Showing 33001 words to 36000 words out of 98705 words
Chapter 12 - ALIYU ASADULLAH Complete Book By Mrs Usman .txt
shi da Kanwar shi Me suna. Najwan, suna aiki da kula da mahaifiyar su.
Halwani mutum ne da bai iya boye abinda yake so ba, kuma ko zaka kashe shi baya boye abinda ranshi yake so. Dan haka yana ganin Buhayyah ya faɗa soyayyar ta.
A cikin satin suka tattara suka tawo Tankara, za ayi nadin sarautan Asad da kuma saka baikon shi da Natashah. Dan ma ana cewa ayi auren daga bayi ayi bikin tunda tana zata fara bautan kasa a Abuja.
Hidima ya sha kan kowa, Halwani kuwa ya makale min, tun Asad na dauke kai har ya kasa hakuri, yayi min fada.
"Dama kina son aure ne? Idan aka fara cewa zaki yi aure ranki b'aci zai yi tunda kinsan dole sai an nimo danginki" kallon shi nayi sannan nace mishi.
"Kayi hakuri, ban san yadda zan kore shi bane."
"Toh ki zauna har a gaya miki yadda zaki kore shi" ya faɗa min a masifance.
Ya juya ya barni cikin takaici, ban san meke damun shi ba. Amma tabbas akwai matsala.
..... Ranar nadin sarautan muka fito zamu tafi inda zasu yi hawan daba, muna hira sai ga Prince Khamil. Dira yayi a kan dokin shi ya iso gabana, tare da mika min hannun. Kunyar mutane da jama'ar gurin na maida hannuna baya.
"Common zo mana, na nunawa duniya kece matar da zan aura"
Isowar Halwani gurin ya ja hannuna muka bar gurin, bin bayan mu Khamil yayi. Tare da riko hannuna.
"Bafa inda zaka kai min abar kaunata" ya fisgo ni.
"Zan baka mamaki, sake min ita"
"Idan naki fa" Asad ba can yana kallon mu, na kasa magana dan takaici. Yan matan cikin masarautan da suke ƴaƴan dangin kamar su kashe ni.
"Ku sake ta" inji Asad, sake ni suka yi, sannan ya saka Ni a gaba, ya kai ni a har cikin gidan su, bai tsaya ba har cikin master room din shi.. ya bini da kallon banza, sannan ya rufe gidan ya fita ya barni a dakin, a hankali na shiga yawo a cikin dakin kome na dakin neat ne, ya burge ni. A hankali na shiga cikin wani daki wanda aka yi shi domin wanka kawai, cire kayana nayi tare da kallon kofar wajen. Na shiga ruwan a hankali sannan na tsaya na cire bra, na shiga na fara wasa da ruwan cikin jin dadi da farin ciki. Ina wanka.
... Anyi shagali amma zuciyar shi yana gurin Buhayyah, ala-ala yake ya zo ya ganta ba shi ya bar gurin ba sai karfe biyar, tun da ya shigo ya sami tsofin abokanshi za suka zo bikin, nan ma suka yi sallah basu bar gidan ba sai karfe goma, sannan ya hauro sama, ya shiga dakin yayi wanka. Kafin ya fara Niman ta, garin bude bude ya shiga dakin ya hango bowl na kayan fruit sai ruwa a gora. Bata san ya shigo ba. Tana wasa da ruwa. Daga ita dai pant.
Tsigar jikin shi ne ya mike.
"Sannun"
A firgice na kwalla ihu tare da juyawa.
"Ya Allah! Meye nayi da zata kashe ni" da sauri ya fita daga dakin nima kuma. Na kama kayana na saka, cikin wani irin kunya, na fito..yana tsaye a bakin kofar.
"Ke baki da hankali ne? Taya zaki zauna babu kaya " kamar zata yi kuka tace mishi.
"Kayi hakuri" ta wuce da sauri. Bin k'ugun ta yayi da ido zuwa kirjinta da suke mishi gizo, kayanta ya nuna mata tare da koranta ta bar mishi dakin baki daya.
