Showing 9001 words to 12000 words out of 98705 words
dibo ruwa, na hadu da wani Almajirin da nake yawan aiken shi karban bokitin yayi yana faɗin.
"Aunty da kanki, kawo na dibo miki." Haka na bashi tare da cewa.
"Nagode!"
Na koma cikin gidan, ina zaune. Can sai gashi haka na amsa tare da shiga wanka, ina fitowa na shirya a nutse sannan na musu sallama bayan na taimakawa innah tayi boli, na koma da ita dakin ta kwanta. Karfe takwas yayi min ne a can, dan haka ina shiga wata mata me suna Madam Safiya yar garin Tirkulu ce, dan haka tana gani na tace min.
"Ke kiyi sauri ki shiga cikin kitchen kice su gyara akan lokaci Princess Natashah Abbas tare da Mahirah Musaddam Wazir, sai Nishat Badar Turaki, dan suma zasu zo koyan girki ne."
Gyada mata kai nayi tare da shiga cikin nayi musu Bayani, take jikin su ya fara rawa, suka shiga aiki har dani, ina cikin yi Madam Nafisah Shamaki ta shigo.
"Ke Buhayyah lokacin Class yayi ki tafi, kuma ku ajiye aikin ku tafi class, sabida an fara karatu."
"Ok Mah" muka fada tare da nufar hanyar da ta biyo, mace ce kamilah sanye take da kaya irin na alfarma, duk da tana gaban mu, haka ba zai hana ka gano kyanta da cikar halittar ta ba, har zamu shiga tace min.
"Buhayyah!" A hankali na tsaya a gefen ta nace.
"Yes Mah!"
"Idan kin gama kizo."
"Ok Mah"
Na fada tare da nufar aji.
***
Natashah Abbas
D'akinta kawai wata duniya ce me cin gashin kanshi, domin duk wani abu da zaka gani a cikin dakin dauke yake da siffar barbie, gashi tsarin dakin kamar na yara an shekara goma sha daya. A hankali ta ja bargonta me hoton Anna na cikin Froze ita da elsa. Sunyi kyau.
Yar karenta me suna Chu-chu ta lashe fuskarta, murmushi tayi cikin shagwaɓe tace.
"Chu-chu" ta kira sunan ta a yanga ce, murmushi tayi tana kallon karen da take lashe mata fuska. Tashi tayi bayan taji ana buga kofar ta.
"Amma wannan yarinya baki da mutunci yar iska. Kin manta abinda zamu je yi ne, Prince Asad zai zo da matar shi, shine zaki ajiye mu."
Wani irin yatsina face tayi kamar ta ga abin kyama tace.
"And so what" ta sauke kafarta a kasa, tare da kallon su lokacin da Nishat ta shigo, tana chat.
"Inji Sawwama wai a gaishe ku."
"Don Allah!"
Inji Princess Natashah.
"Gashi tunda na miki abinda na saba"
Amsar wayar tayi tare da ganin lokacin da Sawwama ta sauka a online. Wurga mata wayar tayi tare da cewa.
"Banza tun jiya ne ma"
Tsaki tayi tare da mik'ewa ta nufi ban daki, tunda ta shiga karfe tara na safe bata fito ba, sai sha daya na rana, sannan aka zauna makeup kamar wani masu zuwa gasar kyau. Suna gamawa ta saka riga da wando, kafin ta dauki wata top me shegen kyau ta saka.
A hankali ta saka heel shoe ɗinta dan dama ɗabi'ar su ce saka wannan takalmar, suka nufi waje bayan sun gama barna da turare, falon sama suka haɗu da Hajiya Balaraba, kallon su tayi cikin izza tare da cewa.
"Nishat naji ance Me Kano za abawa ke ko? Mahirah kuma Moddibo. Princess Natashah kuma Lion King!" Murmushi suka yi lokaci guda, sannan Uwar ta Cigaba da cewa.
"So ki amshi breakfast a kasa dan nasaka an gama miki. So ayi karatu me kyau."
