Showing 99001 words to 102000 words out of 124539 words
dan Allah inbika Ka saukeni agida dan Allah ingaida hajiya,aa kibari gobe sai kije keda tasleem, yaya dan Allah yau nakeso kaga sai na kwana acan gobe kazo ka daukeni,wani irin kallo ya watsa mata saboda me zaki kwana,sunkuyar dakai tayi batace komai ba,tambayarki nake,yaya dama ina gudun yau ma inkasa bacci shiyasa tace cikin sanyin murya,hmm Yusrah kenan,ke kuma ta nan kika bullo,how long zanriga jigilar kai ki gida in ina bangaren tasleem,moreova yau nafara kwana adakin tasleem din da zaki cemin kin kasa bacci,idan ma Abu kika sa aranki yake hanaki bacci gwara tun wuri,kicire,inkin kasa bacci kitashi kiringa nafila ko ki dauko Qur'ani ki karanta,to yaya nafasa kwanan dan Allah Ka kaini ingaida hajiya,to ina kaiki gida abar tasleem ita kadai agida,yaya bafa dadewa zanyi ba dan Allah,hmm to shikenan tinda kin dage, jeki shirya,washe baki tayi tace yauwa yaya ngd,ficewa yayi yatafi bangaren tasleem, alokacin tasleem tana waya da Fateema,ganin waya take ne yasa yanufi dakinsa dan ya shirya,katse wayar tayi tabi bayansa,juyowa yayi ya kalleta har kin gama wayar ne,aa kashewa nayi,meyesa? Sabida nasan mijina na bukatar attention dina,murmushi yasaki daya bayana hakoransa,heartbeat wlh dabiunki nakara sawa inji kaunarki araina,Allah yabarmu tare,ameen nocsol MD fita zakayi ne? Ee wlh zamu fita da alhaji, Daga nan zan sauke Yusrah agida,lafiya zaka kaita gida,ee lafiya hajiya takeso taje ta gayyar,langabe kai tayi tace ashagwabe nima inje inshirya in binku in gaida hajiyar,nima fa hajiyata Ce,kamo hanunta yayi yace nsani heartbeat hajiyarki ce kema,kibari zan kaiki gobe,kinsan dalilin dayasa banaso kuje tare,girgiza kai tayi,yau kece da girki ina bukatar kulawarki,and zan dawo dawuri kafin indauko Yusrah,sabida mu soye,kingane ai yace yana Kane mata ido daya,sunkuyar dakai tayi tana murmushi, bari insauri inshirya inje in dawo everlasting one ya cikata yanufi wadrobe yadauko wani dakakkiyar shadda brown,yacire doguwar rigar jikinsa yasa kayan,tasleem kua dama tana ganin yafara cire riga ta sunkuyar dakai,heart beat,zoki zaba min hular daxansa,wajensa takarasa ta dauko mishi wani milk din hula kasancewar aikin jikin shaddar milk ne,ta sa masa hular,tnx everlasting one kinga yanda nayi kyau kua,yace yana kallon kansa amudubi,murmushi tayi tace kayi kyau sosai,juyowa yayi ya rungumeta heartbeat Bari inyi sauri inje in dawo ki tanadeni kafin nadawo,love and miss you,yakai mata kiss a lips dinta,yaruko hanunta muje kirakani,suna saukowa suka tarar da Yusrah atsaye ajikin mota taci kwalliya sosai da Jan shadda bakaramin kyau tayi ba,karasawa sukayi gurinta,el Bahrain yace Kai deserved one kinyi balain kyau hajiya kikayiwa kwalliya ko ni,murmushi tayi ta kalli tasleem, gaskia kinyi kyau Yusrah,nagode Aunty,shiga mutafi alhaji na jirana,el Bahrain yace yana shiga cikin motar,Ku gaidasu hajiya,zasu ji insha Allah sai mun dawo Yusrah tace,el Bahrain kiss yamata blowing yace miss you everlasting one, ta Daga mishi hannu,yaja motar suka fice,ciki takoma tanufi dakinta ta kwantar dan sai yanzu takejin bacci,minti biyu da kwanciyarta bacci yayi awon gaba da ita.
