Showing 12001 words to 15000 words out of 98705 words
aiki bayan sallah zan cigaba, nayitawa Aunty Nafy godiya. Sannan tace min.
"Idan kin sami lokaci kina zuwa gidana duk da zamu hadu a gidan Aunty Firdausi, suna hanya kinji."
"Insha Allah Aunty!" Na gaya mata.
Bayan na gama na fara zuwa gidan Maman Uwani, nakai mata kome ta gani, sannan tayi min fadan Alkhairi. Na dawo gida.
.....
Wurgi tayi da jakarta tare da fashewa da kuka, kallonta Mahaifiyarta su tayi tare da cewa.
"Lafiya Natashah?"
"Mum sun ce bani naci ba, na fadi duk wahalar da nayi, sai wata yar matsiyata ce taci."
Kallonta Yayan yayi tare da cewa.
"Yar gidan Uban waye a cikin tankara?"
"Wata wacce talauci ya kare musu ne sunan ta Buhayyah."
"Bani hotonta"
Jikinta yana rawa ta mika mishi wayar ta, tare da mishi kwantancen unguwar kaftawaye,, koda ya fita wayar shi ce tayi kara tare da dauka abokin shi ne tuni ya manta da wata Buhayyah.
Rarrashinta Hajiya Balaraba tayi sai da tayi shiru, tare da gaya mata koda haka burin su, ta auri Asad shine babban abinda take bukata, ga ilimi ga wayewa ga Uwa uba kudi da kyau. Na asalin shuwan chadi. Wannan ba karamin mata dad'i yayi ba.
--- satina biyu da komawa makaranta aka fara shirin azumi, gashi naji suna cewa za a tafi hutu sabida zafin da ake a garin tankara.
Ina kwance wani yaro ya shigo wai.
"Buhayyah tazo inji Maman Uwani" tashi nayi tare da cewa.
"Toh gani nan"
Riga da wando na kayan barci ne a jikina sannan na saka hijab tare da cewa Siyama.
"Kizo muje!"
"Kije duk yadda aka yi kya gaya min"
Ta faɗa min tare da cin taliyarta" fita nayi, daga gidan.
Na isa gidan Maman Uwani, mika min shayi tayi tare da soyayyen kwai da brodi, kadan nasha nace mata.
"Nagode;"
"Alhamdulillahi mutanen Turai sun iso, nan da kwana takwas wasu shigo da fatan kin shirya keda yar uwanki?"
"Eh mun shirya"
"Toh akwai abu daya, har da Babban dan su zasu zo da matar shi da yaran shi biyu, amma kuma mafadaci ne gaskiya zan gaya miki.dan haka ki kiyaye abinda zai hada ku. Sauran yaran basu da matsala sai Sawwama dab itama tana da wulakanci, akwai Mufeedah bata son magana amma likita ce, ita kuma tana da kirki. Amma zaki sha aiki dasu. Yadda kike da hakurin nan, ki kara akan haka zaki sha mamaki."
Wallahi Maman Uwani mace ce fa tasan darajar rayuwa, dan haka da zan fito ta haɗa ni da abin karyawa na kawowa Innah ta, tunda na gayawa Siyama sakon tayi tsaki.
***
A Abuja suka sauka, a mansion din su, unguwar yayi kyau, dan haka suka shiga kasuwa tare da karo sayayya da suka yi, kayan da suka kawo daga can aka turo a babban mota ya kai musu Tankara aka zuba a gidan.
Kamfanin shi na nan ya je ya duba, tare da jagorancin Yazed, kanin Bashir, ko ina yayi kyau, sannan yace mishi.
"Insha Allah duk sati xan na zuwa duba kamfanin Allah ya tayaka rikon."
"Amin Ya Allah, Nagode da bani amanar da kayi Nagode Yarimar tankara."
Share shi yayi sannan ya nufi hanyar waje.
"*"
Ya shiga gidan ya same ta kwance.
"Ya dai"
"Babu" tace mishi.
Har zai wuce ya dawo da baya tare da zama yana kallon ta.
"Akwai wani abu mana"
Kukan da take dannewa ne,.ya kwace mata ta mika mishi wayarta tare da cewa.
"Yarinyar ta dame ni, ban hanaka niman aure ba amma me yasa ba zata daina turo min sakon cin mutunci ba?"
