Showing 33001 words to 36000 words out of 139085 words
Chapter 12 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
har zuwa yamma, ko kwalliya ta yi taji yana kod'ata sai tace wai uwar gidan shi ba ta yi shi ya sa idan ya ganta da kwalliya kamar ya ga matar aljanna, hakan ya sa ta sawa ranta ta na zuwa gidan za ta cinye yak'in ba tare da tasha wahala ba, amma kuma gashi Mariya ta kawo mata wani labari da ya sa har ta fara had'awa da malamai.
_Toh, ko tunanin Usman ya fad'a mi shi daidai? Shin Haseenah za ta zama kamar yanda ya d'auka? Ko kuma dai *kallon kitse ne ya ma rogo*?_
*Mu koma labari*
Ko da ya dawo daga kan Bilal kai tsaye falon shi ya wuce, sak'o ya turowa Khadija ta same shi falo haka ma Haseenah da ke d'akin ta, hakimcewa ya yi ya na jiran zuwan su, (da alama Usmanu yan mulkin sun motsa, yau kam duk wacce ta yi wasa za ta gane shayi ruwa ne π), kusan a tare su ka shigo falon sai Khadija da ta k'ara da sallama, zaune su ka yi su na fuskantar shi su na kallon shi, d'ago kan shi ya yi ya kalli Haseenah ya kalli Khadija kafin yace "Kun gaisa ne da safen nan?"
Khadija da tasan waye mijinta ne ta yi saurin cewa "Sosai ma, har falo ta same ni ai, mun gaisa da ita."
"Da kyau." Ya fad'a ba annuri kafin ya d'ora da "Ku zuba mana abinci mu ci."
Satar kallon shi Khadija ta yi dan tasan ya same ta tana karin kummalon ta, amma jin haka daga bakin shi da kuma ganin yanayin shi ya sa tasan yau ba ya yanayin wasa, dan haka ta mik'e tare da Haseenah da ke ta wani yauk'i kamar za ta karye, murmushi ta mata tace "Kinga amarya zauna, ki zauna zan zuba."
Ci gaba ta yi da zuba ma kowa har ta gama ta aje farantin a gaban shi kafin ta matso kujerar ta kusa da shi, sai da ya fara saka hannu tare da bismillah sannan su ma suka saka, Haseenah dama haushi ne kamar ya kashe ta, Khadija kuma a k'oshe take neman agaji take, a tare su ka cire hannun su suna kallon shi, shi ma kallon su ya yi yace "Me ku ke nufi?"
Cikin wata shegiyar shagwab'a Khadija tace "Mun k'oshi."
Duk daba kuzari a tare da shi sai da ya murmusa yace "Ku na nufin ni kad'ai za ku bari? Ai ba ku isa ba, dan haka ku mayar da hannuwan ku."
Kamar za ta fashe da kuka ta shafa cikin ta tace "Ciki na fa zai fashe, ka ci kawai sai ka had'a da nawa ka ci."
Sama da k'asa ya harare ta yace "Sannu mai wayo, kenan ni na cika cikin nawa? To na k'i wayon."
Mik'ewa ta yi tace "To bari na je na amaye wanda na ci sai na dawo mu ci gaba ko?"
Da gayya Khadija ta dinga tafiya ta na wani juya k'ugunta, mazaunan ta na kad'awa yanda su ke so, sai da ta kai k'ofar fita ta juyo ta kalle shi dan dama a sanin da tawa mijinta ba ta ba da baya bai bita da kallo ba, su na had'a ta ga ya wani saki baki ya na kallon ta, cije leb'e ta yi ta kashe ma sa ido d'aya ta fice da murmushi, Haseenah Usman ta bi da kallo ganin ya wani wagale baki har da rumgume hannaye ya na kallon ta, sai da yaga ficewar Khadija ya sauke wata sayayyar ajiyar zuciya da murmushi a fuskar shi wanda shi kad'ai ya san ma'anar shi, a hankali ya zuro hannun shi cikin farantin da nufin ci gaba da cin abincin shi sai ya lura da Haseenah da ta kafe shi da ido, saita nutsuwar sa ya yi yace "Ya dai?"