A hankali na bar part din shi, na nufi gurin Aunty Mufeedah.
"Ina kika shiga hankalina ya tashi"
"Hmm, ina nan"
"Amma ince babu abinda ya faru?"
"Wallahi ban yi kome ba"
Na zauna a gefenta, take bani labarin abinda ya faru da ban gani ba.
"An daura auren Daddyn Aroosh da Natashah bikin sai bayan layya"
"Allah ya tabbatar da alkhairi" na fada ina jin babu dad'i. Can kuma ban ga amfanin jin babu dadi na ba, kawai na share.
Da safe muna karyawa, sai ga Khamil, yazo ya zauna kusa dani.
"Ina kwana Umma ina Kwana Abba, brothers ina kwanan ku. Abar kaunata ina kika shiga? Na kasa barci saboda ban ganki ba do ga wayar da na sayo miki jiya tare da layi, please idan kin ga kirana ki dauka, zan tafi wani aika ne ki gaya min me kike so na saya miki. Muna june next month Birthday dina, ki ajiye min abinda xan yi farin ciki da fatan zaki zo ko?"
Kamar Status haka na zuba mishi ido, shafa kumatuna yayi sannan ya yi musu sallama ya tafi.
"Zanci Uban wannan gayen?" Inji Halwani.
"Ke kuma kin zauna sai surutu yake miki ba zaki ci Uwar shi ba"
Buga table din yayi yana faɗin.
"Ya isa, ki hada kayanki yau zaki bar garin nan" inji Asad.
"Ai ba ita daya ba, dukkan mu tafiya zamu yi tunda an gama kome."
"Lion King, me yasa kake kokarin shiga tsakanin mu ne? Meye matsalar ka da Yarinyar nan?"
Mik'ewa yayi sannan yace mishi.
"Yarinyar nan sabida ni take gidan nan idan na kore ta zaka iya dawo da ita ne? So please karka kawo min shirme a magana ta" ya faɗa tare da barin gurin. Fuskar shi a murtuke
Warning. This article contains pornography and sex warnings for girls and widows ..
7/11/21, 10:31 AM - Buhainat: *_ALIYU ASADULLAH♡_*
'''The Lion of Monarchy'''
MrsUsman400
Chapter 1️⃣7️⃣
Har ya isa bakin kofar, yaja ya tsaya tare da juyawa yana kallon waje.
"Buhayyah! Ki ajiye wayar Khamil! Idan kika Kuskura na ga kinyi amfani dashi sai ranki ya b'aci wallahi tunda kin zama Celebrity kowa sai kwallon yake dake"
Ya fada tare da barin gidan, kaina a sunkuye jikina sai rawa yake. "Ke ki nutsu" inji Halwani,
"Wallahi Mama ban ruke shi ba, shi ya kawo"
"Ke tafi can indai Aliyu ne baki ga danyen halin shi, ba sai ya kara guntsuma miki rashin arzikin shi."
Ai bamu tashi a gurin ba sai da Halwani ya sani dariya. Bamu bar garin Tankara ba sai yamma, domin da rana tafiya nayi gidan Innah Larai, na kai musu kayan da nazo musu dashi. Ranar kamar su dauke ni haka dauke ni, haka na wuni na dawo sabida kiran da ake min zamu koma gida. Tunda na shiga gidan ya kafe ni da ido. Haka na sunkuyar da kaina tare da shiga motar muka bar Tankara. Tunda muka shiga cikin jirgin. Na mike tare da nufar ban daki, yana kallona yabi Ni dashi sannan ya bi bayana, ina shiga yana turo kofar.
"Wayyo Allah!"
"Ki min shiru, da nace ki shirya da wuri shine sai da aka bi ki."
"Toh kayi hakuri"
"Hell You da hakurin!" Ya daka min tsawa, kamar zan yi kuka nace"toh Allah ya baka hakuri" tsaki yayi tare da fita daga ban ɗakin, kallon shi Mabrooka tayi dake tana bayan shi, shiga ban dakin tayi na mike a razane.