"Ok Mum." Suna sauka suka nufi dinning table, a tsatsaye suka karya lokacin har karfe sha biyu yayi, dan haka suka nufi hanyar Shamaki catering services. A motar Mahirah, suna zaune a cikin motar tare da manna madubi a idanun su. Bayan su kuwa escort ne suke bin su. Wani irin dad'i suke ji.
Duk inda suka gifta sai anyi magana, har suka isa katafaren gurin girkin. A hankali aka bude musu motar, suka fito cikin jijjji da kai. Tare da mugun izza da takama, sai fadawa da suke bin bayan su, tare da wasu bayi mata suna rike da jakar su.
Sam ban san da mutane ba, dan haka ina zuwa na bangaje daya na cikin su. A zafaffe ta watsa min mari,. A kidime na d'ago kai na bakina yana rawa.
"Kiyi hakuri wallahi ban sani bane!" Na fada kuka na kwace min. Sabida naji mugun zafi. Huci take dayar ta rike ta.
"Mahirah amma ai ta baki hakuri"
"Please let me deal da ita bitch kawai, jaka jiki duk talauci zaki bangaje ni"
"Amma she apologizing"
"Please kiyi min shiru, I will deal with you, idan na kuma ganin shegen fuskar nan naki"
"Buhayyah" juyowa nayi ina kuka,
"Meke faruwa?"
"Mah ban sani bane na bangaje ta, shine.." na kasa fada.
"Mahirah Musaddam Wazir! Maybe kin manta da dokokin nan da aka tura muku ne ko? Toh zaki iya tafiya an dakatar."
"Please Aunty Nafy, don Allah kiyi hakuri babu dad'i a ce daga zuwa har mun fara fadawa matsala, kiyi hakuri Buhayyah" inji daya na gefen wacce tafi su kyau, amma bata yi magana ba, tana ta wasa da wayarta.
"Zaku iya shiga class dan an tashi na safe zasu tafi practical ne"
Ta faɗa tare da kallona cikin jin haushi tace.
"Ke kuma biyo ni" ta faɗa min. A sanyayye nabi bayanta, ina shiga cikin Office din tace min.
"How old Are You?"
"22 to 23" na fada mata. Dukar table din tayi cikin masifa tace.
"Nonsense mate dinki kikewa kuka? Me yasa baki rama ba!"
Wasu kwalla ne suka kuma tuttukowa, nace mata.
"Dakyar na sami aikin nan, sanan kuma nayi abinda zai wargaza min bukata ta, please zan kiyayye abinda na aikata amma ban iya fada ba, wallahi ban tab'a musayar yawu da kowa ba."
Na fada ina kuka, kasa yarda tayi ta tawo kamar zata mare ni, taga na maza na durkusa tare da kare kai na ina cewa.
"Am sorry ba zan kuma ba, don Allah kiyi hakuri ban iya fada bane wallahi kuma nice na ture su, i swear to God"
"Ok na yarda shiga cikin toilet ki wanke fuskarki, ki tafi kitchen ban da fada." Da sauri na shiga ina cewa.
"Toh." Ina shiga na wanke fuskana tare da fitowa, mika min dan karamin gidan Powder, shafawa nayi tare da mata sallama, abinda ta kirani ta bani na ta manta sai bayan na fita, ina shiga kitchen na hango su. Gaba na ne ya fadi, kamar na juya na bar kitchen ɗin haka na daure domin Allah ya zuba min mugun tsoron su.
Ina shiga na koma can baya na zauna,.ina kallon yadda ake koyarwan, duk da hankalina yana kan karatu, amma baki daya yadda suke harara na ya sani jin kamar na bar kitchen ɗin, tasowa Yarinyar tayi tare da isowa inda nake zaune, ta taka min kafa, kwalla ne suka diro daga cikin idanuna.
"Kiyi hakuri wallahi ba da gayya bane"
"Zaki min shiru, yar matsiyata ashe Mother in law ce ta turo ki ban, dan Ubanki sai kin gudu da kafarki." Ta faɗa tare da barin gurin, share kwalla nake amma dan zafi naji zafin, bayan an gama na fito ina dingishi, taka min takalmi suka yi ya tsinke, na fadi kasa. Cikin dauriya nace musu.
