Showing 21001 words to 24000 words out of 98705 words
Bawan Allah nan yana kurb'a furza yana faɗin.
"Ina shayin da ake kawo min ba wannan ba."
"Toh wallahi ni ba zan yarda ba, haka kawai yarinya sai kace mayya kullum kaci a abincin ta sai ka yaba, har kasan banbancin abincin mu da nata ba zan yarda ba."
Murɗe hannun ta yayi cikin nutsuwa.
"Ke kin isa ki hanani tafiya da rayuwata yadda nake so ne? Duk wannan haukar da kike ban ma san yarinya ce ki babba ce take girkin na dan haka be careful wallahi" ya faɗa cikin bacin rai. Tare da sake hannunta, fita tayi daga dakin tana kafta mishi rashin mutunci, yana cikin haka Alhaji Ibrahim Amin Danrimi ya kira shi, ya gaya mishi an kai sadakin shi na gurin na tasha.
Haba jama'a masifa yake a daren har aka yi sahoor anan yake gaya musu shi zai je har fada ya gayawa Mai Martaba baya son magana.
Basu kuma shi ba, dan sun zuba mishi ido, suka shirin ganin ikon Allah. Itama Mabrooka bata fito ba, dan fushi take dashi.
......
Da gari ya waye nazo na fara aikina, cikin nutsuwa nake tafiya har na shiga masarautan. Suna zaune a inda suke zama da yan iskan abokan shi.
"Amma Prince Khamil wancan Yarinyar zata dace da kai duba da kyau akwai kayan abinci kuma irin su idan ka fara cin su bakaramin dadi zasu yi ba." D'ago kai yayi tare da zuba mata ido. Idanun shi ya sauka akan kirjinta wanda suke tsaye curr daga nesa kamar an hura baloon.
Shafa sajen shi yayi tare da cewa.
"Ka bari ranar sallah zamu gyara mata zama, kuma yadda take tafiya alamar bata yarda an cita ba, Ni zan fara cin abata. Na koya mata shan abata....
Warning. This article contains pornography and sex warnings for girls and widows ...
7/9/21, 8:04 PM - Buhainat: 1️⃣1️⃣
Haka kawai jikina ya bani ana kallona, dan haka ka kuma nutsuwa sosai ina tafiya. Tare da kara kame jikina har na isa damar su.
Cikin daga murya yace min.
"Ki gama kamewarki ni kuma zan fanshe dukar da wancan jahilin yayi min" cikin sauri na bar gurin sabida tsoron da ya dirko min, koda da na isa gidan. Gaida su nayi sannan na fara aikina, cikin nutsuwa sabida na bar Innah jikin yana son motsawa.
Sam na manta da batun wayar dake yau sinasir za ayi, wanke shinkafar nayi, tare da wanke yin miyar kub'ewa.
Ina gamawa na fito sallah, a falon ina idarwa, aka shiga hira. Kallona Aunty Mufeedah tayi tace min.
"Ina wayarki?"
Zaro idanu nayi na fara inda inda .
"Humm, ai na manta dashi"
"Toh kin sayi layine?" Nan ma na shiga ƙoƙarin musu karya.
"Ai na fa.."
"Yayan matsiyata basu saba rike babbar waya ba."
"Baki da hankali ne? Baki iya magana ce? Ko dan bakin san darajar dan Adam bane?" Ya fadi haka tare da saukowa daga step.
"Karamin hatsari aka samu wayar ya fadi, kuma nasan ya lalace domin."
"Ina ta san darajar shi?" A fusace ya juya kan Sawwama dan tun da ta fara maganar yayi mata magana ya dace tayi shiru. Sai da ya dauki remote ya wurga mata, ta gudu.