Ita ma had'e abin da ke ran ta tayi tace "Ranka shi dad'e, wai me ya sa aunty Khadija ke jin dad'in anfani da gilashi a kowane lokaci? Ba ta tsoron ta samu matsala a idon ta."
Kallon ta ya yi ya na tunani, bayan gamsuwa da zuciyar shi sai kawai yace "Haseenah kema yanzu iyalin gidan nan ce, ba wani abu da za'a b'oye mi ki, Umman Bilal na fama da larurar ido ne, kuma anyi neman maganin amma har yanzu shiru ba labari, sai dai har yanzu ba mu cire rai da rahamar ubangiji ba, mu na sa rai wata rana za ta samu lafiya da yardar Allah."
D'auke idon ta ta yi daga kan shi ta kalli k'asa da murmushin jin dad'i a ran ta kuma ta furta "Ashe ma makauniya ce, gilashi shine idon ta, hum."
D'agowa ta yi tace "Allah sarki, Allah bata lafiya."
"Ameen." Ya fad'a ya na cire hannun shi ya wanke cikin wata k'aramar roba mai d'auke da ruwa, mik'ewa ya yi ya kalle ta yace "Zan d'an shiga d'akina na kwanta, misalin *11:00* sai ki tashe ni."
Mik'ewa ta yi cikin kwarkwasa tace "Ni kad'ai kenan zan zauna? Gaskiya a'a sai dai na bika mu je tare."
Kallon ta ya yi ya na sauke ajiyar zuciya yace "Haseenah kenan, kedai kawai ki na so ki hana ni bacci ne, amma idan ba haka ba me zai hana ki je wajen yayar ki."
Cikin sanyin jiki tace "A'a gaskiya, gwara na zauna d'aki na ni kad'ai."
Da mamaki sosai ya kalle ta yace "Me ki ke nufi? Haseenah akwai wani abu da ake mi ki a gidan nan da ba kya jin dad'i ne?"
Wani murmushi ta yi da bai kai zuci ba tace "Ba komai fa, kawai ka je ka kwanta abin ka."
Rumgumo ta ya yi jikin shi su ka nufi d'akin na shi ya na fad'in "Ai sai kin taimaka min kafin na yi baccin ko?"
Su na shiga d'akin ya cire doguwar rigar shi ya kwanta, hijabin ta ta cire k'ananan kayan ta su ka bayyana, bayan shi ta kwanta ita ma ta na shafa kan shi har zuwa kunne, ba tare da magana sai kuwa bacci ya d'auke shi, a hankali ita ma sai bacci ya yi awon gaba da ita, daga nan fa su ka shiga baccin su hankali kwance.
Khadija kuma na falo ita da Uwani su na ta hira su na kallo, har ita ma Khadija ta kwanta a kan kujera bacci ya soma d'aukar ta, *12:15* Uwani ta daddab'a k'afar Khadija ta farka, agogo ta kalla tace "Aunty, na ga sha biyu har ta wuce amma Bilal bai dawo ba."
Da sauri ta zabura ta mik'e zaune ta na fad'in "Abban shi ya fita ne?"
"Gaskiya ban ga fitar shi ba, dan har yanzu motar shi na waje."
Wayar ta ta d'auka ta kira shi amma ta na silent, dan haka ba ta sake na biyu ba kawai ta kira lambar Naseer, ya na d'auka ya fara da "Autar Hajia ya ake ciki ne?"
Cikin shagwab'a tace "Yaya na, Bilal ya na makaranta har yanzu ba'a d'auko shi ba, kuma na kira wayar Abban shi ba ya d'agawa, shine na ce ko za ka saka cikin yaran shagonka su d'auko min shi?"
Daga in da ya ke ya mik'e yace "Abu mai sauk'i, dama zaune na ke ina kallon titi, bara na isa da kai na na d'auko shi."