"Amma na baku hakuri ko? Toh meye nayi muku da bazaku hakura ba..."
Marin bakina tayi, tare da durkusawa tana faɗin.
" Idan na kalli yanayinki tsoro kike bani, domin wallahi sai na kashe wannan face dinki. Poor girl." Ta faɗa tare da zungure min goshina.
Had'iye yawu nayi. Tare da sunkuyar da kai na kasa.
"Jaka kawai!"
"Ya isa haka, bana son wancan matar tazo tagan mu. Karshe ta gayawa Surukar mu, don Allah muje Mahirah abu baya karewa a gurin"
Daukar littafin da nake rubuta kome tayi ta yaga shi into two pieces, sannan ta fita abinta, ina zaune a gurin kwalla yana zuba a idanuna akan littafin. Fitowa tayi ta hango ni, tsaki tayi tare da fita. Kome ta tuna ta kuma shigowa tana waya, tana faɗin.
"Toh ni ya zanyi da ita bata iya fada ba, kome aka mata sai kuka gata matsoraciya ce"
Mika min wayar tayi na amasa hawaye na zuba min.
"Buhayyah? Meye haka" kuka na saka mata sosai dan na gane muryan Maman Uwani ce, kuka nake sosai tare da kasa magana daga karshe nace mata.
"Na hakura da aikin"
"Akan me?"
"Tsoron su nake ji kuma ban iya fada ba," murmushi tayi sannan tace min.
"Ok toh kiyi hakuri, ki Cigaba da zuwa zan gayawa Hajiyar sai ta musu magana Kinji"
"Nagode Sosai Mama!"
Haka na mika mata wayar ta riko hannuna, na mike tare da barin gurin, sai da na tsaya na saya mana abinci sannan na isa gida, hada kafana nayi tare da wanka da ruwan zafi. Sai kallona Innah take tare da jin babu dadi musamman da ta ga alamun duka a jikina.
Dauke kanta tayi tana me jin kamar zuciyar ta zata fito, kwanciya nayi dan jikina da fiskana ciwo yake sabida marin da wannan Mahiran tayi min, barci ne me cike da wasu miyagun mafarki. Ina tana kallona. Shafa kaina take sabida kukan da nake Sosai.
"Toh bana baku hakuri ba, ku kyale Ni mana;"
D'aga bulalar hannun su, suka yi zasu dake ni ban san waye shi ba, dai naga ya kare ni, kifa kaina nayi da hannuna cikin tsoro. Sautin murmushin shi naji kawai yana yawo a kaina, a hankali na d'go ban iya ganin fuskar shi ba, sunkuyar da kai nayi. Zanyi magana naji kiran sallah Isha. Bude idanu nayi cikin zazzaɓi. Na tashi nayi sallah sannan na hada da shafa'i da wutiri kafin na kwanta, barci me nauyi ya dauke ni.
.... Washi gari ma ina tashi nayi kome na musu sallama, sannan na nufi bakin hanyar mota na jirana. Ina shiga na ce mishi.
"Ina kwana" sai lokacin na lura su biyu ne a cikin motar.
"Lafiya Buhayyah, ashe kuma jiya Abinda Ya faru kenan?"
Shiru nayi dan sai yanzun na tuna akwai wasu da zasu iya min Iskanci, gabana sai faduwa yaƙe, har muka isa makarantar, yau sunyi sammako. Tsoron da nake ji yasani kasa fitowa.
"Muje" inji daya mutumin.
"A'a kawai zan koma gida ne na fasa" na fada ina jin kamar zanyi kuka.
"Fito nace;"
Ya daka min tsawa, a tsora ce na fito ina jin kwalla na cika min idanuna.....
🙋 Hi....
Warning. This article contains pornography and sex warnings for girls and widows ...
+2347035133148 a tura evidence ta nan👈🏽
0472282105 Ramlat abdulrahman manga GT bank
7/9/21, 8:01 PM - Buhainat: *6*
بسم الله الر حمن الرحيم...