"Mai Kano ka kaita Mall ta zab'i wayar da take so"
"Kamar Ya? Zaka sayawa Yar aikin waya? Wallahi ba zata sab'u ba, bayan gama yabar girki ta bai isheka ba? Duk tulin kunyar da nake nuna maka bai maka ba, sai ka kure hakurina toh wallahi ba zaka saya mata waya ba. Shegiya mayya kin zo zaki dauke min hankalin mijina yar matsiyata talaka fakiri yar wanken wanke da shata"
Takowa yayi gabanta tare kallon Buhayyah wacce itama ta gama firgita da abinda Mabrooka tayi. Tare da cewa.
"Umma ce zata gaya min haka, ke da nake aure baki isa ba. Abdullahi ka dauki Yarinyar ka saya mata wayar da take so"
Daga haka ya fita bai kuma bin ta kanta ba, fada Mother tayi mata amma ta haura sama, dan haka nima cikin sauri da tsoron su na bar gidan Mai Kano yana min magana ina na kula shi.
..... Ina isa gida na sauke ajiyar zuciya, ina godewa Allah da ya kai ni gida, koda muka yi bude baki kwanciya nayi dan na gaji ainun. Ina barci naji kamar nayi fitsari ina dubawa naga ashe period na fara gashi yana matukar bani wahala, haka na duba magani na nasha. Tsabar tsoron kar ya kamani. Dan ina wahala.
Har gari ya waye, ciwon ciki nake tare da murkusussu.. dakyar na shirya ina ƙoƙarin b'oye ciwon. Na gayawa Umma zan tafi.
"Kiyi hakuri baki da lafiya"
"Umma bari naje"
Haka na tafi. Ina fama da zazzabin.
Ina shiga harabar gidan,
"Yawwa Beauty gashi can a falon ki dauka kiyi mishi godiya dan bai fita ba."
"Ok Nagode sosai" na fada tare wucewa a hankali ina rike cikina. Har na shiga cikin gidan.
"Yarinyar nan bata da lafiya"
Haka na shiga na sami su Natashah da Mahirah da Nishat sai Sawwama da Mabrooka. Gefen su Siyama ce tana fadanci.
Had'iye yawun nayi tare da cewa.
"Sannun ku" na wuce kitchen, muryan Mama ta fita ita da Mufeedah zasu tafsir ya sani fitowa muka gaisa. Da sauri ya dauko yana waya ranshi a b'ace ban sani ba a hankali na zubawa tafiyar shi irinta Sadaukan maza. Kwarjinin shi da kiran shi sun kuma bayyana kiran shi cikar halittar jikin shi kawai abin duba ne. Haka zuciyata take kisina min, dan haka na ce mishi.
"Nagode Yallabai.."
"Kiyi min shiru!" Ya daka min tsawa, bayan Mama na boya jikina yana rawa, sai masifa yake ta wayar tare da barin gidan.
"Kyale shi rigima yake ji tun jiya da dare,"
Gyada mata kai nayi, sannan suka fita. Rufe gidan Sawwama tayi wani irin murdawa cikinta yayi. Juyawa da zanyi muka yi ido hudu da su, tsoro ne ya kuma kamani na had'iye yawun tsoro.
"Kunga wayar, iphone 12pro. Yau zaki ci Ubanki da baki sanshi ba. Yar karuwa kawai."
"Indai akan wayar ce don Allah ku dauka kuyi hakuri ba zan kuma." Marina Natashah tayi tare da janyo hijab dina suka fito dani falon.
"Zanci Ubanki mutumin da zan aura kike shiga sabgar shi? Idan ma ɗan fuskar ki da yake kamar an zubawa rubebbiyar abinci miyar kuka sai munci uwarki" ta shiga marina tare da dukana, ba iya daya ba hatta Sawwama Mabrooka zungure min goshi take.
.haka suka dake ni.. tare da cire min hijab dina, rike hijab din nayi ina kuka.
"Don Allah duk abinda zaku min karku cutar da mutuncina"
"Sawwama dauko min dutsen guga na goge fuskarta Shegiya mu muni kamar bakar ƙaddara" inji Natashah..wani irin tsoro ya kuma kamani lokacin da suka jona iron din da wuta.