Bangaren izzadeen kua,yana amsa wayar Ummansa yajuya yanufi gidansu,hankali atashe dan yasan Kiran da ummansa ta mishi bana lafiya bane,en mintina ne suka kai shi gidansu,yayi parking yafito dasaurinsa ya shiga cikin gidan
[2/20, 6:08 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*Written by*
š
š
*sadnaf*š
137
Gabansa ne yafadi daya hango suhaima azaune,ummansa kuma sai girgiza kafa take tana jijiga kai,sallama yayi ya karasa gurin da ummanshi ke tsaye ya tsuguna,Umma Allah yasa lafiya naji kince inzo,wani mugun kallo taringa mishi,mai yasa Ka saki suhaima,shuru yayi baiyi magana ba yasunkuyar dakai gabansa na faduwa,suhaima kua ta kuma fashewa da kuka,ina tambayarka kamin shuru tace tana daka matsa tsawa,Umma ciki tazo min dashi gidana shiyasa na saketa,cikin wa tashigo ma dashi?Umma wlh nima bansani ba,izzadeen kabani kunya Ashe haka kake,ina maka kallon salihi,Ashe kai bai salihi bane,har Ka Iya samun Yar mutane Ka mata ciki,sanan dan bakada hankali Ka kuma saketa,Ashe kai watsatse ne bansani ba,karasa wacce zaka nema da fasikance sai matar da zaka aura,dagowa yyi dasauri ya kalli suhaima yana mamakin irin sharrin data kalla mishi,umma wallahi karya take min ko hanunta bn taba rikewa ba har na aureta,dan ubanka sharri zata maka tace kai kamata ciki Umma tace afusace,yarinya kintsatsiyya Ka. Lš
°Lš
°Tš
°. Mata rayuwa sanan dan rashn imani kazo kana cemin ko hanunta baka taba rikewa ba,izzadeen kabani kunya bantaba tunanin dan cikn Dana Haifa za aikata zina ba gshi harda cikin shege,izzadeen Ka cuceni duk tarbiyyar Dana baka da nasihar Danake ma daka guji aikata zina bakaji ba, yanzu kajanyo mana abun kunya azurriyarmu,kajanyo mana abun fada amaryar kwana uku da ciki,tace tana fashewa da kuka ina zan kai wanan abun kunyar ni Abu,izzadeen tunda Umma tafara magana yaji zuciyrsa kamr tafasa kirjinsa ta fito,shima hawaye ke zubo masa yafara magana azuciyrsa ni suhaima zatayiwa haka,duk matan Dana nema babu wacce nataba yiwa ciki,amma ni suhaima zata shigowa da cikin kato gida tace nawa ne,taxo ta hadani da mahaifiyata harta sa mahaifiyata zubar da hawaye akaina,girgiza kansa yayi wani hawayen bakin ciki nkara zubo masa atake ya tuna,maganar mahaifiyar tasleem inda take cewa izzadeen insha allahu yanda kasni zubar da hawaye sai mahaifiyarka ta zubar mka da hawaye,tun ba,aje koina ba hakkin tasleem yakamni na auri karuwa da cikin shege ga mahaifiyata ta zubar min da hawaye,dagowa yayi ya kalli suhaima,suhaima kiji tsoron Allah zaki mutu ki tadda Allah ni namiki cikin dake jikinki,banasan jin komai ummansa tace atsawace,abun kunya dai