Lashe bakin shi yayi sannan ya rungume ta.
"Idan ba yau ba ban santa ba, dan haka zan yi magana da Mufeedah taja mata kunne ya sunan ta?"
"Natashah Abbas"
D'ago kanta yayi tare da cewa.
"Wannan yarinyar?". Tsaki yayi tare da barinta zaune. Dan bai ga abin kuka ba, mata dai basu da abin yi.
---- sai da suka kwashe kwanaki bakwai ana gobe Azumi suka sauka a garin tankara, tun daga Airport ake dayawa Asad hannu da tutar masarautan, ana kiran shi da Yarimar tankara. Shi kam hidiman shi yake, sun isa cikin masarautan wanda yake dauke da tsofin ginin gadon zamanin iyaye da kakanni,. A hankali ya sauko daga kafar shi daya.
"Gafara jama'a Gafara dan sarki jikin Sarki, waye zai ce ba kai ba, akawali kafi musaya, farar tantabara mai yaɗa alkhairi, gamji kake sara da sassaka baya hanaka toho, hasken farin wata game duniya.
Kasakali me tafiya da tankar taguwar, alfadari me kashin kudi , hadarin kakka lalata aikin ragwaye, mesa me hadiyar namun dawa, mage kake me kwanciyar daukar rai. Girgije kare wanda Allah yaso, An gaida Yarimar Tankara Aliyu Asadullah zakin Tankara namiji Uban Yan bako Uban Firdausi Uban Ahmad, An gaida Mijin Mabrooka, ango Mai rabo. Dawisu me adon ban mamaki. Aliyu ASADULLAH. Aliyu Haidar. Aliyu Ghaji, Ni Sarkin Kirari na maka kirani Yallabai idan ka toshe Ni da Umra wannan kadai ya isa na ambace ka da Hadarin gabas....
Warning. This article contains pornography and sex warnings for girls and widows ...
7/9/21, 8:02 PM - Buhainat: *7*
Karan busar algaita da harbi ya sanya kanshi kamar zai fashe dan haka ya dafa Bashir da yazo jiki.
"Man ya dai?"
"Jiri"
Haka suka shiga cikin fadar tun daga bakin kofar ya cire takalmin shi. Baba Danrimi ya saka aka kwashe mishi zunzurutun rashin yarda da abinda zai iya faruwa a cikin masarautan.
Yana isa gaban me Martaba Sarkin Abbas Muhammad Al-Amin, ya zube tare da kai gaisuwa.
"Yarima Aliyu Asadullah yana gaisuwa mai martaba, yazo hutun shi da Azumi nan"
Cikin jinjina kai Mai Martaba ya amsa tare da nuna alamar a bashi Anis da yake hannun Moddibo, mika mishi yaron aka yi tare da mishi addu'o'in sannan ya kalli Sauran Hakim fadan ya kalli Turaki yayi kasa da kanshi bayan ya gama jin abinda ya faɗa.
Mik'ewa yayi tare da cewa.
"Mai Martaba ya amshi gaisuwar Aliyu sannan ya kuma kara mishi da kyauta biyu. An bashi Yarimar Tankara tare da auren Gimbiya Natashah" a firgice ya d'ago kan shi yana kallon Bashir, rike hannun shi yayi sabida rawa da jikin shi yake yi.
"Madalla kowa ya shaida Nan da bayan Sallah daukacin Al'ummar Tankara zasu shaida Auren Aliyu Da Natashah Allah ya nuna mana, sannan za a hada da bikin nadin sarautan shi."
Inji Me jawabin Sarki. Lumshe idanun shi yayi tare da ji kamar zai bar duniya dan bakin ciki.
Bashir ne Ya d'aga kai cikin nutsuwa yace.
"Abba mun karb'a kuma mun gode Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana, Abba mun gode"
"Yarima Aliyu Asadullah ya amsa daga bakin Matawallen Yarimar Tankara, Mai Martaba Matasa samari sun asma, sun gode kuma sun amsa kuma sun gode.". Cikin farin ciki Bashir ya kalli Mahaifin shi. Yana jin wani irin kwalla na cika mishi ido. Yace.
"Amadadin ahalin Aliyu Ghaji Shamaki muna miki godiya ga Mai Martaba, Allah ya saka da Alkhairi. mun gode mun gode, mu ahalin Magajiyar Babban daki mun kara godiya bayan wanda muka yi, Yarima Aliyu Asadullah ya amshi kyauta da aka bashi. Mun gode."