"Don Allah kuyi hakuri daga yau ka bar aikin ma, ba zan kuma dawo ba. Siyama ki gaya musu wallahi ba zan kuma dawowa ba."
"Kan Uba Shegiya a haka da hijab kin dauke hankalin mutane duba gashinta Aunty Mabrooka, dan Ubanki sai mun yanke shi damu kike magana, bamu almakashi"
Karar takalmin shi wanda ba haddace daga shekaranjiya zuwa yau, ya sani kallon step din, shine fuskar shi babu yabo babu fallasa kowa ganin shi ya sha jinin jikin shi. Murmushi yayi sannan ya dawo falon ya zauna yana kallon mu, tagumi ya zabga.
Ya jima yana kallon mu kafin ya cewa matar shi.
"Na zata idan na kawo wani abu me muhimmanci zaki iya tsare min shi ba tare da wulakantashi ba? Wannan Yarinyar Mahaifiyata ce ta dauke ta domin taimaka muku aiki kwandala na bana biyanta.
Ban san mahaifiyar ta ba, ban kuma ɗan daga inda take fitowa ba, abin da na sani girkinta ya ishe ni."
Takowa yayi tare da ɗaukar hula na ya mika min, sannan ya dauko hijab din, kallonta yayi da wutsiyar ido yana kallon yadda yadin material din ya kwanta a jikinta luff, kallon kirjinta yayi suna cike bam wani irin yanayi ya tsinci kansa da sauri ya mika mata hijab din. Sannan ya cigaba da cewa.
"Ke. Da ake bina na aure ki shine kike wannan haukar? Keda girkin ma kasa wucewa kika yi sai namiji irina zaki yi faɗa a kaina,".
Murmushi yayi sannan ya kalle Mahirah yace mata.
"Ke bana ce kar na kuma ganin ki ba? Nishat ke kina da hankali, ko daina biye musu..ke kuma Sawwama sai na fasa miki jiki duk abinda kike ina sane dashi yau Ni dake sai Allah, ke kuma kar naga kafarki a kasa. Muje ke"
A hankali na fita yana bin bayana, ban san inda xan nufa ba . Har ya wuce gurin motar shi, horn yayi min na juya gurin motar.
A hankali na shiga bude kofar baya, sauke glass din nayi yace min.
"Waye drivenki?" Gaban motar na koma, a hankali na shiga na zauna. Ina rufewa ya ja motar a guje muka bar gidan, suna kallon mu.
Tunda na shiga motar nayi shiru tare da lumshe idanuna nayi, tare da juyar da kaina. Kirjina na bugawa. Asibiti ya kai ni, aka bani magani da allura dan dama ina fama da ciwon ciki. Dan kin magana nayi a gaban shi sai da ya fita na gaya mishi ina ciwon ciki nake sai kuma bayanin da nayi mishi.
Murmushi yayi ya tare da rubuta min magani, ina fitowa ya shiga tare magana da likitan, yana fitowa ya kalle ni tare da tab'e baki.
Tafiya yayi ya barni a gurin motar shi, can sai gashi da wani mutum, ya mika mata sannan ya bude mata motar tare da kunna mata AC, sannan ya rufe motar. Har ya fita sai ya kuma dawowa ya buɗe.
"Karki sake ki tafi wani gurin, stay here a will be back Soon"
Gyada mishi kai nayi tare da lumshe idanuna, har ya tafi ina kwance a gurin, na fara Barci.
-::-
Kallon su Mama tayi Mufeedah da Aunty Nafy suka ce.
"Taya zai fita da yar mutane babu dalili?"
Cikin kuka Mabrooka tace.
"Ga shaida ya saya mata Iphone, sannan ya dauke ta a sabuwar motar da ko daukata Yar shi bayi ba, shine ya dauki yar aiki."
Ta faɗa tana kuka tare da kallon Mama. Kiran Amnah ce ya shigo mata, tana kuka take gaya mata. Irin abinda ya faru. Cikin fada da cin mutuncin tace mata.
