Showing 51001 words to 54000 words out of 124539 words
ai sai da kudi,hajiya fita nakeso muyi fa zamuje unguwa naga kuma tana miki kitso,ai tama gama yimin kitson ina zakuje,Sosa kai yafara yi em em wajen tasleem zan kaita su gaisa,ah ka kyauta gwara su San juna tin yanzu,maza tashi yusrah kije ki shirya ki fito Ku tafi,tashi tayi tanufi dakin hajiya dan ta shirya,yauwa kamalu dazu muke zancen izzadeen da alhaji,gashi anfara shirye shiryen bikinka yakasa leko mu wane irin aiki ne yasha masa kai haka, gwara alhaji yace yana kiransa su gaisa kaga yakamata ya shigo kuyi tsare tsaren da zakuyi sabida harkar biki sai da taimako,hakane hajiya amma ai nafada miki ba abinda zanyi walima kawai zanyi da abokanai na kece
Ma naji kince zakiyi mothers night, duk dahaka Yakama ta yazo tunda bakada amini sama dashi, daukar wayarta tayi bari nakirashi naji wanne irin ayyuka ne suka sha masa kai haka, dazaayi bikin amininsa da bashida lokaci,kiran layin izz tayi tasa handsfree yana fara ringing hankalin el Bahrain ya tashi dan yasan indai yadaga hajiya tambayoyi zata ringa jera mishi kuma bai San zaiyi aure ba,izz kua tunda yabar gida,agidan wani abokinsa ya tsaya, jafar lokacin zai fita kasuwa shima ganin izz yazo yasa yabashi mukuli da zumar inya dawo sai ya raka izz gida,tunda yace masa baya jin dadi dan yayi wani zuru zuru,jafar na fita ya kulle gidan ya kwanta yana mai al ajabin abinda yafaru tsakaninsa dasut tasleem,yana kuma mamakin jarumtakar Fatima dan yasan yanda take azuciye da ita ce tasleem tsaf zata harbeshi,haka kawai kuma ya tsinci kansa da tunanin tasleem dan gaskia yau ta tafi da imaninsa shi sai yau ma ya tabbatar da mai kyau ce lumshe ido yayi daya tino yanda take murmushi,wai ya akayi mashida ma tazama kanwarsu,yace a filli gaskia zan nemi el Bahrain ya shiryamu da tasleem nakuma nuna masa na amince zan aureta dan gaskia yau Dana ganta ta tafi da imanina yace afili,jin wayarsa na ringing ne yasa yadauko Daga aljihunsa ganin mai kiransa ne yasa yasaki murmushi Allah sarki hajiya tajini shiru kwana biyu Daga wayar yayi tare da sallama
[2/20, 3:48 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 72
Amsa sallamar tayi,hajiya ina wuni,haba izzadeen ina ka shiga haka da baka ganuwa wane irin ayyuka ne suka sha maka kai dazai sa ka kasa zua kuyi tsare tsaren daya dace kuyi,tsare tsare kuma,ee mana ko iya walimar zakuyi ai ka dai samu lokaci kazo,tinda kai ka tsaya ruwan ido ka kasa tsayar da mata,bai gane inda zancen ta ya dosa ba,wayancewa yayi wlh hajiya ayyuka ne suka sha min kai amma yau zan shigo daddare insha Allah, allah ya yarda sai ka shigo din,toh hajiya ngd,ta katse wayar,el Bahrain kua tinda izz yadaga gabansa yafara dukan uku uku, dan yadauka izz zai gayawa hajiya baisan komai ba,yauwa kamalu kaga hakan da nayi ne zai sa ya ajiye ayyukan dayake yi yazo,hakane hajiya,wai shi bashida buduruwa ne kaga da anhada aurenku,tinda a unguwa daya kukayi gini,wlh hajiya bansani ba,yazakace min bakasani ba kai kua kasani tunda amininsa ne kai,zaiyi magana Yusrah tafito Daga dakin,duk juyawa sukayi suna kallonta, material tasa baki,mai adon stones ja,sai Jan rosek,data daura da Jan takalmi sabida