Mintsin shi Asad yayi cikin jin haushi, haka suka gama godiya sannan suka nufi cikin gidan. Bayan sun fito daga cikin fada akwai wasu tsofin bishiyar kuka da tsamiya wanda suke cikin masarautan an ki sare su.
Rangad'a guɗa aka yi tare da shewa da murna, kafin kace me busa da Algaitu da kiɗa har da sarewa, ana shewa. Abinda aka ce a tarihin masarautan ba a tab'a ya ba, rabon da ayi haka tun zaman sarki Ali Ghaji, a watan da zai rasu sai Sarki Saminu a lokacin da ya kudiri a niyyar daidaitawa da aljanun gurin shima sun mishi wannan al'amarin.
Yau gashi sunyiwa Aliyu Asadullah.
Dakyar ya sami kanshi tare da nufar cikin gidan su, a hanyar shi ya hadu da Khamil, yana zaune akan motar shi fuskar shi manne da wata sunglass, d'ago kai yayi tare da kallon shi yace.
"D'an kasuwa?" Bai kula shi ba yayi gaba abin shi. Dira yayi tare da bin bayan Asad. Har ya cin mishi.
"Anyway ban san me kayiwa wancan mutumin ba da ya zabi ya baka matsayina, bayan yasan ni ya haifa,.koma yayya ne zan dawo da abuna sabida ba zaka zo fadana ka amshe min"
Kallon shi yayi daga sama har kasa sannan yace.
"Me kace?"
"Baka gane Yaren da nayi maka bane?"
"Ban fahimta ba"
"Karka rena min hankali! Mana, taya zan maka magana da Hausa kace baka gane ba."
"Idan ka sami lokaci ka rubuto min na gani" wuce shi yayi dan bai da lokacin shi.
Irin wannan yaran hauka yake damun su, shi yasa baya shiga harkan Moddibo, yana shiga da gudu kanen shi mata suka rufa mishi. Suna cewa.
"Congratulations Yaya Asad, mun taya ka murna. Masha Allah Ubangiji ya tayaka riko."
"Amin Ya Allah," ya faɗa tare da kallon Mahaifiyar shi cikin kara mishi kwarin gwiwa, ta sake mishi murmushin jin dadi. Janye Mufeedah yayi tare da nufar Mother.
"Umma!"
"Allah ya tayaka riko, bayan matsayin Shamaki sam babu wata sarautan da Yaran Magajiyar Babban daki take dashi sai yau gashi an baka Yarimar Tankara, nasan ka amsa ne dan ahalinka Nagode da wannan ƙaramcin da kayi mana"
Kwalla ne ya cika mishi ido a sanyayye yace mata.
"Nagode Umma na,"
Sannan ya kalli matar shi ya shige cikin gidan, bin bayan shi tayi cikin nutsuwa, tana isa ta samu ya rufe kofar. Tare da shiga ban dakin, buga kofar dakin tayi tare da cewa.
"Assalamu alaikum na shigo"
"Eh princess Mabrooka"
"OMG" ta faɗa da karfi ta bude kofar ta shiga da gudu, tana ihu. Bude mata hannu yayi tare da jin wani irin dad'i a ranta.
"Nagode My Prince" shafa bayanta yayi tare da cewa.
"Me too Princess"
Goga kanta take a kirjin shi tana kuma jin wani irin dad'i.
---
A kasa kuwa kitchen suka shiga tare da Cigaba da aiki. Wayar Salulan Mother yayi kara ta saka a kunne.
"Kai Nafi ki kawo mana, bamu jima da isowa ba, Mutumin ki aka bawa Yarima tare da auren Natashah."
Murmushi tayi sannan tace mata.
"Karki Damu ni nasan abinda na haifa, indai Asad ne babu macen da zata juya mishi ra'ayin shi, itama Matar shi kokari muke akan shi, amma bata jin dadin shi. Sannan rawan kai kuwa zai gyara mata zama ai na gayawa Mabrooka idan tayi hakuri zata more idan kuma ta juya halin ta. Wallahi zata wahala. Gwara ta a hankali."
Daga haka suka gama wayar sanan suka ci-gaba da aikin.
