Showing 6001 words to 9000 words out of 139085 words
Chapter 3 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
a hannun shi, amma fa duk da haka sai mun d'an k'ara da malamai, ko ba komai su tayaki da addu'a dan ki samu bakali a wajen shi."
Tashi ta yi tsaye tace "Shikenan aunty Mariya, yanzu wannan kud'in ma ki rik'e a fara wani abun da su, yau ko gobe zan sa ya zo sai na samu kud'in, amma kar ki bari mama ta ji, kinsan halin ta yanzu sai tace ba ta yarda ba."
"Ni? Ina zan fad'a mata, ba ki ga sai da ta tashi ba ma na fad'a mi ki."
"To ni zan tafi su Zeinab na jira na."
"Sai kun dawo." Ta fad'a ta na bin ta da kallo.
*Allah ya fidda _Delu_π daga rogo.*
β©β©β©β©β©β©
Khadija kam a wajen bikin suna can har yamma, sai da su ka gama zubin da suke na k'awaye kafin su ka fito tare da Kaltume, motar ta su ka shiga ta bata wasu harkokin, kamar yanda ta san Khadija farin sani, ba ta anfani da kowane irin garin magani, musamman wanda za ace ayi matsi da shi, ta na sallamar ta ta fita daga motar ta rufe tace "Sai kin zo k'awata."
Kaltume ce tace "A'a k'awata, gaskiya ba na so na zo gidan ki yanzu, na fi so sai an fara shagulgulan bikin nan, lokacin na k'ara had'o mi ki wasu kayan."
Dariya Khadija ta yi tace "Ke fa muguwa ce, wato kullum burin ki kiga bawan Allah nan ya na gasa min aya a hannu ko? To daga wannan da na karb'a sai amarya ta zo ta haihu, idan za ta yi arba'in sai mu shirya tare."
Cikin d'aga murya Kaltume tace "Ina, ana babbak'ar gwiwa wa ke jiyo k'aurin zomo, ai dole yarinya ta gane da banbanci wallahi, wanda ya sa ta shigo gidan Khadija ta Usee, shi zai sa ta gane Khadija ta mata nisa na har abada."
Cikin dariya Khadija tace "Dan Allah k'awata ki ragawa yarinyar nan, har yanzu fa ba mu san ta ba bare mu san da me za ta shigo gidan ita ma."
Cike da gadara da tabbatarwa tace "Ai ko ni Kaltume za ta d'aura a k'ugun ta taje dani gidan, wallahi na riga da na bawa Khadija sirrin da za ta mata rata mai tsayin gaske."
"Na yarda, yanzu dai sai anjima, sai munyi waya ko?"
"To ba damuwa k'awata, ina k'ara fad'a mi ki dai, dan Allah banda nuna kishi a fili, ayi komai cikin kissa k'awata, ban da matsala da ke ta wannan fannin , amma kishi masifa ne wallahi."
"Hakane k'awata, kuma insha Allah zan kiyaye, nagode sosai."
"To, ki kula da kan ki."
"Kema haka."
Da haka ita ma ta shiga ta ta motar ta bar wajen, Khadija kuma ta na zuwa gida ta samu wannan kayan arzik'i, gidan su ta kira ta fad'a mu su, zuwa bayan sallah magrib kam sai ga maman ta da matan yayyun ta sun zo ganin kayan, hotunan su ta d'auka ta turawa k'awayen ta dan su gani suma ba sai sun zo ba, anan ne ma har su ka yi magana da maman ta a kan kayan d'aki da za ta canza, mahaifiyar da kan ta ta d'auki alhakin yi mata odar su daga k'asar waje, dan itama ta na so ta kece raini.
Sun fito dan tafiya Usmane ya shigo gidan, da gudu Bilal ya k'arasa ya rumgume shi, har k'asa ya duk'a ya gaishe da mama, mama ce tace "Kai yanzu da girman ka har ka ke wani mak'ale shi kamar yaro."