"Kin zata kwarton kine ya dawo? Shegiya mayya" ta kai min duka a cikina, sake rufe Ni tayi da duka. Kamar ta samo yarta. Dakyar ta kyale ni dan ganin kar a gane yasa ta Barni a yashe, sakamakon gwara min kai da tayi da abin ban dakin na suma.
Shiru ban dawo ba, yasa Aunty Mufeedah ta biyo bayana,.anan ta ganni a yashe. Da gudu ta fita ta gayawa mutane dole aka zo aka fitar dani. Kallon Mabrooka yayi. Yasan itace zata yi haka. Bai ce kome ba, ganin Halwani da Mufeedah suka kokarin dawo da ita hayacinta, ya sashi jin kamar zuciyar shi Halwani yake tab'awa.
"Kyale ta haka mufy duba ta,"
"Toh amma ai aikin mu ne ko? Tunda na."
"Please rike maganar ka, bana bukatar kome daga bakinka, Mufeedah duba min Yarinyar nan"
"Ok" duk da ta maida hankali akan ceto rayuwar ta, haka bai hana Halwani gaya mata abinda zata yi ba, can kuwa aka yi dace numfashin ta ya dawo.
"Sannun kinji"
Lumshe idanun nayi sannan na dauke kaina. Gurin zamanta suka maida ita, sannan suka shiga tattaunawa akan abinda ya faru, ina jin su goge bakina nake inda jini ya taru, a raina nace.
"Indai zata min duka haka sabida mijinta meye Matsalata dashi? Meye damuna dashi? Zan bar mata mijinta zan bar mata mijinta. Har muka isa Abuja idanun shi na kaina, ban kalli inda yake ba, sun so kai ni asibiti amma naki, dole suka hakura domin bana son zuwa.
A hankali na saba da Halwani musamman yadda na fahimci shima dan cikin gidan ne, kuma aka masifar kaunar su, ganin duk inda zai tafi ina biye da shi. Haka ba karamin bawa Asad haushi yayi na, kuma abin da yake tsoro matsalar da nake fama dashi. Sai da muka yi sati Daya muna wasan boya dashi karshe dai ya tattara ya gayawa Maman su ya sama min aiki a kamfanin shi dan haka har da drive ba nima min, dan haka sai na daina wasan boya dashi.
Ranar Asabar aka gaya min, ranar Lahadi ina kwance Mufeedah take gaya min.
"Ana niman ki a waje" ta gaya min.
"Toh waye? Ni da ba fita nake ba"
"Oho idan kika je zaki gani"
Tashi nayi na saka doguwar riga da gyale na fita, ina daga bakin baranda na hango shi yana cikin motar shi.
"Lallai wannan mutumin taci uwar renin hankali." A hankali na sauka tare da isa gurin shi na tsaya tare da buga mishi motar. Banza yayi da ni, kamar baya gurin.
Yana kallon lokacin da tafito tana kallon inda yake, yasan kuma shi yace a kirata, shine zata zo ta buga mishi window. Cizon bakin shi yayi sannan ya cigaba da abinda yake. Sake buga kofar nayi. Yaki buɗewa. Kawai na juya zan koma cikin gidan ya zuge glass din tare da cewa.
"Sabida kin rena ni ko?"
Tsayawa nayi kafin na juya na kalle shi, dauke kai yay, sannan na isa daya gefen na bude tare da zama.
"Idan wadancan yan iskan ne baki iya nutsuwa zaki bisu amma kuma ni idan nai magana sai ki rena min hankali." Cikanka bance mishi ba, haka muka nufi Sahad store na nan Abuja, ya zuba min kaya musamman dogayen riguna da suit na mata, sannan muka nufi sani gurin kayan makulashe.