"Yawwa yah Naseer nagode."
"Uhum! Kar ki damu."
Aje wayar ta yi ta na mamakin abin da ya sa Usman mantawa da gudan jinin shi a makaranta, sharewa kawai ta yi ta kalli Uwani tace "Uwani, ki duba madafa ki ga idan babu kowa sai ki d'orawa Bilal indomie kafin ya dawo, dan kinsan abinci ya ke fara nema da ya sauko."
"To aunty." Ta fad'a ta na tashi ta nufi madafar, ba kowa a ciki dan haka ta fara abin da ya kai ta, sallama ta ji tun daga tsakar gidan, lek'owa ta yi dan madafar a bakin k'ofar shiga duka b'angarorin take, su Rabi'a ne da kuma matar Kabir *Jauza'u*, amsawa ta yi ta na fad'in "Aunty Rabi'a sannun ku da zuwa."
"Yawwa Uwani sannu, aiki ake?" Cewar Rabi'a, k'ofar Haseenah su ka nufa Rabi'a ta sa hannu ta bud'e sai ta jita a rufe gam, kallon Uwani ta yi tace "Amaryar ba ta nan ne?"
"Ta na nan, amma ina jin kamar ta na d'akin Abban Bilal." Ta fad'a da nuna mu su falon na shi, Jauza'u ce tace "Shikenan bara mu shiga wajen aunty Khadija to."
Da sallama su ka shigo a bakin su, Khadija da ke zaune ta na danna waya ne ta d'ago ta kalle su, sharrin shaid'an da zafin kishi ya sa Khadija tuna irin k'iyayyar da yanzun su ke mata, a ganin ta suna matuk'ar farin ciki da k'ara auren Usman, su na jin dad'i saboda an mata kishiya, sai kawai ta ji ba ta buk'atar sakar mu su fuska kamar baya, fuska ba fara'a ta amsa da "Wa'alaikum salam."
Suma k'asa su ka zauna Jauza'u na fad'in "Aunty Khadija ke kad'ai zaune?"
Kallon ta ta yi tace "Umm."
"Ina kwana aunty Khadija?" Cewar Jauza'u, ta na ci gaba da danna wayar ta tace "Lafiya k'alau, ya ki ke?"
Duk da Jauza'u ba haka ta saba gani ba ammata dake tace "Lafiya lau, ina Bilal?"
Ba tare da ta d'ago ba tace "Bilal ya na zuwa yanzu daga makaranta."
Sai lokacin Rabi'a tace "Ina kwana?"
D'agowa ta yi ta jefe ta da wani banzan kallo kafin ta yi k'asa da kan ta tace "Lafiya, ya gida?"
Sai da ta harare ta ta wutsiyar ido kafin tace "Lafiya lau."
Shiru ne ya d'an ratsa wajen kowa da abin da ke sak'awa a ran shi, Jauza'u kam duk ta ji ba dad'i dan har ga Allah ta na k'aunar Khadija, saboda ta mata abin da ko mijin ta bai iya yi mata ba a lokacin da baya da k'arfi, su na haka babu mai magana shiru kamar ba gidan wannan Khadija ka zo ba wacce ke washe baki idan ta yi bak'o har ya tafi ta na rawar jiki, amma yau gashi sai wani shan k'amshi take.
Usman ne ya zabura ya tashi ya na rarraba ido, da sauri ya kalli agogon da ke fuskantar shi, " *12:45*." Shine abin da ya fad'a da k'arfi har ya sa Haseenah tashi zaune ita ma, da hanzari ya sauka daga kan gadon ya na d'aukar doguwar rigar shi ya zura, makulin mota ya wawura a gefen gadon ya juya zai fita Haseenah tace "Wai saurin me ka ke ne haka?"
Ba tare da ya juyo ba yace "Yarima zan d'auko, lokacin tashin su ya wuce sosai."
Da sauri ta duro daga kan gadon ta tari gaban shi tace "Amma haka za ka fita ko wanka ba ka yi ba?"