"Mother amma da an hakura da yarinyar nan sai gobe Insha Allah tazo ba"
"Kai Mufyy kawai tazo na ganta a zahiri"
Juyawa Mufeedah tayi a zafaffe tace mata.
"Munafuka algunguma. Kice kina son ganin ta ko hotone ya gyara ta" dake tasan halin Mufeedah bata da mutunci yanzun dai ta dake ta, yasa bata yi magana.
----
Ina shirin tafiya makaranta Maman Uwani tayi mana sallama, da sauri na bude mata babbar kofar ta shigo ita da Aunty Nafy.
"Aunty, Mama, ku shigo"
Na bude musu kofa tare da musu iso a tsakar gidan da na share tare da wanke shi, taburma na dauko musu sannan na shiga kitchen na dibo musu ruwan sha. Leka dakin Inna larai nayi domin na gaya mata Mama tazo.
"Toh munafuka mun ji muryan su."
Had'iye yawu nayi cikin tsoro na fito ina murmushin yake.
"Mun zo zamu kai ku cikin fada ne kun shirya?"
"Eh mun shirya Siyama tana shiryawa ne"
Na fada tare da shiga dakin na dauko hijab dina da Safa, sai Nikab. Sannan na sallami Inna, shiga dakin suka yi tare da gaida ita.
Bayan sun fito suka haɗu da Siyama taci Uban kwalliya zata aiki. Kallon Mamaki suka mata kafin suka ce mana.
"Toh muje"
Haka muka fita bayan sun gaisa da Inna larai, muka nufi inda motar shi yake. Tunda muka shiga muke hira jifa jifa da Aunty da kuma Mama.
Har muka isa Fada, kafin aka wuce damu cikin gidan.
"Buhayyah zaki cire nikab din nan fa"
"Toh Aunty" na fada a hankali.
A kofar shiga gidan muka tsaya bayan an buɗe mana get, muka shiga. Tunda nake a rayuwata ban tab'a ganin gidan da ya girgiza Imani na kamar ba za a mutu a duniya ba. A hankali muka fito daga motar, cikin hikima nake kallon kusurwan gidan. Waya Aunty Nafy tayi sai ga wata budurwa sanye da wata mayyar abaya, tana taku cikin nutsuwa da yauki.
"Aunty Nafy! Barka da zuwa Maman Uwani kamar ba zamu kuma haduwa ba, Barka da zuwa." Kallon mu tayi sannan ta watsar damu.
"Muje"
Ta saka wayar ta a kunne, muka nufi cikin gidan, wani sansanyar kamshi ne ya kama hancina, kallon gidan nake cikin nutsuwa da wata irin kamala. Kallon falon nayi yara biyu na wasa. Dake Allah ya daura min son Yara kamar diyoyin turawa, haka na isa tare da ɗaukar su.
"Honey!" Na fada tare da kai shi kirjina.
"Ajiye mana yaro, kalan talauci da fatara" tafada min.
Da sauri na ajiye shi, yaron bai san kome ba, ya rike ni gam. Tare da saka ihu.
"Dawo nan ki zauna Buhayyah"
Cikin rawan jiki na koma kusa da ita,dake muna shigowa Aunty Nafy ta shiga kitchen. fitowa suka yi tare da Aunty Nafy, murmushi dauke akan fuskar su.
Bata tab'a gani na ba, amma tana fitowa tace.
"Buhayyah ko?"
Murmushi nayi domin haka kawai matar ta kwanta min.
"Ina wuni? Kun iso lafiya?
"Lafiya lau, ya jikin Mamar naki?"
" Sauki sosai"
"Hello. Sun iso"
Ta faɗa tare da kallona, nan aka shiga yar hira tare da taya su murna bawa dan su sarauta, ina jin su.
"Nafi tace min kina N.C.E,, kuma kina zuwa da safe ya zamu tsara aikin mu ne?"
"Hmm! Yau zasu bamu hutu Insha Allah babu wata matsala." Na fada kamar dai yadda nake magana ta.
"Assalamun Alaikum!" Dai dai fitowar wata budurwa daga cikin kitchen. Suna ganin ta duk suka nutsu. Sai dayar ce take ta jan yan matan nan da hira. Tsoron su ya hana Ni motsi har muka gama magana ta kalle mu tace min.