Zama nayi kamar yadda yayi, sai lokacin na lura da Shamaki vanillah. Haka yake jikin rigar su, a hankali suke ajiye mana kome, kallona yayi tare da harde kafarshi.yana kallon yadda na zubawa abincin ido. "Kici"
"Nakoshi"
"Better eat domin ina da inda zani dake" a razane na kalle shi. Yayi wani fuska kamar bashi ba., Haka na soma cin abincin jikina yana rawa, har na gama sannan ya saka aka kuma zuba min wasu abincin muka fita daga gurin muka nufi gida. Muna isa gidan yaga ina kokarin fita ya ce min.
"Ya kina shan maganinki kuwa?"
"Eh"
Daga haka ya bude min motar na fita, ina fita na sauke ajiyar zuciya. Na nufi cikin gidan da kaya niki niki. Na gayawa Mama, murmushi tayi sannan tace.
"Kinyi mishi godiya? So gobe Natashah zata zo garin nan dan haka ki dan kame kanki."
"Insha Allah zan yi yadda kika ce"
Sannan bar gurin na koma d'akina.
*** Washi gari
Da Asuba na shiga kitchen, ban fito ba sai karfe bakwai da rabi na shiga daki nayi wanka tare da shiryawa cikin kayan da suka yi min mugun kyau. Kasa dauke idanu Halwani yayi a kaina, yana faɗin.
"Zan kai ki yau"
"Akwai driven da zai kai Ni" na fada da sauri gudun kar yace sai ya kai ni. Daga haka na mike nayiwa Mama sallama, tare da barin gidan. A kofar waje muka hadu da Mabrooka. "Aunty Buhy! Kin kai Ni school" "ina kwana Aunty" na gaida Mabrooka a tsora ce.
"Nace ki rabu da mijina amma kinji? So duk abinda na miki ke kika saya."
Da sauri na bar su a gurin dan nasan bata da hankali sai ta saka min hannu. Cikin sauri muka isa kamfanin ya gabatar da ni a matsayin sabuwar sakatariyar shi. Ba laifi sun amshe ni kamar yadda yace sai dai yan matan.da suke kamfanin sun ji babu dad'i.
Ban damu ba, na fara aikina ina sane da abubuwan da ake fada a cikin kamfanin baki daya. Sai dai a bangare shi da zaran yayi bako aka ganin zai su ce Mishi.
"Wannan sakatariyar naka ba karamin kyau take dashi da." Sai ya zo fuskana yake cewa.
"Mumuna da ita, da hanci a yanke?"
Idan naji haka sai naji babu dad'i. Amma bana iya koda kula abinda yake min, na rike aikina da muhimmanci, tare da yarda da ƙaddara na kuma rike kome tsakanina da Allah, yawan maganar da mutane suke ya maida ni Office din shi.
***
"Wannan son kai ne fa, taya zaka dauki yarinya ka maida ita office dinka, sannan ka hana kowa mata magana." Inji Bashi.
"Kaga malam karka fara zargina ni ba.mutumin banza bane"
"Amma kana son yarinyar, kuma shaidan ai ba abokin kakan ka bane"
"Ban san bura uba"
"Can ta motse maka"
Haka suka gama fadar su kafin suka shiga hiran arziki. Dama sun saba ba sabon abu bane a gurin su.
*
Yau ina sauka a motar muna haduwa da Prince Khamil. Zuba min ido yayi sannan yace min.
"Dama nan ya kawo ki? Ok shiga kiyi sign ka fito mu fita"
"Khamil don Allah karka ja min magana".na fada mishi kamar zanyi kuka.
"Ok na shiga nayi miki ne"
Sanin zai aikata ya sani maza na shiga ciki nayi kome sannan ina tsaye tare da gaya musu zan fita dai an jima zan dawo.
Tunda muka fita dashi zan iya cewa ban tab'a farin ciki irin na ranar ba, sam na manta da Asad, domin kuwa mun yi yawo sosai mun shiga inda nake so. Ya kai ni ko ina.
Kallon yan Office din shi yayi bayan ya cire tie din shi.
"Kuna kallo wani dan iska ya dauke ta? Sannan kuna gaya min wani dan iska ya dauke ta" jan abin yayi tare da cewa.