"Ai muma a Tankara zamu yi sallah Insha Allah muna zuwa next week"
Shiru tayi tana ajiyar zuciya, kafin tatashi a falon ta barsu falon. Wasa wasa sai gashi har karfe biyu babu Asad babu Buhayyah.
.....
Bude kofar aka yi na farka ina kallon shi, sake lumshe idanuna nayi tare da gyara zaman na, dan na zata mafarki nake. A hankali ya zaro wayar shi, ya shiga abinda yake gaban shi.
Kura mata ido yayi sannan yana tuna yadda ya ganta d'azun. Lashe bakin shi yayi sannan ya yadda motar,
Dake yasan abinda yake damunta bai mata maganar sallah ba, har suka isa gidan yana mamakin yadda take barci kamar ta sami d'akinta. Tunda ya shiga cikin gidan ya tsaya bai fita ba kuma bai kashe motar Ba, karshe wayar shi na bude ya juya a hankali tare da ɗaukar Laptop din shi.
"Innah don Allah ki kai ni, gurin dangin mu." Ta faɗa a shagwaɓe.
Yarrr yaji yaji wani abu ya tsaya mishi a ranshi, ya kura mata ido, a hankali ya dauki Laptop din yana kallon ta. B'ata fuska tayi tare da tura baki. Kafin kuma ta razana tare da kare fuskarta, tana cewa.
"Toh ni ina ruwa na, ku dauke wayar Ni dai karku ta b'atani" ta faɗa tare da sake kuka. *Drama queen* ya faɗa a hankali yana kallon yadda take mafarki. Buga motar aka yi ta side din da take kwance.
A hankali ta bude idanunta tare da yin mika.
"La! Yallabai" na shiga zare ido. Zan fita.
"Common dauke min maganinki nan" ya wani b'ata rai kamar an mishi laifi. Dauka nayi tare da cewa.
"Nagode" na fita da sauri.
"Ina wuni?"
"Lafiya!"
Na wuce shiga cikin gidan nayi yabi Ni da ido, sannan ya shiga motar yana kallon yadda Aminin shi yake bin Yarinyar da tafito motar.
"Asad ya dai? A ina kasami wannan kayan?" Daure fuska yayi sannan yace mishi.
"Mind your mouth"
"Toh nayi shiru, amma d'azun Amnah ta kira ni fa akan matar ka da Yar aikin ta."
"Hmm!" Ya fada tare da Cigaba da aiki da wayar shi.
"Tace wai baka cin abincin ta sai na yarinyar baka yaba mata sai yarinyar"
"Hmm"
"Toh wai jiya kasayawa Yarinyar irin phone dinta, yanzun kuma ka dauki yarinyar a motar ka daka saya ko Yarka baka dauka ba"
"Next!"
"Shine ta kawo karanka!"
"Toh Alhaji Ahmed Amin, kawai saura ko na fita?"
"Karka mai dani sakarai mana"
Murmushi yayi sannan yace mishi.
"Sarautan da ya dace da kai kenan ai. Wato Mabrooka bata san matsayinta ba, shi yasa take kure Ni, ka gama ko har yanzun da saura?"
"Kaga Man ka tsaya muyi magana daya. Ka fita harkokin yarinyar." Ya fada mishi tare da kawo mishi wasu dalilai, takaici yasa Asad gyada kanshi zai fita a motar, Bashir ya rike shi.
Nan suka tsaya suka yi magana sosai, sannan yake gaya mishi wallahi bai tab'a kawowa ita take girkin ba, shi dai ya sani sau biyu kenan yana taimaka mata, so shi baya son damuwa duk abinda taga yayi mata tayi amma ba zata mishi ra'ayi ba, hakuri Bashir ya bashi.
A hankali suka fito tare da sallama, shi ya nufi gidan Bashir yayi tafiyar shi. Lokacin da ya shiga falon ya same mu a tsaye na kasa cewa kome sai kuka nake. Ba wai dan ina ganin arahar kukan bane sai dan yadda Mama take ta min faɗa, akan abinda aka gaya mata babu bincike....