A hankali na fito daga cikin motar shima kuma ya fito, Mahirah ce dama a tsaye duk sauran suna cikin mota. A rikice ta shiga niman hanyar komawa cikin motar.
"Ke;"
Ya kirata wacce aka watsa mata ruwan sanyi jikinta ya fara rawa,
"Kar na kuma jin abinda kika aikata jiya"
"Toh" sannan ya nuna min hanyar cikin. Kafin ya juya ya mata kashedi sosai, yana barin gurin tace.
"Dan isa wallahi ko zaka kashe ni sai na dake ta, tunda ba gadon Ubanta nan."
Suna shiga suma aka fara class, ana gamawa na mike tare da nufar ban ɗakin. Sabida jikin alamar zuwan bakona, bude drowen toilet din, na dauki pad da na gyara jikina, ina cikin haka suna shigo min ban daki dai dai ina wanke hannuna. Gabana ne ya fadi. Ina kallon su.
Lashe bakina nayi tare da matsawa zan wuce, suka hango ni tare da rufe ban dakin kai na suka tura a cikin ruwan da suka tara.
"Dan Ubanki meye alakarki da Familyn Shamaki ne? Me yasa suka damu dake? Gaya mana ko naci Ubanki."
Fito da kaina suka yi tare da cewa.
"Zaki gaya mana ne ko sai mun dauke ki babu kaya"
"Wallahi babu kome, aiki zan musu shi yasa suka turo ni nan."
Gyada kai suka yi tare da tura min kai na cikin ruwan, na shaka har hancina, zuɓewa nayi a jikin abin kirjina ya bugu dashi, na suma. Sannan suka fita abun su.
Zuwa aka yi aka gayawa Aunty Nafy, sai gata tare da Masu kula da lafiyar gurin, fitar dani aka yi zuwa Office ɗinta, dakyar na farfaɗo, tana waya da wata alamar ranta yana b'ace ne.
Tari nayi tare da tashi zaune.
"Aunty Firdausi ta tashi!"
Mika min wayar tayi,
"Buhayyah!"
"Na'am" na amsa a hankali,
"Ya jikin naki?"
"Da sauki sosai."
"Ok zaki hakura da zuwa gurin kawai kinji, Insha Allah muma zamu zo Soon"
"Amma.....amma... Kawai xan iya babu kome, dan ina fahimtar abinda ake sosai."
"Toh yanzun baki ga yadda suka miki bane?"
"Babu kome zan iya." Na fada mata.
"Ok bawa Auntyn ki"
"Kinga Aunty Firdausi, Wallahi na rasa gane meke damun yaran nan, amma nasa a dakatar dasu."
"Haka ma yayi." Ta faɗa tare da yi mata sallama, mika min jaka Aunty nafy tayi tare da bani kudi tace.
"Inji Aunty Firdausi, so akwai hijabai dan naga kina son saka su."
"Nagode sosai, ki mata godiya."
Haka nayi ta zabga godiya har tace min ya isa,
"*"
A hankali nake kara fahimtar abinda nake zuwa yi, duk da an dakatar da Yan mata ukun nan bai hana su, su min Iskanci ba, har gidan mu suka bini tare da ɗaukar videon gidan bayan sun san bana gida, dan haka suka tashi da izgilanci suka watsa a grp din su na Tankara kingdom family grp.
Wannan shine gidan su Yarinyar da aka tura ta koyon aikin domin Mu da mazajen mu, gidan da talauci ya musu katutu.
Mufeedah dake yar zafin kai ce tana budewa tacewa.
"Ke yar gidan Uban waye a cikin tankara? A haka za a hada ki da Adam? Kinyi kuskure adam ba zai tab'a auren sakarya ba."
Shiru grp din yayi duk da da farko sun dauka wasa ne, sai Moddibo yazo yaga abinda suka yi har da hoton Innar Buhayyah yace.
"Am so surprised da abinda Mahirah kika yi na zata ke me iya kare mutuncin mutane ce?"
"Please Adam karka mai da karamin abu babban Abu, ita fa wasa tayi ba da gaske ba."