kusan Rabin kayan da abbanta ya dinka mata tayi fitar biki suna gidan,hoda kawai tashafa da wetlips amma tayi kyau sosai dan el Bahrain shima kasa dauke idonsa yayi akanta,kanta asunkuye takaraso gurinsu,aa kinga Amaryar kamal sun sha anko da angonta,hajiya tace tana zolayarta,kai hajiya ta ina mukayi anko tasa baki da ja ni nasa baki da fari,kundai yi ankon kuma kunyi kyau,yakamata Ku tsaya agidan photo kuyi ko kala daya ne,murmushi sukayi dukansu,Yusrah mai zaki kaiwa kishiyartaki naganki da Leda,turare ne hajiya,ah kin kyauta wlh,kamalu ni yaushe zata zo ta gaisheni,tunda ka tasa yata agaba taje ta gaisheta,zata zo kafin biki insha Allah, Allah ya kawota lafiya,ameen hajiya bari muje lokaci na tafiya Daga nan zaka wuce da ita gida ko zaka dawo da ita, aa gida zan wuce da ita,to shikenan Yusrah ki gaida min da antynki, zata ji insha Allah,suka bar palon,kafin su karasa wajen dayayi parking wayarsa tafara ringing, yana dubawa yaga izz ke kiranshi,tsaki yayi ya maida wayar cikin aljihunsa,izz suna gama waya da hajiya,yafara tunanin badai aure el Bahrain zaiyi ba bai fada masa ba inbahaka ba wane tsare tsare hajiya take zancensa,inkua aure zaiyi bai fada masa ba lailai bakaramin fushi el Bahrain yake dashi ba,dan shi tun aranar da yazo sukayi kaca kaca washegari yafara nadama dan yasan koma menene bai kamata yayiwa el Bahrain haka ba,shine ya dauki waya dan yakira shi yaji wane tsare tsare hajiya ke magana bai Daga ba, haka yayita kira Daga karshe ma aka kashe wayar ajiye wayar yayi yaci alwashin zua gidansu el Bahrain daddare,el Bahrain akofar gidansu tasleem yayi parking ya juya ya kalli yusrah da tunda suka taho tayi shiru ko kwakwaran motsi takasa yi sai murza zoben hanunta takeyi,"yusrah" naam ta dago ta kalleshi,yana ganki kamar atsorace ko tsoron yayartaki kike ne,girgiza kai tayi,murmushi yayi karki damu tasleem batada matsala zata karbeki hannu biyu,bari nafara kiranta awaya, kunna wayarsa yayi,yakira tasleem,dagawa tayi tare da sallama ya amsa,"heartbeat" gamu awaje fa mun karaso, gaban Yusrah ne yafadi ta nanata sunan aranta heart beat,jitayi hawaye na Neman zubo mata,kk gatanan shigowa,Yusrah shiga ciki tundazu suke jiran isowarki,Yaya kafada mata wata tamin iso mana tunda bantaba zua ba,muje sai in nuna miki,ni adakin saukar baki zan zauna,fitowa sukayi Daga motar gabadaya,suka shiga cikin gidan,ga kofar dazata sada ki da palonsu can,yanuna mata,mikewa tayi tanufi ki
Kofar,shikuma yayi bangaren da suke zama,tinda suka gama girkin daxasu sauke Yusrah dashi,Fatima tasaka tasleem agaba da sai tayi kwalliya,Jan shadda tasa sai farin mayafi gyaran gashin da aka mata yana nan,bai warware ba shiyasa ta kashe dauri itama tayi balain kyau,el Bahrain na mata waya tasa Fatima ta tafi Palo tazauna,ita kuma ta zauna adaki,sallama Yusrah tayi abakin kofa Fatima ta dago ta amsa,dan wani novel take karantawa,shigo mana kika tsaya,shigowa tayi tasamu gu tazauna,Fatima still kallon bakin kofa take,ina Yusrah take naga bata shigo ba Fatima tace tana murmushi,murmushi Yusrah tayi tace nice yusrah ai,kan balain nan Fatima tace azuciyarta tsalli,au yihakuri wlh nadauka ko kanwar Yusrah ce,bari nakawo miki ruwa...
