Showing 54001 words to 57000 words out of 139085 words

Chapter 19 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

ta ga dama ne?"


Murmushi ya yi daga in da ya ke yace "Ran gimbiya ya huce, kawai dai ina tambaya ne."


Cike da rashin kulawa tace "Ka ga ina tuk'i fa, sai munyi magana."


Kasje wayar ta yi ta ci gaba da abin da take, shima kuma d'auko Haseenah ya yi sai dai bai fad'a mata yanda su ka yi da Khadija ba har suka isa ya sauke ta, da d'ar-d'ar ta shiga gidan bikin ta na sallama wata bayan wata, cikin sa'a ta hango su Hassana da Husseina da duk sauran yan uwan tare da Hajia sarakuwar su zaune, da azama ta isa can ta zauna su ka gaisa, Rabi'a ce ta fara tambayar ta da "...




*Ku yi hak'uri masoya abisa jinkiri na, hakan na faruwa ne sakamakon al'amura da su ke sha min kai na.*πŸ‘
04/02/2020 Γ  21:00 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘






_SAMIRA HAROUNA_




*Littatafan marubuciyar*




*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._




*SADAUKARWA GA*


_MATAN FARKO_πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)*




πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›




```Fatan alkairi masoya```
*πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S*
(GIDAN ZAMAN LAFIYA DA AMANA INSHA ALLAH)πŸ€œπŸ€›




*SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!*




*INA JIGA JIGAN MASOYAN πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S WAD'ANDA BASU DA TAMKA A WAJENMU????? DUK WANDA YAKE TARE DAMU A CIKIN GROUPS D'INMU TO MUN TABBATAR K'AUNARMU CE TASA KUKA KASANCE TARE DAMU, MUNA YABAWA KUMA HAR ABADA BAMU DA KAMARKU WALLAHI,πŸ‘ DUK DA HAKA DAI GA LOKACI YAZO, KUMA DAMA TA SAMU NA TABBATAR MANA DA KUMA NUNA MANA HAK'IK'ANIN K'AUNAR DA KUKE MANA,πŸ‘‡*




Kunsan cewa k'ungiyarmu *πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S* suna cikin gagarumin gasa na samun award Wanda *women24 TV WhatsApp group* suka shirya kuma zasu gudanar?


A wannan gasar ne za'a samu k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan fans da Kuma bin k'a'idar rubutu


Dan ki samu damar zabar k'ungiyarmu *πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S ASSOCIATION* zaki iya tuntub'ar wannan lambar 09030159301 Dan su saki a *WOMEN24 TV WHATSAPP GROUP* anan ne za'ayi zab'en k'ungiyar da tafi kowacce k'ungiya yawan masoya


*Women24 Tv*
Ba zabe kad'ai zakiyi ba


Zaki k'aru da abubuwa da yawa kamar haka


*Yanda ake girke girke*
*yanda zaki gyara jikinki*
*yanda zakiyi makeup*
*yanda zaki daura Dan kwali*


Kuma suna shirye shiryen nan na *arewa24 tv* kamar su


*TARKON KAUNA*
*DADIN KOWA*
*KWANA CHASA'IN*
*JAMAI RAJA*
*SAPNE SUHANE*
*GIDAN BADAMASI*
*RUDIN ZUCIYA*
*BAGHYA LAKSHMI*
*AKUSHI DA RUFI*
*AUDIO NOVEL*
*HAUSA NOVELS*


Kada ki manta da ranar zabe inkin shiga group d'in ki zaba *πŸ‡ΈπŸ‡¦ZAMAN AMANA WRITER'S* tanan ne zaki iya nuna mana irin sonda kuke ma k'ungiyarmu da littattafammu


Allah yabar zumunci🀝😍πŸ₯°πŸ’‹




_Bismillahir rahamanir rahim_




*19*






"Haseenah ke kad'ai ki ka taho ne?"


Da kunya ta kalle ta tace "A'a, shi ya kawo ni ai, da tare da aunty Khadija zamu taho, to kuma bansan tafiyar ta ba."