"Ke ya sunan ki?" Cikin rawan kai tace.
"Siyama"
"Toh nawa zamu biya ku"
Kallon Mama nayi tare da wasa da hannuna.
"Hajiya ki bamu dubu goma"
Da sauri na d'ago kai da sauri ina kallon su.
"Toh Buhayyah bata ce kome ba"
"Mama duk abinda kika bani, Allah ya sanya mishi albarka."
"Dubu goma yayi miki kaɗan ne?"
"A'a wallahi Mama yayi yawa, ina laifin dubu biyu" baki daya suka zuba mata ido.
"Shi kenan dubu biyu yayi miki"
"Wallahi yayi min albarka ce nake nima ba yawan shi ba"
"Alhamdulillahi, shi kenan ke Siyama wanke wanke da shirya mana kitchen zaki yi, ita kuma Buhayyah zata tsaya a girki ne, Allah ya albarkaci zaman da zamu yi"
"Amin Ya Allah"
Saukowa wata mata tayi sanye da Jallabiya ta mata, tana kallon mu.
"Yaran da suka taso cikin talauci basu san darajar kudi ba, dubu biyu kudin da ake wanke min kafana a gurin Saloon." Sake mannewa nayi a jikin Maman Uwani.
Zuciyata tana wani irin bugawa.
Haka muka gama tsayar da shawara sannan muka mike zamu tafi. Daya daga cikin yan matan nan ta saka min kafa zan fadi.
"Ji jaka, babu ido ne a jikinki?"
"Kiyi hakuri wallahi ban lura ba ne, Sannun kiyi hakuri m"
"Karki saka min hannun ki ajiki dan ban san me kike nufi dani ba. Wawuya."
"Ke Mahirah wannan wani irin hauka ce."
"A'a mama wallahi nice na takanta."
A hankali ya sauko yana waya, hankalin shi yayi gaba, bai kallo gurin ba, yayi wucewar shi.
Haka muka fito bayan mun yi sallama dasu, aka bamu dubu biyu kudin keke napep.
Lokacin da suka iso gida zagin cin mutuncin suka min, bance musu kome ba.
Washi gari..aka tashi da azumi.
Da wuri na shirya tare da tadda Siyama.
"Ke ki tafi tunda nasan hanyar gidan." Jin haka nayiwa Innah sallama, na nufi cikin masarautan. Tun daga nesa Baga wasu dogarai da kuka wasu matasa. Sauri nake har na iso gurin su zan wuce.
"Prince ga ita"
"Kuci min Kaniyar ta"
"Ke dawo nan"
Cikina ne ya cire guri guda, wani uban tsoro ne ya kama ni, ban san lokacin da na fashe da kuka ba.
"Ke" dogarin ya sake min bulala tare da daka min tsawa.
"Wayyo Allah" na fada da karfi. Ina yarfe hannuna, duka ne yake babu tausayi balle Imani. Ganin Prince Khamil ne yake wannan hukunci babu wanda ya isa magana, daga can sama ya hango ta tana tsalle dogarai suna zane ta.
Cike da mamaki ya fito tare da kiran Mai Kano suka nufi kofar gidan. Har suka iso gurin zane ta ake, abun tausayi kuka take tare da yarfe hannunta. Tana basu hakuri. Naushi ya kaiwa dogarin sai da ya fad'i. Sannan ya kuma nausar dayan.
"Ka gafarce mu Yarima muma umarni aka bamu"
"Wuce da ita cikin gidan." Amsar bulalar yayi tare da watsawa Khamil a cinyar shi sai da ya diro a motar.
Warning. This article contains pornography and sex warnings for girls and widows ...
7/9/21, 8:02 PM - Buhainat: _ALIYU ASADULLAH♡_*
```The Lion of Monarchy```
MrsUsman400
Chapter0️⃣8️⃣
بسم الله الر حمن الرحيم...
"Dalla malam meye nayi maka?" Sake watsa mishi bulalar yayi a bayan shi sai da ya dira a saman motar. Dan dukar ya shige shi.
Yasar da bulalar yayi tare da cewa.
"Nasan darajar mace shi yasa na dake ka, kuma ka sake sai na baka mamaki ai ko dan albarkaci kaza kadangare yasha ruwan kasko, shine zaka zane musu yar mutane. Toh wallahi ka kiyayye mai nima,