Hararan wasa Bilal ya aika mata yace "Kaji tsohuwar nan, ke ma fa idan na je gidan ki har d'auka ta ki ke."
Dafe k'irji ta yi tace "Kaji min sarkin sharri, ni kuma ina zan iya d'aukar ka? Ka fad'i abin da hankali zai d'auka mana."
"To ai dai Abba na ne ko." Ya fad'a ya na k'ara sarkafe wuyan Usman da har yanzu ke durk'ushe, ita ma kuma cewa ta yi "Ni ma kuma d'ana ne ba, kaga kuwa ba zan bari nima ka karya min yaro ba."
A hankali Usman ya kalli Bilal ya d'an janye shi daga jikin shi yace "Mama ta fika gaskiya, kowace uwa d'an ta ta sani, dan haka kowa ya je wajen maman sa, kai ma jeka ga ta ka can."
Kallon shi Bilal ya yi yace "Lallai ma Abba, za ka nemi ne ai har in da na ke, kafi kowa sanin cewa ni ne bugun zuciyar ka."
Wajen Khadija ya nufa ta d'auke shi saboda k'arfin hali duk da girman shi, mama kuma kallon Usman ta yi ta k'ara da "Mun ga kaya fa, a gaskiya sunyi sosai, sai dai kuma kayan kamar sunyi yawa, Allah ya k'ara bud'i na alkairi."
Ba tare da ya d'ago ba yace "Ameen ameen Hajia, ai ni ne da godiya, Allah ya saka da alkairi, Allah ya k'ara girma da lafiya."
"Ameen ameen." Mama ta amsa kafin Khadija ta d'ora da "Tofa, yanzu za ka fara godiyar ko?"
D'ago kai ya yi ya kalle ta yace "Ke kuma ba kya so ina godiyar ko?"
Hannaye ta d'aga tace "Allah ba ka hak'uri, ga ka ga su."
Mama kam wucewa su ka yi suna fad'in "Sai da safen ku."
Bilal da ke bayan Khadija ne ya d'aga musu hannu yace "Sauka lafiya, ko k'ofa ba zan raka ki ba bare ki sa ran samun na adaidaita."
Usman ne ya juyo ya kalle shi yace "Haihuwa maganin takaicin duniya, sai da ta haife ni kafin kai ma ka zo, dan haka da kai na zanyi dakon mahaifiyar ta har makwancin ta."
Dariya kawai su ke har su ka isa k'ofar gidan, cikin shagwab'a Khadija tace "Amma fa kar ku jima, ku yi sauri ku dawo."
Kafad'a ya mak'ale yace "Na k'i d'in."
Hararan shi ta yi tace "Za ka dawo ai ka same ni, zan kama ka a hannu."
Ba tare da ya bari mama ta gani ba ya mata gwalo yace "Ki kama ni d'in, ba zan shigo ba sai kinyi bacci."
"Bayan na rufe gida na ba." Ta fad'a kamar mai son tabbatar masa da za ta iya, haka dai ya d'auke su su ka wuce, mama ta so ya yi zaman shi su k'arasa titi su hau adaidaita, dan dama ko da *Naseer* ya kawo su sun fad'a mi shi za su koma da kansu, amma bai bari ba sai da ya kai su har k'ofar gida ya dire su, nan ma sai da ya fito daga motar ya sake mu su sallama kafin ya yi gaba, ya na kan hanyar shi kuma kiran amarya Haseenah ya shigo wayar shi, kashe kiran ya yi sannan ya sake kira da kan shi, ta na d'auka cikin ladabi tace "Amincin Allah ya tabbata a gare ka adali na."
Cikin jin dad'i yace "Kema haka, ya amarya ta take?"
Cikin siririyar murya tace "Da dad'i ba dad'i, amma daga yanda na ji karsashin muryar ka sai ya sa na ji wata tabbatacciyar lafiya na shiga jiki na."