Ai kuwa abin da ta fad'a ya samu shiga sosai, hakan ya sa Hassana cewa "Amma yasan za ku taho tare?"


"Eh ya sani, shi yace ma mu taho tare tunda safe."


Rabi'a ce tace "Amma kuma dan rashin mutumci shine ta taho ta baro ki? Lallai ma matar nan, kullum iskancin ta k'aruwa ya ke."


Husseina ce tace "To ba ita ke da mota ba, kinga kuwa dole ta yi yanda ta so."


"Hum." Cewar Hassana, cike da wauta Aziza tace "Wallahi kema kar ki yarda ya siya mi ki ko moto ne, dan ba za ki zauna ta na mulkar ki ba."


Hajia ce ta kalli Haseenah tace "Ki shiga wajen mai jegon mana ku gaisa."


"To Mama." Ta fad'a ta na mik'ewa, cike da dattako Hajia ta sake cewa "In ce dai ya baki abin da za ki kaiwa mai jegon?"


'Yar dariya ta yi tace "Eh Mama, tunda safe ma ba bamu dukan mu."


Hajia na ganin wucewar ta ta kalle su dukan su tace "Yanzu mi ye anfanin haka? Wannan yarinyar yaushe ta shigo cikin ahalin ku da har ku ka yarda da ita haka? Mi ye Khadija ba ta mu ku ba a rayuwa da har ku ka butulce ma ta haka? Dukan ku fa mata ne, kuma Rabi'a ce kad'ai ba ta da abokiyar zama a ciki, ke kan ki Aziza da ki ke wata banzar magana na ga saurayin da ki ke so ai mata gare shi, shin idan aka mu ku haka za ku ji dad'i? Nace za ku ji dad'i idan aka mu ku haka? Ba za ku ji ba kenan? Shine kuma ku ke wa wata rashin kunya wacce ta mu ku alkairin da ki shi d'an uwan na ku bai mu ku kamar shi ba, shi d'an uwan na ku kunsan yanda ya ke d'aukar ta da kuma matsayin ta a wajen shi? Ku kan ku da akwai mutumci ai Khadija tafi k'arfin komai a wurin ku, wallahi ta wuce cin mutumci da cin zarafi, ko ba komai mafi soyuwar abu a zuciyar d'an uwan ku shine d'an wannan matar da ku ka raina, sannan ina yak'ini akai ko tamtama babu cewar Khadija ma tafi soyuwa a zuciyar d'an uwan ku, idan kuma kun shirya rasa shi ne to dan Allah ku ci gaba da mata rashin kunya, ni dai na fad'a mu ku gaskiya a matsayi na na uwa, kuma ke Aziza."


Hajia ta fad'a ta na nuna Aziza da hannu kafin ta ci gaba da "Kar na sake jin bakin ki daga yau in har su na maganar su, tunda ke kinfi kowa butulcia cikin su, Aziza matar nan har kashi da fitsarin ki ta ci kamar yanda ni ma na ci, matar nan ta kwantar da ke a gaban k'irjin ta kamar 'yar da ta haifa, matar nan ta mi ki wanka da hannayen ta ta shirya ki, duk lokacin da mijin ta baya nan ke ce abokiyar rayuwar ta, har rayuwa ta canza mu su ta haifi nata yaron ba ta banbanta ki da shi ba, Aziza sai da aka kai k'adamin da ta ware mi ki d'aki a gidan ta, kinfi kowa sanin Khadija a cikin dangin mu, amma kash ke ce farko wajen juya mata baya, Allah ya kyauta."


Ta na fad'a mik'ewa ta yi daga kan kujerar ta koma wajen wasu tsofi ta zauna, su kam tabbas jikin su ya yi sanyi, sai dai a ganin su duk cikin sharrin Khadija ne, Husseina ce tace "Gaskiyar Hajia, wallahi duk ranar da yah Fodio ya ji maganar nan a bakin mu, to fa kashin mu ya bushe."


Aziza ce tace "To ai dole tunda ta gama da shi, in ba kinibibi ba miye ta ke bashi kowane dare ya na sha da sunan shayi? Har da wasu k'ulallen abubuwa kamar kashin shanu kuma bai kai kashin shanu ba na ga ta na sakawa."