Ka ringa Ka janyo mana,mahaifinka da yana rayye da nasan bakincikin abinda kayi kawai zai Iya sa ya hadiyi zuciya dan babu Wanda yakai shi kyamatar zina,amma bbu komai izzadeen nagode da sakayyar daka mana,tashi Ka dauki matrka Ku barmin gida,kuje can kuyi rainon cikin shege,dagowa yayi cikin tashin hankali,Umma nasaketa fa saki biyu wlh ba cikina bane karya takemin,sabida bakada hankali Ka saketa bayan ka gama watsa mata rayuwa,maza mayar da auren Ku tashi kubar min gida,magana yakeso yayi tace yanzunan kafin in fusata inyi maka baki,Durkusawa yayi har kasa yace Umma dan Allah kiyi hakuri Allah yahuci zuciyarki,zan maidata dan Allah ki yafemin,tashi Ku bace min da gani,ke kuma suhaima ina miki kallon kintsatsiyya yarinya mai tarbiyya Ashe zaki Iya biye wa saurayi ya lalata miki rayuwa,gashi yanzu kema kinjanyo wa iyayenki abun fade,wlh bakuyi mana adalci ba,kai kuma sakamakon abinda kayi zan tattara kayana inkoma garko,dan bazan Iya jure wanan abun kunyar ba,kuma ban yafemaka ba indai Ka kuntatawa suhaima tunda duk halin data tsinci kanta aciki Kaine sila,tajuya tashige dakinta tarufo Kofarta,izzadeen daya sunkuyar dakai dagowa yayi yabi kofar da kallo yadawo da kallonsa Kan suhaima, suhaima sai Allah ya tsinemiki albarka tunda kika hadani da mahaifiyata,yajuya afusace yabar gidan suhaima tabishi abaya dasaurinta,yana kokarin tada motar tayi sauri tashiga motar, Jan motar yake da Iya gudunsa, innalilahi wa inna ilaihi rajiun Ka tsaya in sauka karka kasheni,wlh ko ban kasheki ba sai na miki mugun dukan da sai na barar da wanan cikn shegen yakaimata duka acikinta,tasaki ihu.
El Bahrain kua suna zua gida tare suka shiga cikin gidan apalo suka tarar da alhaji da hajiya azaune apalon zubewa sukayi akasa suka gaishesu,suka amsa cikin faraa,ina kuka baro amaryar naganku ku kadai hajiya tace,wlh tana gida sai gobe zan kawota insha Allahu,kaji jairi meyesa baka zo da su biyun ba dan kar ace mata biyu ne dakai, alhaji yace,murmushi el Bahrain yayi yace vahaka bane wlh,hmm mamana hope dai baya takura miki kuma bakya fuskantar Matsala Daga wajen abokiyar zamanki,ee Abba,yauwa haka nakeso,alhaji banda abunka kaga yanda yartawa tayi kiba takara haske kace ana takura ta,aa bani intambayeta kinsan fa yartawa akwai zurfin. Ciki tashi kishiga ciki luba ma tana ciki hajiya tace,Yusrah mikewa tayi ta nufi dakin,alhaji mun FASA fita ne,el Bahrain yace yana kallon alhaji,ee wlh yakirani yace in bari sai gobe, to shikenan ni bari in wuce office sai nadawo daukan Yusrah,to shikenan sai kadawo suka Ce,el Bahrain yayi waje yaje yaja motarsa yadau hanyar gida.