[2/20, 3:49 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 73
Ta mike tadauko lemon kwakwan dasuka hada da ruwa mai sanyi tasa afaranti,takawo gabanta ta ajiye sannu ko tace tana tsiyaya mata lemon acup,yauwa Anty bamu gaisa ba ina wuni,lafiya lau bafa nice Anty tasleem ba ni kanwarta ce bari nakirata ta mike tayi hanyar dakinsu,Yusrah kua tadauka Fatima Ce tasleem Ashe ba ita bace ahaka tana ganin Fatima tamata girma ya yayarta zata kasance,Fatima kua data tafi daki dan takira tasleem zancen zuci take,tab ai yusrah nan mai kyau ce ba abinda Anty zata gaya mata kash bahaka naso ba wlh naso Anty tafita kyau nesa bakusa ba tura kofar tayi tashiga Anty har ta iso fa nakai mata lemo da ruwa,taso wa tayi sis kinganta?ya take? Tafini kyau ko? Murmushi Fatima tayi aa ta isa tafiki kyau fari kawai tafiki,sai dogon wuya kamar marikin lema,amma Anty yarinya ce fa sosai wlh dan data shigo ban dauka ita bace,Allah ko,wlh,dama yace min bazata fi 16 17 ba,muje palon cewa nayi bari nakiraki,fitowa sukayi Daga dakin Fatima agaba,tasleem abaya,yanda ta tafi tabarta ahaka tazo tasemeta,aa Yusrah ya baki sha ruwan ba,Fatima tace tana zama akan kujera,tasleem kua tunda suka fito idanta nakan Yusrah data sunkuyar dakai,sai da Fatima tayi magana ta dago,gabanta ne yafadi datayi tozali da fuskar Yusrah dan bakaramin kyau ne da ita ba,gata er yarinya sbd akanta dai yarinya ce sosai,zama tayi akan kujera da Fatima ta zauna,Yusrah sanunki da zua tace tana murmushi,itama Yusrah sai da gabanta yafadi,dasuka hada ido da tasleem dan itama taga kyan tasleem sanan kuma taga ta girmeta nesa bakusa ba duk da karamin jiki ne da ita amma kana ganin kwayar idanta zakasan tana da shekaru,ina wuni Anty tace tana dan rusunawa alamar girmamawa,lafiya lau Yusrah yasu hajiya,suna nan kalau yauwa sannu,kisha lemon mana,tasleem tace,daukar lemon tayi hanunta nadan rawa ta kurba ta ajiye tana wasa da zoben hanunta,Fatima wayancewa tayi kamar novel take karantawa amma satar kallon Yusrah take,Fatima jeki dauko mata abincin nan ki Kai mata dakinmu naga alamar kunya takeji,mikewa Fatima tayi tanufi kitchen tadauko farantin dasuka jera abincin dasukayi aciki takai dakin,kizo muje kici abinci tasleem tace tana mikewa tsaya,Anty wlh akoshe nake,aa inkikayi haka bazanji dadi ba musamman nashiga kitchen nagirka miki,ko kyankyamina kike shiyasa bakyaso kici abincin,aa wlh Anty bahaka bane nakoshi ne,amma muje ko kadan ne naci,yauwa ko kefa,Fatima kuje ki zuba mata,bari naje mu gaisa da el Bahrain, hanyar dakin sukayi ita kuma ta fita waje jikinta duk yabi yayi sanyi dataga yusrah dan ganin datayiwa Yusrah dagani batasan komai ba virgin ce dole gata da kyau,ahaka ta karasa gurin el Bahrain, tayi masa sallama,ya amsa fuskarsa dauke da murmushi,heart beat shine kika shanyani ko,yace ashagwabance,ni na isa na shanyaka muna gaisa da yayata ne,dariya ya kyalkyale dashi,wai yayarki kanwarki dai,kundai gaisa ko,ee mun gaisa kyakyawa da ita masha Allah, hmm duk kyanta takai princess dita ne,zageni kai ma kasan tafini,nikuma ba macen danake ganin kyanta aduniya sama dake,tsarani,Allah ba tsaraki nake ba,hmm yasu hajiya,suna nan kalau tama San nan zamu zo,har tace ince miki yaushe zaki zo ki gaisheta,Allah sarki zanje in gaisheta kwanan nan insha Allah, yakamata kam dan ta matsu taganki yanda taga na isheta da labarinki,lailai kam,heart beat gaskia kinyi min kyau sai kace amarya,murmushi tayi ngd amma duk kyan danayi ban kai ka ba,aa ni ina naga wani kyau,bari inkoma gurin yayata,tinda mun gaisa,kizauna muyi hira mana,aa yanzu zan dawo,toh kifadawa Umma zan shigo ingaisheta,tom zan fada mata,ta fice Daga palon,dakin Umma tashiga tasameta azauna tana cire lallen hanunta,sallama tayi mata ta amsa,tasleem bakuwar taku ta iso ne,ee tundazu ma dayake sun fada mata komai game da el bahrain kawai boye mata sukayi abokin izz ne,dama el Bahrain ne dama yace ingaya miki yanaso yashigo ya gaisheki,toh jeki shigo dashi bari na wanke hanuna,fita tayi Daga dakin tafara shiga dakinsu dan taga Yusrah ko taci abincin,Yusrah nazaune akan carpet ga tulin kuloli agabanta,Wanda aka zuba mata,ma ko cokali uku batayi ba,Fatima nakan gado azaune tana chatnn da mashida tana munapinta mata kyan Yusrah,aa Yusrah ya bakya cin abincin,murmushi tayi Anty inaci fa,Anty tasleem tindazu nake fama da ita taci wlh sai juya cokali take inaga abincin ne bai mata dadi ba Fatima tace, wlh bahaka bane akoshe nake ne shiyasa, toh shikenan zan rama ai inazo gidanku,nima bazan ci komai ba,kifito Ku gaisa da Umma,dasauri Yusrah ta mike kamar kiris take jira tabi bayan tasleem, ki zauna kafin tafito Bari naje nashigo da el bahrain,tafita Daga palon....