Dake sunan Moddibo kenan, kasancewar takwaran Sarkin Yola marigayi aka saka mishi dan a shekaran da ya rasu aka haife shi,.shi kuma Mai Kano sunan shi Abdullah, lokacin sarkin Kano ya tafi Ingila aka haife shi, kuma shi yayi mishi huduba, koda ya tambaya wani suna za a saka mishi Papa yace.
"Ranka ya dade sunanka ya dace dashi."
"Toh masha Allah an samu me kano."
Shine kowanne aka mishi lakabi da sunan yankin da ya ci, murmushi Sawwama tayi sannan tace.
"Toh ina hoton ta?". Shiru grp din yayi karshe ganin abun zai zama faɗa, aka rufe grp din. Mabrooka tana jin haka tace su bata hoton yarinyar da ake fada akan ta, tura mata hoton Buhayyah Nishat tayi tare da cewa.
"Mom Aroosh ina Durling yake turo min hoton shi." Wato Anis,.ita kan bata da rawan kai irin na Natashah Abbas da Mahirah Musaddam Wazir,
Murmushi tayi sannan ta tura mata, murna da sauri ta daura a Status tare da saka wasu manyan turancinta.
Zooming hoton Buhayyah tayi, tana kallon yarinyar, lokaci zuwa lokaci zuciyarta yana bugawa, dan kyau Yarinyar tayi kyau, amma bata san me yasa take jin bugun zuciyar ta akan Yarinyar ba. Goge hoton tayi baki daya.
Sai dai irin wayarta baya goge kome dukka dan zai dawo.
Fitowa yayi tare da mika mata hannu, a hankali ta mike tare da isa gurin shi.
"Good Morning Daddyn Aroosh"
Shafa bayanta yayi tare da d'ago kanta.
"Har yanzun kina son zama da cikin jikinki ne?"
Had'iye yawu tayi tare da kallon shi.
"Hmm, zan je a cire shi."
"Good Girl, ki kuma tabbatar kin saka wani abu, domin kula da lafiyar ki, bawai bana son haihuwa bane so ina duba halin rayuwa ne tarbiyyar su ma da kanshi yake zaune, karka haifi abinda ba zaka iya bashi tarbiyyar da ta dace."
Gyada mishi kai tayi.
"Kun hada kome naku ko? Dan nan da three wks zamu bar garin."
"Eh mun gama."
Shafa bayanta yake a hankali, har ta fara barci bai tashe ya ba, sai wayarta da ya gani yana haske, dauka yayi tare da bibiyar chatt din da akayi a grp din da suke na Tankara kingdom family grp, tab'e baki yayi , dan ya tsani renin hankali.
Rufe mata data yayi sannan ya kai ta d'akinta ya juya ya dawo dakin shi, leka dakin yaran shi yayi tare da musu addu'a, sannan ya juya ya fita kitchen ya shiga ya haɗa coffee ya fito falo, ya fara sha yana kallon labarai, yana gamawa ya tashi tare da nufar dakin shi..ya watsa ruwa ya kwanta.
----
"*"
A hankali muka cinye wata biyu, duk da haka kullum cikin tsoro da fargaba nake, domin wancan watan Mahirah tura ne tayi daga step, sai da naji ciwo a kafana, tsoron Allah da tsoron su ya hanani komawa. Sai da Aunty Nafy tazo min, bayan na warke na koma.
Alhamdulillahi yau muke practical din mu na karshe, daga shi sai kuma idan kin iya zasu dauke ki aiki idan kuma baki iya ba zasu sallame ki da kayan da zaki Cigaba da koya, a cikin wata biyu nan kuwa na samu alkhairi dayawa. Har yakai sai da na kai Innah asibiti aka bata magani. Kudin da suka rage na biya kudin makaranta na, na nutsu na gama bada abinda aka saka ni bayan mun yi girki tare da musu bayanin akan yadda ake sarrafa abincin. Murmushi Aunty Nafy tayi.
Bayan mun gama aka fitar da jadawalin mu da muka gama da sakamako mai kyau, aikuwa yan matan nan biyu suka fadi dakyar Nishat tasha, tare da tayani murna.
Da fushi suka bar gurin, bayan an gama suka dauke ni