Murmushin jin dad'i ya yi yace "Allah na gode ma ka da ka sa Haseenah za ta zama tawa, kalaman ki su na fasa min kai na, shi ya sa ba na gajiya da sauraron ki, yanzu fad'a min, ko zan iya sanin in da amarya ta take? Dan ina jin hayaniyar ababen hawa a in da ki ke."
"Wallahi Abban Bilal mu na wajen mai d'inki ne, amma yanzu za mu koma gida."
"To in dai hakane ki ce kawai na zo na mayar da ku gida?"
"A'a, ba na so na shiga lokacin aunty na gaskiya, kawai ka bar shi zamu koma da kan mu."
Dariya ya yi yace "Allah sarki Haseenah baiwar Allah, a gaskiya ki na birge ni sosai ta yanda ba kya so a takura yer uwar ki, amma duk da haka ki bari zan zo na kai ku gida, dan dama ban shiga gida ba."
Cikin murmushi tace "Yanda ka ce haka za ayi ranka shi dad'e."
"Ina nan k'arasowa nan da d'an lokaci da zaran kin fad'a min in da ku ke."
Tsaf ta kwatanta mi shi in da su ke, sai da ya wuce gidan shi kafin ya d'auki hanya zuwa in da su Haseenah su ke, hak'ik'a har zuciyar shi ya na jin dad'in mu'amula da Haseenah, duk da ta na da k'arancin shekaru amma ta na da tunani da hankali kamar babbar mace, uwa uba girman da ta ke ba shi da kuma matar shi, hakan na faranta ran shi sosai, shi ya sa yake ji baiyi zab'en tumun dare ba, za ta girmama matar shi sannan ta darajanta yaron shi da yan uwan shi, sannan ya na ji cewar za su zauna lafiya ita da Khadija, dan dukan su babu mai matsala a cikin su, dan da matsala ke sa a k'ara aure, to da shi da k'ara aure sai dai in an had'a shi da matan aljanna, amma Khadija ta gama mi shi komai a rayuwar duniya, lokaci ne idan ya yi ba makawa sai anyi.
*Kallon kitse ake wa rogo*
Da isar shi ya kira ta suka fito, yan mata uku ne su ka fito daga cikin shagon, kusan dukansu da ledoji a hannu, haka kuma dukan su babu mai hijab a ciki, dogayen riguna ne a jikin su sai kallabin rigar da suka yane kan su da shi, siririyar cikin su ya kafe da ido har ta bud'a gidan gaba ta shiga da murmushi a fuskar ta, sauran ma shiga su ka yi suka zauna, kallon shi ta yi tace "Sannu da zuwa adalin miji."
Da murmushi yace "Barka da fitowa adalar amarya."
Tayar da motar ya yi su ka fara tafiya...
*A samu a addu'a.*
_Duk mai son shiga grp d'ina dan samun littafi kai tsaye ya tuntub'i wannan mutanen._
*Mamienmu.*
*My Heenat.*
*My BK.*
*Ma chΓ©rie Hakeema.*
*Momyn Dady.*
30/12/2019 Γ 12:50 - πππ: ππππππππππ
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*5*
Hira su ke ta kwasa shi da k'awayen ta, Haseenah kam dariya ce ta ta, a haka dai su ka isa k'ofar gidan su Haseenah da ke unguwar *Arène da lute*, a tare su ka fita daga motar su ka rufe a tare, sauke gilashi ya yi ya kalli k'awayen yace "To Hajia *Zeinab* saura kud'in taxi ko."
Dariya k'awar ta yi ta juya ido tace "Ina fatan ka na da canji dai?"
"Akwai canji mana, mai sana'a da mata ai baya rasa yan matsabbai."
Dariya su ka sake yi kafin ta kalli Haseenah tace "To ki biya shi, daga baya ni sai na biya ki."
Da sauri Usman yace "La la la, ke dai kawai ki ce ba ki niyyar biya na ba, dan haka na yafe kawai."
Kallon shi ta yi tace "Oho, ashe kud'i na ne za ka iya amsa."
