Showing 138001 words to 139085 words out of 139085 words

Chapter 47 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

inda za ku je, na gaji da wannan yawan na ku kullum."


Khadija ce tace "To ni ka ban makullin tawa motar zan fita, ai dai kasan aro ne na baka jiya ko."


Kallon Usman yayi yace "Idan sarki ya bayar da izinin fita sai ku fad'a min zan kawo mu ku."


Cike da jin dad'i Usman ya aika mishi da sumbata yace "Allah ya maka albarka yarona, shi ya sa banda matsala da gidan nan ko bana nan nasan akwai original Usman a gidan, da ni ne da yanzu sun min fari da ido na basu makullan."


Fita yayi daga d'akin sai Usman daya kalli su Aisha yace "Ku kuma ki fito daga nan munafukai kawai, dama da kinga suna raba ido kinsan basu da gaskiya, kuma wallahi ku ka sake shigar masa d'aki ba neman izini da kaina zan hukuntaku."


Cikin turo baki suka sauko suka fita daga d'akin suna kumbura, dan tunda su ka ji Bilal ya rantse sun sa babu inda za su je, suna fita Usman ya kalli tsofaffin nashi yace "Ku shirya da kyau, wannan hutun na k'arshe zan had'a yaran nan da Bilal na aurar da su."


Wata sanyayyar ajiyar zuciya Khadija ta sauke tace "Alhamdulillah, wallahi naji dad'i da wannan maganar, dan duk sanda na kalli yaran sai naji fargaba ya ziyarceni, gashi k'awayen su sun fara aure, sai kaga an fara sakawa yaranka wani tunani na daban alhalin kana tsaye kan tarbiyarsu tsawon lokaci."


Haseenah ce tace "Allah yasa haka shi yafi zama alkairi, amma ka fitar musu da maza ne?"


"Eh to, a tunani na dai da zan had'a Aisha da *Kamal* (babban d'an Murtala) ne."


Humaira kuma sai a had'a ta da *Mujahid* (d'an Issoufou d'an uwan Usman), amma fa sai in basu da wanda suke so, dan ba zamu had'a su da wanda ba sa so ba tunda zamaninmu da nasu ba d'aya ba, da a lokacin yanzu ne aka mana auren da aka yi mana ni da *Dijangala* to na tabbatar ba za su zauna ba."


"Ai ko ni da ga yanzu ne aka had'a ni da kai to da babu abin da zanyi da tsoho." Cewar Khadija kafin ta d'ora da "A gaskiya dukansu sun fad'a min suna da samarinsu har shi Bilal d'in."


Kallonta Usman yayi yace "Kenan duk sun fad'a mi ki nine suka mayar bare."


Gwalo ta mi shi tace "Nifa uwa ce."


Haseenah ce tace "Aunty su wa suka fad'a mi ki suna so?"


Cike da k'asaita tace "Sirri ne tsakani na da yara na."


Tasowa Usman yayi ya bata kunnanshi yace "To fad'a min a kunne naji."


Ai kuwa rad'a mi shi tayi cewa "Bilal ya fad'a min suna soyayya ne da *Ikram* (yar Kaltume), sai Humaira tace suna soyayya da *Kamal* d'in da ka ke son had'a Aisha da shi, sai kuma Aisha tace wani yaro ne mai sunan *Jabir*, d'ane ga Alhaji Abbakar, amma kuma da wata yar matsala."


Kallonta ya yi yace "Matsalar me?" D'orawa ta yi da "Domin kuwa *Miemie* (yar Ashir) tana mutuwar son Bilal, dan har ta fad'a masa ma, kuma yace ba zai iya cewa baya sonta ba saboda tana birge shi sosai."


Dariya usman ya yi sosai kafin yace "Dan haka saiku shirya, yaronku da mata biyu zai fara insha Allah, na yarda da mazantakarshi."


_Tofa fan's wata sabuwa, ga Usman na shirin lak'abawa Bilal mata biyu a lokaci daya, tabbas akwai wasu darussa a cikin labarin rayuwar gidan Bilal, sai dai Meeranku yanzu ta zama lazy wrriter, da zan zo na kawo mu ku d'orawar shi amma ba zan iya ba saboda na gaji yasin._


*Alhamdulillah*


*Alhamdulillah*


*Alhamdulillah*


*Ina godiya ga Allah da ya nuna min na kammala littafi lafiya kamar yanda na fara, Allah ubangiji kasa a anfana da darasin dake ciki, Allah ka sa mu tsarkake zuciyoyinmu wajen yin kishi mai tsafta, duk wanda suke da abokan zama Allah ka k'ara had'a kansu, wanda basu da kuma Allah ka had'a su da na gari, Allah ka k'ara sanyaya mana zuk'atanmu.*👏👏👏


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya





Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,





Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan


Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490





A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,





Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu





Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC





Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku




This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there


Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online


It is free we do not charge for uploading novel


Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services






Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us






Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it






Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT






This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng


For feedback and support


Facebook : https://facebook.com/taskarnovels


Twitter : https://twitter.com/taskarnovels


Telegram : https://t.me/taskarnovels

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login