Ture ta ya yi daga gaban shi yace "Wani wanka dallah, yaro na can tsaye ya na jira na, ban san a wane hali ya ke ba."
Fita ya yi daga d'akin ta bishi da kallo, k'wafa ta yi ta fita daga d'akin ita ma kai tsaye madafa ta nufa da tunanin d'ora silalar nama sai ta yi wanka, ta na bud'a k'ofar ya yi daidai da Uwani ma za ta fito, hakan ya sa Uwani bige ta ba ta sani ba, rik'e hannun ta tayi da ta bugu ta na ma Uwani kallon tsana, cikin jin zafi da b'acin rai ta kife Uwani da marin da ya sa farantin indomien zubewa k'asa saboda yanda ya zo a bazata , dafe kunci ta yi ita kuma ta na fad'in "Dan uban ki ni za ki bige? Wacece ke a gidan nan? Me ma ya kawo ki madafar nan? Ko kin manta yanzu ni ke aiki a ciki ko wacce ta aje ki sai na yarda za ta shigo? To ki saurare ni da kyau, daga yau ba na son sake ganin k'afar a madafar nan in har aiki na ne, in ba haka ba kuma zan ci uwar ki a gidan nan sannan na sa mai gida ya yi waje da ke, kinji ni ko?"
Kai Uwani ta d'aga alamar ta ji, da hannu ta mata alama tace "Fitar min daga nan, k'azama kawai 'yar matsiyata."
Kasancewar Uwan irin mutanen nan ne masu jin zafin magana, wanda da ka zage su yafi sauk'i ka yanke su da wuk'a, hakanne ya sa ta fito tana kuka tana jin k'una na kalmar 'yar matsiyata da ta yi da cewa za ta ci uwa ta, ta na nufowa falon Khadija ta tsinkaye ta, dan haka ta tashi da sauri ta nufe ta, sai da ta rumgume ta a jikin ta ta fara tambayar ta lafiya? Cikin kuka ta ke fad'in "Aunty amarya ce tace wai kar na sake shiga madafa in ta na aiki."
Shiru Khadija ta yi tana sauke huci kafin ta d'ago Uwani daga jikin ta tace "Haka ta fad'a mi ki?"
Kai kawai ta d'aga mata, d'orawa ta yi da "Shikenan Uwani yi hak'uri, yanzu ina indomien da na saki dafawa?"
"Ta na can ta zube." Ta fad'a tana share hawaye da hijabin ta, da k'arfi tace "Ta zube kamar ya?"
"Lokacin da ta mareni ne faranti ya sub'uce a hannu na ta zube."
Da k'arfi ta dafe k'irji tace "Mari kuma? Ta mare ki fa ki ka ce?"
Kai Uwani ta d'aga alamar eh, share mata hawayen fuskar ta ta yi tace "Wuce d'aki Uwani ina zuwa, zanji dalilin marin ki, in ba ta san darajar mutane ba ni na sani."
Za ta wuce madafar Uwani ta rik'o hannun ta tace "Dan Allah aunty Khadija ki yi hak'uri, na yafe mata wallahi, ba na so saboda ni ku samu matsala."
Fincike hannunta ta yi tace "Uwani kin tab'a ganin b'acin rai na?"
"A'a." Ta fad'a har da girgiza kai, "To ki wuce d'aki kamar yanda na ce." Ta na fad'a ta nufi madafar a matuk'ar hassale, daidai lokacin kuma mai gadi ya bud'e k'ofa da motar Usman da ta motar Ashir ta danno ciki, Ashir na kusa da gidan ya ga motar usman, dan haka ya kira shi ya fad'a mi shi ya na tare da Bilal dan haka ya juyo su ka dawo.
Khadija kam na shiga ta samu Haseenah ta wanke naman zabbi ta zuba a tukunya za ta kunna wuta, sai da ta tsallaka indomie da ke zube k'asa kafin ta isa gare ta, cikin gadara ta tsaya bayan ta tace "...