"Da gaske ki ke Aziza?" Cewar Rabi'a da duk cikin su tafi tsanar Khadija tun lokacin da ta nemi kud'i wajen d'an uwan ta, ta rik'e abun sosai a zuciyar ta ya na d'awainiya da ita har yanzu, Aziza ce tace "Wallahi kuwa, a madafa ta ke aje abun, kuma ko a gaba na sakawa ta ke."


Cike da makirci Rabi'a tace "Hakan ma wata hujja ce da za ta tona ta, Aziza ya za ayi ki d'auko mana wannan abun?"


Cike da rashin tsoro tace "Abu mai sauk'i, in dai har yanzu ta na aje shi in da ya ke ai zan gan shi."


Hassenah na shiga ta samu Khadija tsakiyar gado da manyan mata sai hira suke ana dariya, cike da fargaba ta yi abin da ya kai ta ta juyo ta fito, wajen su Hassana ta koma su ka ci gaba da hirar su, Khadija kuma na ganin fitar ta ta kalli k'awar ta Hajia Turai DubaΓ― tace "To kinga amaryar ta wa da har yanzu ki ka kasa zuwa ki gani."


Waro ido Turai ta yi tace "Ita ce kishiyar ki?"


"Eh." Ta fad'a har da dariya, hararan ta ta yi tace "K'arya ki ke wallahi, wannan ce za ta zama amaryar ki? Haba Khadija, ko da dai nasan halin mutanen mu ba kunya ne da su ba, amma taya Usman zai had'a ki da yarinyar can?"


*Umma* Khadija ta kalla tace "Ke da ki ka tabbatar sai ki fad'a mata gaskiya."


Umma ce ta d'ora "Wallahi ita ce kishiyar ta."


"Bala'i." Cewar Hajia Turai cikin d'aga murya bugu da k'ari Allah ya hore muryar sosai, kasancewar irin mutanen nan ne masu ido bud'e da basu tsoron tashin hankali ko hargowa ya sa ta shiga aibata Haseenah ta na shammace ta, tun Khadija na cewa ta yi shiru dan Allah har ta yi banza da ita, hakan kuma da akayi duk a ido da kuma kunnen 'yar k'anwar mahaifiyar Usman (cousine d'in shi), ba ta b'ata lokaci ba wajen fitowa ta fad'awa Hassana da dama akan maganar Khadija suke, amma sai da ta keb'e ta gefe d'aya, Hassana ba ta tanka ba har lokacin da Mariya ta kira Haseenah wai idan ta na gida za ta zo ta kawo mata sak'on wajen malam, nan Haseenah ta fad'a mata ba ta gida amma za ta zo yanzu ita ta karb'a, sallama ta mu su tace ta tafi gida ba ta jin dad'i, ta na samun adaidaita ta wuce gidan Mariya, magani ta bata kala har uku wanda in dai ta yi aiki da su to ta tabbatar mata Usman zai zama na ta, d'aya za ta shafa a marar ta ne ranar kwanan ta ya sadu da ita, d'aya za ta saka a abin sha da ya danganci koko, fura ko kunu, sai kuma d'aya da za ta zuba a k'ofar d'akin Usman ya tsallaka, cike da farin ciki da jin ta yi nasara ta baro gidan ta nufi gida.


Fitar ta ba jimawa Khadija ita ma ta wuce gida dan kama aiki, nan fa su Hassana suka shirya abin da za su fad'awa Usman tare da shirya yanda za su yi.


Bayan sallah isha'i Usman na zauna a majalisar su ana hirar duniya kiran Hassana ya shigo wayar shi, sun tsara ita ta kira shi ne saboda ita ce babba da ke bi mi shi, ya na d'auka ta gaishe shi cikin ladabi ya amsa, cikin taushin murya ta d'ora da "Yah Fodio dama ina son yin magana da kai ne, sai dai bansan ta yanda za ka fahimce ni ba."


Kamar ya na gaban ta ya yi murmushi yace "Ki tak'aita mana wahala to, ki fad'a a yanda zan fahimta."