[2/20, 6:10 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
_na sadaukar da page dinan ga duk mai kaunar novel din Lš
°Lš
°Tš
° hakika inajin dadin yanda kukeson novel dina,ina mika gaisuwata gareku aysha mai littafi,action baby marubutan sai na auri izz funny_ šā¤ā¤
Page 138
Ahanya ya tsaya yayi musu take away yasiyi lemuna masu sanyi da fruits,cikin en mintina yakarasa gida awaje yayi parking din motar, yafito da ledojin Daga bayan mota yashiga cikin gidan,dakin tasleem yashiga yaje ya Tarar da ta rungume pillow tana bacci,cire takalmansa yayi ya ajiye ledojin hanunsa ya hau kan gadon,ahankali yazare pillown yayi replacing din pillow yakura mata ido,tasleem kua acikin bacci tafara shakar kamshin turarensa ta bude idanta ahankali,tasaukesu akansa,murmushi yasakar mata,kokarin tashi takeyi,yakara rungumeta,yi baccinki,aa yaushe kadawo,yanzunan nadawo,nazo na tasheki ko,aa yana ga Ka dawo da wuri kafasa Fita da alhajin ne? ee sai gobe zamu fita,eyya ya mutanan gidan, sunan kalau sunce agaisheki,ina amsawa, ki koma kiyi baccinki nima baccin zanyi,aa ai nadaina jin bacci kuma tashi zanyi indora mana girki,basai kin wahalar min da kanki ba nayo mana takeaway,haba nocsol md mai nayo mana takeaway,da kabarni na girka mana,wlh inbadan baccin daya daukeni ba da tuni nadora girkin,to yanzu dai na hutasheki kwantar muyi baccinmu,in mun tashi sai muci abinci,bari to muyi sallah tukuna naga lokaci sallah yayi,cikata yayi ta mike shima ya Mike yayi hanyar dakinsa,wanka tafara yi sanan ta daura alwala tafito,doguwar Riga ta zura tayi sallah,kafin ta shirya,tana idarwa ta cire doguwar rigar taje gabn mudubi tayi en shafe shafenta, kowane lungu da sako na jikinta sai data Shafa turare,hoda kawai tashafa sai wetlips,tanufi wardrobe dinta,tadauko wani farin top Mara nauyi mai gajern hannu tasa da wani Jan skirt Iya gwiwa,gaban mudubin takoma,ta taje gashinta tashafeshi da mayuka masu kamshi,batayi parking din gashin ba ahaka tabarshi,tajanyo drawern jikin mudubin ta dauko turaren da umma ta aiko mata dashi,ta shashafa ajikinta,ta mayar, coal ta kunna ta sa turaren wuta nan danan dakinta ya dau kamshi, tana kokarin fita waje el Bahrain yashigo,da alama wanka yayi shima dan jikinsa adan jike yake sakin baki yayi yana kallonta dan wani irin kyau yaga tamasa duk da ba kwalliya tayi ba,sunkuyar dakanta tayi dataga yanda ya zuba mata ido taringa murza zoben hanunta,karasawa yayi gurinta ya rungumeta everlasting one kinyi min kyau, dagota yayi yaringa Shafa gashin kanta,heartbeat inasan tabon sallah nan naki,dan bazan manta ba,shi yafara tafiya da imanina,yace yana taba goshinta,lumshe idonta tayi tana murmushi, kara rungumeta yyi yafara yakai hancinsa wuyanta yafara shakar kamshin turarenta,jiyayi hankalinsa yafara tashi,heartbeat dawane irin turare kike amfani ne? Yace cikin rawar murya dan yafara loosing control sosai,sakoni yafara aika mata cikin rawar jiki,ganin tsayuwa na Neman gagararsu yasa yajata yakaita kan gado,ahaka yacigaba da aika mata da sakoni,har yasamu ya biya bukatarsa,Yarungumeta sosai kamar zai maidata ciki,dan jiyayi kamar kara mata niima akayi dan bakaramin dadi yaji ba, heart beat inasnki,ina kaunarki,ina samun nutsuwa dake, everlasting one kifdamin abinda kikeso inyi miki shi,yace yana kara kankameta,hawayen farinciki ne suka zubo mata,tace ba abinda nakeso