Dariya ya yi yace "Shikenan dai magana ta wuce tunda na yafe, yanzu sai da safen ku."
"Sai da safe." Su ka fad'a su na nufa na su gidanjen da ke unguwar, kallon Haseenah ya yi yace "Ki shiga gida, ba na so k'urar nan na tab'a min ke fa, sai munyi waya."
Cike da rausaya tace "Angama ranka shi dad'e, sai munyi waya. "
Gida ta shige ita ma kafin ya wuce na shi gidan shi ma, ya na zuwa ya sa mai gadi ya rufe gidan gaba d'aya dan ya shiga kenan, tun a k'ofar falo Khadija ta tarbe shi su ka yi cikin d'aki, (to ni wanka ma tare su ka yi shi ko kuwa ita ce ta mi shi oho), amma dai a tare su ka fito kuma suka shirya, kai tsaye wajen cika ciki su ka nufa, tun da ta bud'a kwanon ta d'auki k'aramin faranti ya zura kai cikin kwanon ya na fad'in "Me aka dafa mana yau *Nana*?"
Ba tare da ta kalle shi ba tace "Kan kare."
Yamutsa fuska ya yi yace "Kuma ki na ganin zaiyi dad'i?"
Ita ma yamutsa fuska ta yi tace "Um; ba tabbas, amma ka fara d'and'ana mana tukuna."
Nuna kan shi ya yi da yatsa yace "Ni? To na k'i, ki bawa d'an ki ya fara lasawa."
Murmushi ta yi tace "Ka na so ne na rasa d'ana?"
"Oho, ni ne kenan banda mahimmanci? To nima haihuwa ta aka yi, kuma yanzu haka da iyaye na za su ji me ki ka fad'a, to da kinga yak'in duniya na uku ganin idon ki."
Tunda ya fara magana take dariya har ta gama zuba mishi ta aje farantin gaban shi, janyo kujera ta yi ta zauna daf da shi yayin da Bilal ya zauna a k'afafun Usman, dukansu hannayen su suka saka suna cin abincin, dan a d'abi'ar Usman yace Allah ya hore mu su yatsu har biyar saboda su yi anfani da su ne har wurin cin abinci ba, da hakane su ka saba da ci da hannu in ba abin da ya zama dole aci da cokali ba, su na cinyewa Khadija ta turo baki gaba tace "Duk kun fini k'atuwar loma, kuji fa kun cinye abincin kai da yaron ka."
Kallon Bilal ya yi yace "Yarima ka ji me ta ke fad'a, ka duba ka gani wa yafi k'aton ciki a duk cikin taron nan."
Tsaye Khadija ta mik'e tace "Kai ka fi mu cin mai yawa, dan haka zan k'ara kuma banda kai za mu ci."
"Tab'dijam, na kawo abincin, na sarrafa shi, na dafa shi, kuma ace ba zan ci na k'oshi ba, lallai ma yau za mu tara yan kallo a gidan nan." Ya k'arashe maganar da juya baki, hannu Khadija tasa ta d'auki kwanon miya ta na fad'in "Ai dai abinci ba zai ciyu gaya ba, ni kuma zan iya cinye naman ciki na kuma tsoma bredi a miyar."
Shi ma jan kwanon shinkafar ya yi yace "Ni ma kuma zan iya zuba man gyad'a a shinkafa ta, haka zan iya saka sardine (kinfi gwangwani)."
Bilal ne ya katse su da "Kai, Kai, wannan rigimar ta ku wata rana za ta ja min ciwon yunwa, kaga Abba kawo nan."
Karb'ar kwanon ya yi ya aje ya nufi Khadija ya karb'i kwanon miyar ya aje sannan yace "Yanzu kowa ya d'aga min rigar shi na ga tunbin shi sai na ga wanda ya fi k'oshi."
Dukan su a tare suka turo baki gaba da rumgume hannaye a k'irji, Usman kam har da k'arawa da mak'ale kafad'a yace "Um, um."