Gaban ta ne ya sake fad'uwa kafin ta dake tace "Yah Fodio dama abin da ya faru d'azu wajen biki ne gaskiya bai ma kowa dad'i ba, Khadija dai ita ce babba kuma za ta iya rik'e ragamar gidan ka ko ba ka nan, amma abin da su ka yi d'azu da k'awayen ta gaskiya bai dace ba, dan wannan salesalen tayar da masifa ne, wallahi saida mu ka iza k'eyar Haseenah ta koma gida saboda ran ta ya sosu."


Kasanvewar ya na cikin mutane ya sa matsa gefe da su yace "Me ya faru? Me Khadija ta yi ita da k'awayen ta? Hassana ba na son masifa da tashin hankali ke kin sanni."


Cike da tabbatarwa tace "Wallahi gaskiya na ke fad'a ma ka, a d'akin *Zaliha* fa su ka zauna suna ta shammatar Haseenah su na zagin ta ta uwa ta uba, idan kuma ba ka yarda ba ka tambayi *Nana* (cousine d'in su) za ta fad'a ma ka gaskiya, musamman ma wannan k'awar ta ta mai ido tsaye Hajia Turai."


Ba wai rantsuwar da ta yi ba ce ya sa ya yarda sai anbaton sunan Hajia Turai da ta yi, matar ba ta da wata d'abi'a da zai ce ba ya son mu'amular ta da matar shi, sai dai irin matan nan ne da masu da kimtsi, komai ya zo bakin ta fad'a ta ke sannan ba ta tsoron bala'i da mace kl namiji, hakan ya sa ma har yanzu ta ke zawarci babu mijin aure sai duniyar ta da ta ke ci da tsinke, nisa da tunanin da ya yi ne ya sa ya kashe wayar bai ma san ya kashe ba, zunbur ya mik'e ya fad'a motar shi ya nufi gida.


Tsaf Khadija ta gama shirya komai ta aje a muhallin shi ta shiga wanka, jin babu motsin ta ne ya sa Haseenah tabbatarwa yanzu ta na wajen shiri, ta falon ta ta shigo na shi falon cikin sand'a da rashin gaskiya, kai tsaye k'ofar uwar d'akin shi ta nufa da k'ullin maganin ta, ta na zuwa ta bud'e ledar tasa yatsu biyu kamar yanda aka fad'a mata, barbad'awa ta yi tare da kiran sunan Usman, sau uku ta zuba kuma a kowane zubawa sai ta kira sunan shi, da sauri ta rufe ledar ta koma falon ta da sauri cikin tsoro, ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke kafin ta dafe k'irji ta yi murmushi, Usman da ke hanyar shi ta zuwa gida ne ya ji wani bala'in sarawar kai kamar an buga mi shi guduma, da k'arfi ya take motar ya tsaya ya dafe kan shi, ya jima a haka sai da ya ji motoci na mi shi odar ya ba su hanya kad'ai ya dawo hayyacin shi ya taka, Khadija na d'aki ta gama duk wani shirin ta ta mik'e ta na d'aura d'an kwali ta ji an bud'e k'ofa da k'arfi, juyowa ta yi dan ganin waye wannan, ganin Usman a wani yanayi da ita dai ba ta tab'a ganin shi a ciki ba ya sa ta d'an kalle shi da mamaki, ganin nufota kawai ya ke ba magana ya sa ta k'ara yin baya da in'i'na tace "A..Abban...Bil."


Ba ta k'arasa ba yace "Khadija akan me ku ka ci zarafin mata ta a gidan biki cikin mutane?"


Mamaki ne fal a idon ta, rarraba ido ta fara yi sai motsa baki ta ke ta na so ta yi magana amma ta kasa, nuna ta ya yi da yatsa yace "To daga yau kar haka ta sake faruwa, idan ba haka ba kuma ran ki zai b'ace, sannan Hajia Turai ba na son ki sake mu'amula da ita, kinji na fad'a mi ki."


Bai jira me za tace ba ya fita daga d'akin ya nufi d'akin Hassenah wacce ta buga tagumi ta na jiran ta jime zai faru, ya na ganin ta da wannan tagumin sai ya ji tausayin ta a tunanin shi akan abin da ya faru ne, ita kuma ba ta ma san me ya faru ba, zaune ya yi kusan ta ya kalle ta yace "Amarya ta, dan Allah ki yi hak'uri kinji akan abin da ya faru, insha Allahu na mi ki alk'awari hakan ba za ta sake faruwa ba."


