewa san zuciyarki ba dahakan bata faru ba,am sorry to say ban fadi hakan dan na bata miki rai ba,dan nasan arubuce yake tun fil azal hakan sai yafaru,amma kema kinada laifi tasleem dan izzadeen bai biyoki har gida ba,ke kika je da kafarki tasleem,wani irin kuka ne ya kwacewa tasleem,kiyi hakuri banfadi haka dan naci miki fuska ba,nafadi hakan ne dan kiyiwa kanki adalci ki yafewa izzadeen,dan yanada laifi,kinada laifi,hakane kamal tabbas laifina ma yafi yawa dan da banje gidansa ba da hakan bata faru ba,nayi Dana sani kamal dana biyewa san zuciyata ban kai zuciyata nesa ba,tace cikin sheshekar kuka,naji dadi dakika gane hakan tasleem dan ko ni bazan boye miki ba,wlh tun inada shekara goma sha takwas nake mafarki da mace,ina Daga cin maza mabukata kinga da zan biyewa San zuciyata da nima nafada halaka, amma dayake nakai zuciyata nesa kuma ina mugun kyamatar zina,sai Allah ya taimakeni naringa azumin litinin da alhamis,nasama wa kaina lafiya,dan haka inaso ki yafewa izzadeen dan duk kunada laifi kinji ko,gyada mishi Kai tayi,yauwa heartbeat now wipe away your tears and put a smile on your face, yace yana goge mata hawayen fuskarta,tashi muje kirakani waje,zan dauko Yusrah, mikewa tayi,inaso karakani side din Yusrah ingyara mata kafin tadawo,aa karki wahalar dakanki ki bari inta dawo tagyara,aa dan Allah kabarni ingyara mata,aa fa banyarda ba,magiya Tahau mishi dakyar ya yarda,yarakata bangaren Yusrah ta gyara mata koina har bangaren el Bahrain,ko ina. nagidan yahau kyalli tayi turaren wuta,tajanyo mata