Murmushi Bilal ya yi ya rumgume kwanukan ya na fad'in "Dan haka ni kad'ai zan ci abincin nan, kuma na ga mai ja a maganar yarima."
"To shikenan, yanzu ga nawa." Cewar Khadija ta na d'aga rigar ta sama, hannu ya sa ya shafi cikin ta ya marairaice yace "Ayya! Sarauniyar uwa ta ba ta k'oshi ba har yanzu."
Kai ta girgiza ma sa kamar za ta fashe da kuka, Usman ma haka ya d'aga ya shafa cikin, shima a marairaice yace "Sarki ma bai gama k'oshi ba, to ku zo mu ci tare."
Matsowa su ka yi Usman ya kalle ta yace "Kinyi sa'a fa yarima ya ceceki, da gay kin sha miya."
"Kai ma da ka ci gayan tuwo." Ta fad'a har da masa gwalo, cewa ya yi "Amma dai na san ba ki jin ana cewa azo asha miya, sai dai ace azo aci tuwo."
Yatsa Bilal ya d'ora a labb'an shi yace "Ya isa haka to, aci abinci ba magana ba."
Shirun kam su ka yi su ka saka hannu a abincin da ya zuba su ka ci gaba da ci, daga nan kuma kallo su ka tab'a kafin su ka kwanta da fatan wayewar gari lafiya.
Tunda asuba Usman da Bilal su ka wuce masallacin da ke manne a jikin gidan, bayan sun dawo kuma kowa d'akin shi ya nufa, duk da Khadija ta ji dawowar su amma ba ta je in da Usman ya ke ba, saboda ta san abin da zaiyi yanzu ba ya son hayaniya da takura, sai da ta ga k'arfe *07:00* ta buga daidai ta tashi daga sallaya ta nufi d'akin, da sallama ta shiga ta same shi zaune a kan sallaya, d'ago kai ya yi tare da amsa sallamar ya na rufe Qur'anin hannu shi ya aje gefe, zaune ta yi k'asa kusan k'afar shi cikin ladabi tace "Antashi lafiya *babban mutum*?"
Cikin kafeta da ido yace "Lafiya lau na tashi, fatan kema haka?"
Da murmushi tace "Lafiya k'alau na ke tun da dai kun tashi lafiya."
"Masha Allah, Allah abin godiya."
Kallon shi ta yi cike da kunya tace "Zan shiga madafa ne dama, shi ya sa na ke so na ji abin da miji na ya ke sha'awar ci dan na sarrafa mi shi."
Cike da kallon bege yace "Zab'in ku shine zab'i na, za ki iya dafa abin da ran ki ya ke buk'ata."
"Ba na da wani zab'i da ya wuce na ka, duk abin da ran ka ya ke so shine nawa ya ke so."
"To in hakane sai ki tambayi yarima dan ya raba mana wannan gardamar kamar yanda ya saba."
Cikin shagwab'a tace "Shi ma kan shi yarima zab'in mu shine na shi, dan haka a matsayin ka na shugaba kuma ja gaba dan Allah ka taimaka ka zab'a mana abin da za mu ci."
Hannu ya kai ya ja dogon hancin ta ya na fad'in "Kin ganki ko mai wayo, to shikenan yanzu ki je ki samar mana ko da irin wannan wainar da ki ke had'a ta da miyar kayan ciki."
Dariya ta yi tace "Kwad'ai ko? Wato ka ji dad'in ta?"
Kamo hannun ta ya yi ya sumbata yace "Duk abin da hannun nan zai tab'a to ya kan zama mafi soyuwa a gare ni."
"Shikenan to bara na je na fara aikin, tunda har yanzu *Uwani* ba ta dawo ba bare na tsaya jan jiki."
Rik'o ta ya yi yace "Amma dai ban takura ki ba ko?"
Sai da ta waina idon ta tace "Gaskiya na d'an takura da ka k'i fad'a min abin da ka ke so tun da wuri."
Dariya ya yi ita kuma ta mik'e ta juya, tafin hannun shi ya sa ya daki