"Ga baki daya nayi fire dinku"
"Sir don Allah kayi hakuri"
Take aka shiga niman Bash, domin ya dakatar dashi.
--
Kallon shi nayi kafin nace mishi.
"Ka ga sir Khamil wallahi ban shirya soyayya ba, sabida Ni ba kowa bace, sannan bani da dangi sai Sir Asad don Allah karka jazamin matsala da shi. Kayi hakuri ba naki soyayyarka bace sai dai ance kwarya tabi kwarya."
"Ko kina soyayya da Asad ne?" Da sauri na kalle shi kafin nace mishi.
"Ko daya kawai shi kamar Uba ne a gare Ni, don Allah karka kawo wani damuwa a tsakanin mu," a bakin kamfanin ya ajiye ni, sannan na fita tare da mishi godiya, a hankali nake tafiya dan naga kowa kamar harara na suke.
"Bash wato sun mai dani dan iska, idan kuma kidnap..." Ina shigowa Khamil yana shigowa tare da cewa.
"B baby gashi kin manta da shi"
Da sauri na amsa ina cewa.
"Thank You"
"Ki koma inda kika fito" cikin renin hankali ya kalle Asad sannan yace mishi.
"Wow! Nagode B baby muje, daga nan Tankara zamu wuce a dankara mara aure!"
"Ke dawo nan" ya faɗa a fusace,
"Kinga b love muje kinji"
"Queen Been" kamar wanda aka tsinka min laka na haka na ji baki daya na kasa koda d'aga kafana, takowa yayi tare da kallon Khamil dai-dai shigowar Halwani.
"Ita wannan kayan mallakin Aliyu Asadullah ce!" Ya saka hannun shi a k'uguna, yana kallon Khamil da Halwani da ya shigo.
"Duk wanda ya Kuskura zan bashi ciwon kai" sannan ya juya dani Office din shi, ya ture ni a saman sofar Office din. Ya shiga bala'i kamar zai dake ni, dukar kofar Khamil.
"Wallahi baka isa ba, sai na aure ta"
"Kinji abinda wancan jakiin yaje fada ko!"
"Toh wallahi sai na aure ta."
Haka ya zauna yana jin haukar.da Khamil yake.
Haka yan matan office din shi sai gulma suke, dan haka na basu damar haka ta hanyar dauke kaina daga gare su. Ko a gida ma fada aka yi kamar za kona gidan, domin har Halwani yayi fushi ya tafi Khamil kuma yace sai ya aure ni da karfin tsiya. Washi gari ina zuwa Office ya mika min takardan shiri zamu tafi. China.
Tunda naga yadda tsarin tafiyar nake na dawo gida, tare da gayawa Mama, dake tafiyar akwai yan mata acikin shi zai ban sami matsala da ita ba, muka shirya baki dayan mu. A daren ranar muka yi tafiya, washi gari muna barin garin sai ga Natashah. Tunda na shiga jirgin nake jin mara na yana ciwo, daurewa nayi har muka isa garin Beijing. Da tsakiyar rana, san ma ana mugun sanyi. Tunda muka isa nake jin bazan iya sauka ba, dan haka shi ya dauke ni, tare da nufar motar da yazo daukar mu, sauran sun bi babban motar da yazo daukar su. Ni kuma ya bar ni a cikin nashi. Kallona yayi tare da cewa.
"Ciwon cikin ne ko Period din kine?"
"A'a bashi bane" "ba wanen? Toh wane yake damunki" kuka na saka mishi, tare da rufe idanuna. Wani hadadden hotel ya kai mu, aka bashi daki, ya nufi dakin dani ta elevator. Muna shiga ya matse ni. Yana me shinshina wuyana.
"Abin ne ya motsa?" Ya fada min kasa kasa, rike rigar shi nayi.
"Eh" na d'aga mishi kai. Soft and smooth lips din shi naji akan wuyana, yana sake min wani irin. Breath din shi a wuyana me mugun dumi, rike shi nayi ina shiga jikin shi.....
Warning. This