[2/20, 3:50 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 74
wajen el Bahrain tokama tamai iso har palon, akasan carpet yazauna,dan Allah ka zauna akan kujera tasleem tace,aa kibarni anan am comfortable,tunda suka shigo Yusrah ta sunkuyar dakai,Umma Ce tafito Daga daki tana sanye da dogon hijabi har kasa tamusu sallama,suka amsa,Yusrah dasauri ta durkusa har kasa har suna hada baki wajen gaisheta itada el Bahrain,ta amsa tasamu guri tazauna adan nesa dasu,Ku zauna mana akan kujera dan Allah Umma tace aa wlh nan ma yayi,Ku saki jikinku ai mun zama daya,el Bahrain dai sai kara sunkuyar dakai yake sabida kunya,shiru sukayi dukansu,Umma na dan satar kallon yusrah azuciyarta tana yaba kyau da nutsuwarta,katse shirun tayi ta hanyar tambayarsu,yaushe ne bikin ne,tasleem tace min ankusa,ee ankusa saura sati biyu,Allah yasanya alheri yasa ayi damu,can kasa ya amsa da ameen,dagowa yayi dama alhaji yace infada muku asatinan zasu zo,ai nadauka sai angama bikin zasu zo,aa asatinan yace min zasu zo,to Allah yakawo su lafiya zan fadawa alhajin inya dawo insha allahu,tasleem na zaune acan gefe tunda Umma tashigo,tasleem kin kawo musu ruwa kua,nakawo musu gwara shi yasha ruwan,Yusrah ce dai bata sha ba har abincin damuka bata lokaci muka girka bata ci ba,kai bata kyauta ba kunyar wa zataji acikinku anriga anzama daya,Yusrah ki saki jikinki anriga anzama daya kinji,gyada mata kai tayi kanta akasa,bari nashiga ciki Ku gaida mutan gidan,Umma tace tana mikewa,zasu ji insha Allahu,Umma ta kalli tasleem zo in baki sako,tasleem tashi tayi tabi bayanta suka shiga dakinta,katuwar Leda tadauko ta bude turarruka ne aciki birjik,ta diba tasa awani dan jaka mai kyau sai doguwar Riga mai kyan gaske tahada da wanan turarukan ta mikawa tasleem ki kaiwa Yusrah kice mata gashi ba yawa,to Umma mun gode,takarba ta fice Daga dakin,tana fitowa Daga dakin Umma taga el Bahrain yakoma kan kujera ya zauna,Yusrah tana zaune dai a inda ta barta,kusa da Yusrah taje ta ajiye jakar,gashi inji Umma wai ba yawa,sunkuyar dakai takara yi alamar girmamawa tace nagode Allah yasaka da alheri,haba Yusrah mai abin godiya,kallon el Bahrain tayi dayake ta kallonsu,Ku tashi mutafi in rakaku naga magriba takawo kai,mikewa yayi wlh kamar kinsan Anty har tafara kirana wai muyi mu dawo,bari nakira Fatima Ku gaisa Daga nan sai mu rakaku,dakinsu tayi dan ta kira Fatima,el Bahrain ya kalli Yusrah data sunkuyar dakai taki dagowa tun da yashigo," yusrah" dagowa tayi ta kalleshi batare da ta amsa ba,miko min jakar in rike miki, dan naga alamar bakyaso ki dauka,kabarshi zan dauka,aa kawo dai yace yana kokarin daukar jakar,itama takai hannu zata dauka,hannuwansu haduwa yayi guri daya, Fatima taji wani shock, shima hakan yaji,saurin janye hanunta tayi, adai dai lokacin dasu tasleem suka fito Daga dakin, daukar jakar yayi ya rike,Fatima ta karaso wajensu ta gaishe da el Bahrain ya amsa,sukayi waje gabadaya,el Bahrain da tasleem agaba,Fatima da Yusrah abaya,ahaka suka karasa wajen dasukayi parking, sukayi musu sallama suka tafi,tasleem juya tayi ta kalli Fatima data bi motarsu da kallo,sis kinga kyaun Yusrah ko har kike cewa fari kawai tafini, murmushi Fatima tayi bata fa fiki wani kyau bafa ke kike ganin kyaunta,aikuwa wlh tafini kyau,gata da nutsuwa da kunya wlh, tasleem tace,aikuwa ba laifi tanada kunya ni wlh haka kawai take ban tausayi,dagani ba ruwanta,ai nadauka irin kanta zai ringa hayaki,in gyara mata zama,sai naga Ashe Saliha Ce,kai Anty yanzu sai ace itace uwargida ai tayi kankanta wlh, kamata yayi ace kece uwargida,ita Amarya gaskia ki cewa el Bahrain adaga nashi da ita, afara daurawa dake,inyaso Daga baya sai adaura nasu, aa sis ankusa bikinsu fa kike zancen ince afara daurawa dani,hakane kuma fa,amma dai bahaka naso ba,yauwa Anty bari muyi sallah mu zo muyi tunanin dressing din dazamuyi abikin