kamar so da kaunarka, dan Allah Ka rikeni da amana,heartbeat am all yours Allah yabani ikon farantamiki har karshen rayuwata,kissing dinta yafarayi awuya kamshin turarenta ne yakara tayar masa da hankali,aranar el Bahrain Abu daya yayi tayi dan the more yakara shakar kamshin jikinta d more yakara kashe arna,sai wajen 4: 30 na yamma yahakura ya kyalleta badan ya gaji ba,sai dan sallah dayake so suyi suci abinci,tare sukayi wanka,sukayi alwala suka fito sukayi sallah,tadauki takeaway din daya musu tayi hanyar kitchen dan tayi reheating din abincin dan yayi sanyi
Bangaren Yusrah kua tana shiga dakin taje ta tarar da Aunty luba yayar el Bahrain azaune da yarta hafsa adakin, zubewa tayi akasa ta gaisheta,aa Yusrah kece agidan namu ina kamal din, yana Palo wajen alhaji,zo nan ki zauna tace tana nuna mata gefen gado tashi tayi tazauna agefen gadon,ina tasleem din ko bada ita kuka zo ba? ee tana gida gobe zatazo,meyesa
Ba azo da ita ba yau? itace da girki yau shiyasa,dan itace da girki sai aki zua da ita, wanan ba hujja bace,icce dai Bakwa fuskantar Matsala da ita Dan naga ta girmeki takuma fiki wayewa,aunty bama fuskantar matsala da ita,yauwa haka nakeson ji,kamal din fa hope shima bakya fuskantar matsala Daga wajensa dan naga kansa na rawa akan abokiyar zamanki,bana fuskantar wani Matsala Daga wajensa,haka mukeson ji,dan shi zama na aure sai da hakuri,anan tafara gaya mata yanda ake zamantakewa na aure da yanda zata zauna da el Bahrain tazama mowa agurinsa,harta ta tambayeta ko tana shan kayan dazai kara mata niima,girgiza kai tayi,aunty luba tasaki sallati,Hafsa tashi kibamu waje
[2/20, 6:11 PM] My Mom: šLš
°Lš
°Tš
°š
*written by*
š
š
*sadnaf*š
Page 139
Yanzu Yusrah haka kike zaune bakya shan komai,sunkuyar dakanta tayi batayi magana ba,Yusrah kidaukeni tamkar yayarki karki sake kiji kunyata,bana shan komai aunty,auntynki yanzu bata babaki abubuwa ba lokacin aurenki? Tabani suna gida,au ajiyesu kikayi bakya amfani dashi ko bata gaya miki yanda zakiyi amfani dashi bane? Gyada mata kai tayi,tab Yusrah wake zama haka yanzu azamanin nan, ballantana ke mai kishiya,ina sai inda karfina ya Kare dan nasan abokiyar zamanki ma ita tana shan kayan Karin niima,dan awaye take,yaushe xaki karbi girki,gobe,to shikenan nasan mai zanyi bazaki koma gida ba yau,zankira kamal anjima ince mishi kwana zakiyi gobe yazo yadaukeki,washe baki tayi yauwa Aunty dama sonake in kwna,daukar wayarta tayi takira wata mai siyar da kayan mata da kuma gyaran jiki tace mata inta nan gasu nan zua,tace tanan sai sunzo,katse wayarta tayi,kitashi mu tafi unguwa,tace tana daukar Jakarta,mikewa Yusrah tyi sukayi waje,apalo suka Tarar da hajiya azaune ita kadai,hajiya ina Abba yafita ne,aa yana nan yashiga dakinsa ne,ina zakuje nganku da jaka,ina kamal din yatafi office ina tambayrki ina zakuje,hajiya yanzu fisabillahi haka abar Yusrah ba gyara, wane irin gyara kuma,haba hajiya kamr baki gane mai nake nufi ba,gyara dai mana,au nagane ai nadauka auntynta tana aika mata sakoni,hmm yaushe zata aika mata sakoni,ai kinsan ba ita ta haifeta ba,Yusrah datake da kishiya naka fa naka Yusrah batada sama damu Idan bamu gyarata banga Wanda ya dace ya gyarata ba,nasan ita abokiyar zaman tata va ahaka take zaune ba,dan haka zamuje wajen hajiya Ummi in hado mata abubuwa dan kwana ma zatayi,kwana kuma Lubabatu,ee hajiya ai