Cikin rashin fahimta tace "Me kuma ya faru? Akan me ka ke magana?"


Jannyo ta ya yi jikin shi ya na shafawa yace "Idan ke ba ki fad'a min ba ai Hassana ta fad'a min, amma kamar yanda na fad'a mi ki ne ba zai sake faruwa ba in Allah ya yarda."


Shiru ta yi a k'irjin shi ta na tunanin me ye ya faru to? Jin ta yi shiru ya sa ya d'agata daga jikin shi da cewa "Zan shiga wanka, amma ki tabbatar kin fito mun ci abinci ba sai na zo da kai na ba."


Da kai kawai ta ma sa alamar to, fitowa ya yi ya nufi d'akin shi, ya na bud'a k'ofar ya tsallaka ya sake jin gaban shi ya tsinke ya fad'i tare da sarawar kai, hannu d'aya ya saka ya dafe kai ya rintse ido sosai, da k'yar ya iya furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un."


Gaba d'aya jikin shi ne ya yi sanyi a haka ya cire kayan shi, zai shiga wanka Khadija ta yi sallama a d'akin ta shigo, shiru ya mata kamar bai ji ta ba har ta tsaya gaban shi, wani abu ya ke ji a zuciyar shi da bai tab'a jin irin shi ba tunda ya ke da ita, amma da ya ke sabon abu ne sai ya taushi zuciyar shi, a hankali ta rik'e kunnuwan ta cikin taushin murya tace "Ka yi hak'uri *sadauki na*, na karb'i kuskuren da k'awaye na su ka yi, kuma zanyi yanda ka ce da yardar Allah."


Ba fara'a a fuska yace "Ya wuce." Ban d'aki ya nufa ta yi saurin rik'o hannun shi ya juyo, marairaicewa ta yi tace "Ka tab'a wanka da kan ka idan ban taimaka ma ka ba?"


Wani murmushi ya yi kamar mai ciwon baki kafin ya ja hannun ta zuwa ban d'akin, sosai Khadija ta fahimci akwai sabon al'amari a tare da shi, dan har ta gama mi shi wankan nan ba su yi wata magana ba, kamar yanda sai dai ya mata murmushin yak'e kawai, haka ta gama mi shi shiri su ka fito cin abinci, sun zauna kenan Haseenah ta fito ita ma, tunda ya kafe ta da ido bai d'auke ba har ta zauna, murmushi kawai ya ke sakar mata har Khadija ta gama zuba abinci.


Haka aka ci abinci babu wani nishad'i bare jin dad'i, su na gamawa ya nufi wajen Haseenah dan yi mata saida safe, ita ma Khadija shiga ta yi dan ta yi shirin bacci, amma har ta gama ta dawo bai dawo d'akin shi ba, abun mamaki shine har ta d'auki minti ashirin kwance kafin ya shigo, ya na can Haseenah na zuba shagwab'a wai zai tafi ya bar ta, ya na shigowa kashe wuta ya yi ya kwanta, zunbur Khadija ta mik'e da tafarfasar zuciya ta na kallon k'eyar shi tace "Me zan gani haka Abban Bilal?"


Juyowa ya yi a kasalance yace "Me fa?"


"Baya fa ka juya min, me na ma ka haka da zafi? Akan abin da ya faru ne? Dan Allah ka yi hak'uri in dai abin da ya faru ne zai sa ka juya min baya."


Yanda ta yi maganar cikin muryar kuka ya sa k'wak'walwar shi hasko mi shi wacece ita, tashi ya yi zaune ya rumgumo ta jikin shi yace "Shikenan to ya wuce, ki yi hak'uri kar ki min kuka, ba na yi bane da gangan, kawai ba na jin dad'i ne."


Da kuzari ta kwantar da shi akan gadon tace "Kwanta to na ma ka tausa."


Cire mi shi rigar shi ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login