[2/20, 3:50 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*Sadnaf*š
Page 75
El Bahrain kua gida ya wuce da Yusrah,yayi parking akofar gidansu yasauko daga motar,itama Yusrah tasauko,tayi cikin gida,el Bahrain yakarasa gurin abban Yusrah dake alwala,tsugunawa yayi ya gaisheshi,ya amsa,kun dawo ee mundawo,yasu hajiyar? suna nan kalau sunce agaisheku,muna amsawa dazu munje da alhaji naje naga gidanka yayi kyau wlh kayi mutukar kokari,har angama fenti,ee tun satin daya wuce aka gama fenti,ai kua yayi kyau,yawa dazu muke maganar turawa gidansu yarinyar nan naje nasamu kawu nafada masa, zamuje ran asabar insha Allahu,sai ka fadawa yarinyar tafadawa mahaifinta,ai nafada musu sai dai na gaya musu ranar daza kuje,toh shikenan sai ka sanar dasu,bari in wuce masallaci,maza kayi alwala kar karasa jam'ii dan naga kamar ankusa tayar da sallah,ya tafi masallaci,el Bahrain yadauki butar yayi alwala shima yanufi masallacin,izz kua ana iddar da sallar magriba gidansa ya wuce yayi wanka ya shirya cikin kananan kaya yafito yanufi gidansu el Bahrain, el Bahrain kua ana idar da sallah yafito Daga masallaci,yakoma cikin mota yakira Yusrah awaya dan suyi sallama,kifito zan tafi,ya katse wayar, Yusrah da itama bata Dade da idar da sallahr ba hijabin datayi sallah dashi shine ajiknta ta fita gun el Bahrain,sallama tayi masa ya amsa,ta jingina ajikin motar,ni zan tafi gida kiranki nayi naji koda matsala,shiru tayi batayi magana ba, shirunki yana nufin ba matsala kenan ko,dagowa tayi suka hada ido tayi sauri ta dauke kanta,uhm dama alfarma daya nake nema agurinka,inajinki,dan Allah ka raba mana gida da Anty tasleem,kallonta ya tsaya yi yana mamakin maganar datayi, sabida me? Haka kawai yaya,aa komai da dalili Yusrah,meyesa kikeso araba muku gida ko kishi ne yasa bazaki Iya zama da ita gu daya ba? Aa wlh yaya haka kawai nakeso araba mana gida kaga tagirmeni nesa ba kusa ba shiyasa nakeso araba mana gida,hmm kawai dan ta girmeki sai nahau raba muku gida,ki ajiye batun raba. Gida agefe,gidan duplex ne kina kasa tana sama,ba ruwan kowa da kowa,nasan halinki nasan halinta baza asamu matsala ba,ki fada min inda wata matsalar bayaga wanan, babu yaya,kin Tabbata?,ee to shikenan ni bari na wuce gida sai munyi waya, toh yaya ka gaida gida,rufe kofar motar yayi ya tayar,ita kuma takoma cikin gida,minti goma sha biyar ne yakarasa dashi gida,yana parking,izz na parking,el Bahrain na kallonshi yayi kamar bai ganshi ba,yafito daga motar,yayi cikin gida,dagudu izz yasha gabansa,haba abokina kanaso kace baka gani bane,ko kallonsa el Bahrain bai yi ba yabi ta gefensa ya shiga cikin gida izzadeen yabi bayansa,bangarensa ya nufa,izz kuma yayi cikin gidan dan yagaisa da hajiya,afalo ya samesu azauna suna kallo sallama ya musu,suka amsa,izzadeen sai yau kasamu shigowa abbansu el Bahrain yace,eee wlh alhaji,ciki yakarasa ya tsuguna ya gaishesu,suka amsa,ai dazu ni nakirashi nace ana shirye shiryen bikin abokin nasa