_Wata yau za ta gane kuren ta fa._π
*Allah ka sa mufi k'arfin zuciyar mu.*
21/01/2020 Γ 13:34 - πππ: ππππππππππ
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*14*
"Haseenah, Uwani ta fad'a min abin da ya faru, kuma har ta fad'a min ma wai kin mare ta, shin hakane?"
Juyowa Haseenah ta yi cike da rainin wayo tace "Ki cire wai, gaskiya ne abin da ta fad'a, ko za ki rama mata ne? Sai ki tabbatar min yar aikin gida tafi matar gida."
Wani murmushin gefen labb'a Khadija ta yi kafin tace "Ko kinsan kin mana b'arin abincin da yarima zai ci?"
Ba tare da ta juyo ba tace "Ban san wani yarima ba a gidan nan, sai Bilal kawai, wanda na ke da tabbatacin ba shi kad'ai bane yaron da zai rayu a gidan nan, k'annan shi na nan zuwa duniya nan gaba kad'an."
Wata dariya Khadija ta saki har da rik'e ciki kafin tace "Nagode Allah da ki ka iya tuna Bilal shine babban yaron da ya fara zuwa duniya kuma a gidan nan, hakan ya tabbatar min da mai hankali na ke zaune."
Kallon ta ta yi sosai tace "Kasancewar Bilal d'an farko a gidan nan ba shi ke nuna zaifi sauran yaran da za su zo daraja ba, kamar yanda jimawar mahaifiyar shi a gidan bai sa matsayinta yafi nawa ba, dukan mu mata ne kuma matan Usman a gidan nan, aljanna ki ke nema haka nima ita na ke nema."
Juyawa ta yi ta d'auki wuk'a hakan ya sa Khadija fizgo wuyan rigar ta da ko hijabi babu a jikin ta, sosai ta shak'e ta tace "Dama abu d'aya na zo fad'a mi ki, Uwani ba wai yar aiki ba ce a gidan nan kamar yanda ki ka d'auka, kuma mai gidan ma yasan da haka, ko shi bai isa ya mata abin da ki ka mata ba, dan haka ya zama na k'arshe da kalma marar dad'i za ta shiga tsakanin ki da ita bare duka, na yarda ki mata fad'a idan har ta yi ba daidai ba, amma banda cin zarafi a ciki, ki kiyaye nan gaba."
Sakin rigar ta ta yi za ta fita kawai Haseenah ta ja tsaki tace "Idan shi tsoronki ya hana ya mata magana, ni nan Haseenah zan iya, kuma ki sani shigowa ta gidan kamar shigowar rahama ne da sauyi."
Murmushi Khadija ta yi tace "Ina fatan dai ki na da kud'in biyan bokan na ki, dan in ba ki shirya ba za ki sha wahala wajen karb'ar gidan nan a hannu na."
Juyawa ta sake za ta fita Haseenah ta kuma cewa"Aikin banza, ai ba boka ba malam wallahi zan karb'i gidan nan, makauniyar banza makauniyar wofi, ai ba a banza Allah ya hana ki idon gani ba."
Wannan maganar ta makauniya ita ce ta tsayawa Khadija a rai, da k'arfi ta juyo ta matso daf da ita tace "Me ki ka ce?"
Yanda taga idon Khadija sunyi ne ya sa ta kasa cewa uffan, lumshe ido ta yi ta bud'e ta sauke su a kan ta tace "Haseenah ina da yak'inin ban tab'a yin fad'a ba tun da k'uruciya ta har zuwa girma na, sai dai ina ji a jiki na cewa fad'a na zai yi matuk'ar muni, dan haka ina so ki kiyaye, ba na so na yi abin da zai b'ata min suna ko kuma zuri'a ta."
Cikin rashin gamsuwa da abin da ta fad'a tace "Wai ke Khadija me ki ke d'aukar kan ki? Mummuna ko me? Akan komai sai kin nuna ke dabance, to ba zan d'auka ba