ba itace da girki ba,gobe zata karbi girki zan kira kamal din anjima ince mishi kwana zatayi gobe yazo ya dauketa,to shikenan sai kun dawo,Yusrah tunda suka fara magana ta sunkuyr dakai,wuce mutafi luba tace tayi gaba Yusrah ta bita abaya, motarta suka hau suka dau hanyar court road, tafiyar minti goma sha biyar ne yakaisu,parking tayi akofar gidan suka fito,da sallama suka shiga gidan,suka tarar dawasu azaune akan tabarma anshafa musu dilka da alama gyaran jiki ake musu amsa sallamar aunty luba ta tambayesu
ko hajiyar tana ciki,suka amsa mata da tana ciki,palon gidan suka shiga da sallama hajiya Ummi ta amsa,tana zaune tana kwaba wani Abu da alama hadin gyarn jiki ne,gaisawa sukayi Yusrah ta tsuguna har kasa ta gaisheta,hjiya luba dama talakawa najinku,hmm haka ma zakice,Allah kua yaushe rabona dake ai na manta,ee gskia ne kinsan bamu Dade da dawowa daga Dubai ba shiyasa,Allah Sarki ya mutan gidan suna nan kalau,Hafsa Ce tagirma haka,murmushi tayi tace ba ita bace kinga muna kama ko,ee wlh kanwata Ce,hajiya luba dama kuna da kanwa mace,dariya tayi tace cousin dinmu Ce fa matar kamal,Allah Sarki ai bansani ba Ashe itace matar kamal din,ee itace zua ma nayi ki gyaramin ita,Allah Sarki kin kyauta,wane irin gyara kikeso amata,yanzu dai afara bata emergency hadi,dan tindayi aure haka take zaune,subhanallahi ya akayi hka,wlh kedai bari bansani ba sai yau,kuma fa tana da kishiya kai haba,wlh,aa dole abata emergency,dan Allah ki taimaka gobe itace da girki,insha allahu zan bata abubuwa,da zan samu ma har gyaran jiki ayi mata dan kinga wanan matan na waje duk matan aure ne kuma kishiyoyi duk sati biyu suke zua ayi musu gyaran jki,kut kishiyoyi fa kikace, kwarai kua, tab wlh bazan iya ba luba tace nidai ga Yusrah nan ki gyaramin ita dan nafisan tazama mowa agurin kamal,to shikenan ayimata gyaran jikin ee kiyi mata,zaki kashe kudi fa hajiya luba,dan abubuwa zan hada mata sosai,karki damu bkida Matsala indai kudi ne akwaisu dan so nake ma invaki isassun kudi duk karshen wata taringa zua kina gyarata in kudin ma suka kare kiyi min waya inturo miki koda bana nan,to shikenan hajiya luba zankua gyarata inzan samu ma ta kwana sabida hadi zan mata sosai,babu damuwa ta kwana, gobe dasafe zan zo indauketa,toh shikenan bari na fara dauko Kayan jikin,gyaran jiki tfarayiwa Yusrah, ta dauko maganin mata tayi ta Bawa Yusrah tana sha,kaji biyu tadafa da garin magani tabata tace tacinye tas kar ta tauna kashin,sai wajen Biyar luba tabar gidan,ahanyarta nakomawa gida takira el Bahrain awaya, alokacin suna zaune apalo yayi pillow da cinyar tasleem,suna kallo suna soyayya,jin wayarsa na ringing ne yasa yayi tsaki, waye wanan yke Neman ya katse min jin dadi,dauko min wayar in kashe,tasleem mikewa tayi tadauko masa wayar, alokacin har ya katse, ganin wacce takira ne yasa shi mikewa ba shiri kai Aunty luba ke kirana Ashe,kiranta ne yakara shigowa yayi sauri yadauka,ina ka ajiye wayarka ne inata kiranka baka dauka ba luba tace adan tsawace,bana kusa da wayar ne sai yanzu naji ringing din wayar,kana ina ne haka,ina gida yanzu nake shirin inzo indauki Yusrah, tsaki tayi ai dole ma Ka ki jin ringing din waya, tinda kana gida,em dama bugowa nayi infada maka Yusrah kwana zatayi gobe kazo kadauketa,kwana kuma aunty luba,ee kwana ko itace da girki,aa ba ita bace,to gobe kazo Ka dauketa kuma karinga jin