Warning. This article contains pornography and sex warnings for girls and widows ...
7/9/21, 8:04 PM - Buhainat: 1️⃣2️⃣
Nad'e hannun rigar shi yayi tare da zama, yana kallon yadda take fada.
"Ke ko tausayin maraicin kiyi ba, taya zaki zo kina daukar abinda ba naki ba"
"Meye ta dauka?"
"Na dawo nake niman ta naji wai ta bika bayan ta shiga dakin Mabrooka ta dauki mata kudi shine suka mata fada kai...."
"Mommy! Karya suke yi.".ya faɗa yana kallon matar shi. Mai da kallon shi yayi kan Buhayyah da take kuka, yace.
"Hmm" juyawa nayi na kalle shi sannan na juya zuwa kitchen ban iya cewa kome ba, haka na gama aikin na Ni da Aunty Mufeedah.
Shigowa tayi zata bangaje shi na matsa mata, ashe ban tsira ba. Ta kai hannun zata dake ni Umma ta shiga tsakanin mu.
"Ince duk akan girki ake wannan masifar? Daga yau ke Mabrooka kiyi naki da mijinki, mu kuma Buhayyah ta mana, tunda ke baki da girma sai na jikinki"
Shi kenan na samu sauki, daga lokacin ta koma sama da girkinta mu muna yi a kasa, ga yaranta ina son su. Kodan yadda nake jin girman Ubansu a raina. Haka na boye abin sau dari idan zamu hadu bana kallon inda yaƙe. Kuma bana tab'a jin nayi wani motsin da zai gane ina kallon shi.
Tunda ta amshi girkin su,aka fara tsiya tsiya dashi baya ci sai na su Mama. Karshe har fada suka yi ya shure takalmin shi yayi tafiya abun shi.
Ana jibi sallah aka bamu kayan sallah a dinke, Ni kala hudu Siyama biyu, sai kuncen da Aunty Mufeedah ta bani wanda dayawan kayan ma bata tab'a sawa ba. Katon akwati haka ta bani.
Nayi ta mata godiya, sannan na bar gidan, bayan tafiya ta babbar Yayar su tazo. Ban san me ya faru ba. Amma washi gari ina shiga cikin gidan. Ta fara min rashin mutunci. Sai da Mama tayi mata fada bayan mun yi aiki har mun gaji a gidan na sha ruwa sabida mun yi snacks.
Haka na gama Moddibo da Mufeedah suka rako ni gida.
"Zaki zo kallon hawan Sallah ko"
"Wallahi ban tab'a zuwa ba, amma zan zo."
Haka muka yi sallama na wuce gidan.
Washi gari.
Muka tafi idi, bayan na dawo ban koma gidan ba. Sabida tun jiya na bar musu kome. Siyama ce ma ta koma da safe, bayan mun dawo idi ma ta koma,.ina zaune naji wayata tana kara. Bakuwar Number ce bani da number kowa sai ta Mufeedah da Siyama.
"Assalamun Alaikum!"
"Baki zo ba kin karb'a kudin aikinku ba, kizo maza ina jiranki"
"Toh Mama" na nace mata, kallon Innah nayi tare da gaya mata abinda zan je nayi, cikin sauri na shirya na tafi. Ina fita na sami napep, dake naga ana bikin sallah mayafi na saka a saman riga da zanin jikina.
A bakin kofar fada aka sauke ni na ciro kudin daga side bag na bashi sanan na shiga masarautan a hankali, take tafiya.
Matasa ne na hango a saman dawakai, ban lura da su ba ma, kawai yan iska suka yi kai na da dawakan nan. Baki daya na wani rud'e jikina har rawa yaƙe. Na rasa inda zan saka kai na, fisgo ni da akayi ya sani rintsa idanuna, wanda sun kai minti goma a rufe kafin na bude akan shi. Kallona yayi sannan ya mike tare da nufar cikin