Showing 66001 words to 69000 words out of 139085 words

Chapter 23 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

Ba na son maganar banza fa kinji ko, daga k'aramar magana za ki wani tasowa mutane, zuciyar ki ta raya mi ki k'arya da gaskiya kawai sai ki zauna akai."


Zunbur ta mik'e tace "Au! Wai zuciya ta ma ce ta raya min kenan? To kamar yanda ba ka son maganar banza haka nima, wallahi Abban Bilal ka ji tsoron Allah kasan cewa za ka mutu."


Maida kallon ga tayi ga Haseenah tace "Ke kuma ki sani duk rayuwar da aka ginata babu Allah a ciki wallahi k'arshen ta munin ta ya na bayar da mamaki, Allah ma shaida ne ban rik'e ki a zuciya ta ba ko kad'an, na so na zauna lafiya da ke mu taru mu farantawa mijin mu, amma na fahimci kin biyo abun ta bayan gida saboda cimma burin ki a kai na, ki sani Haseenah wallahi tallahi da ace zan yi dan na raba ki da Usman, to ina da bokan da idan har ya shiga tsakanin ki da shi wallahi tallahi ba ke ba duk wanda ya zauna tare da ke ma sai ya tsane shi, amma tuna akwai Allah kuma zan mutu ya sa na d'aga mi ki k'afa, amma muje zuwa."


Ta na fad'a ta juya ta koma falon ta, janyo Haseenah ya yi ya d'ora a cinyar shi ya fara bata abincin ya na fad'in "Ki shirya kayan ki, ina tunanin tafiya da ke Dubai a satin nan, dan ba zan yarda na barki tare da matar nan ba a gidan nan."


Duk da a zuciyar ta akwai abin da taji shed'an na raya mata, amma sai ta nuna ta yi murna ta hanyar cewa "Dubai? Ni? Wayyo Allah yaushe? Da gaske ka ke?"


"Um, ki shirya kawai, ina tunanin tafiya nan da kwana biyu zuwa uku."


Haka suka gama cin abincin ya fita ita kuma ta koma d'aki, ta jima ta na waya da Mariya ta na fad'a mata canjin da aka samu, amma ba ta fad'a mata abin da ta ke shirin aikatawa ba har suka yi sallama, su na gamawa Haseenah ta shirya tsaf ta fito, kai tsayz k'ofar fita ta nufa mai gadi ya bud'e mata k'ofa, a lokacin Khadija na madafa ta tsinkaye ta ta fice, aikin gaban ta ta ci gaba da yi ba tare da tunanin komai ba, har ta gama aiki da duk abin da ta ke yi, ta na zaune falo tare da Bilal Usman ya shigo, ta yi mamakin ganin shi a lokacin sosai, shi ma kuma ya na ta kiran Haseenah ne ta k'i d'aga wayar shi duk abin duniya ya dame shi, hakan ya sa ya zo gidan kuma ya na nufa b'angaren ta ya ga k'ofar rufe alamar ba ta nan, shi ya sa ya shigo wajen Khadija, tsaye ya yi a kan ta yace "Na ga yarinyar nan ba ta nan ko kinsan in da ta tafi?"


Wani murmushin ta yi tace "Ni kuma ina zan san in da ta tafi? Ko gaishe ni ka ga ta na yi bare na samu kimar da za ta fad'a min za ta fita."


Wani dogon tsaki ya yi ya sake kara wayar shi a kunne, ta na kururuwa wayar amma ta k'i d'auka, sake maida kiran ya yi hakan ya sa mahaifin Haseenahr d'auka, dama ko da ta je gida da kuka ta isa, ta na zuwa ta k'ara fashewa da kuka wai ita wallahi ta gama auren gidan Usman, anyi tabbaya amma ta k'i fad'a saida aka kira Baban ta ya zo sannan tace "Ni kawai ba zan koma gidan shi ba, wallahi ba na bacci a cikin dare sai a dinga bani tsoro, yanzu kuma kawai..." Kuma sai ta yi shiru, mahaifin ta ne yace "Kawai me?"


Kallon shi ta yi da ido tsakar kai tace "Ba komai, ni kawai ba zan koma ba."


Ta na ganin kiran Usman a waya sai ta ture wayar wai ko sunan ma ba ta son gani, hakan ya sa iyayen jikin su yin sanyi su ka fara tunanin shiga baga ne na kishiya kawai, shine yanzu da ya kira baban ta ya d'auka, saida su ka gaisa cikin mutumci kafin yace ya zo ya same shi gida ya na son ganin shi, ba musu yace ya na nan tafe yanzun, dan shima idan bai ganta ba ba zai iya salun nutsuwa ba, Khadija na kallo ya fita daga gidan da sauri.




Ya na zuwa kam suka tattauna sosai in da Haseenah ke cewa kawai ya sake ta ba za ta koma ba, shi kam yace ba zai iya rayuwa ba yanzun babu ita, dan haka dai aka sasanta mahaifin ta yace ta je gida zai samar mata magani, haka ya d'auko ta suka dawo gida bayan ya bawa Baban ta kud'i a fara mata magani, Khadija na kallo suka dawo suka nufi b'angaren ta, ya jima ya na bata magana da rarrashi kafin ya fita, a gida ma suna tafiya mahaifin ta ya fito ya hau moton shi, bai zame ko ina ba sai *pharmacie salfiya* cibiyar magunguna na addini, da ya fad'a mu su matsalar sun zo ya zo da mara lafiyar da suga yanayin jikin ta, amma tunda ya riga ya zo sai suka bashi wanda ya dace da abin da ya fad'a, amma sunce in har ba ta daina ba to su kawo ta wajen su dan su duba ta, ya na barin nan gidan Haseenah ya wuce kai tsaye, dan suna so su d'auki matakin tunda wuri, Khadija na ganin shigowar shi amma ba ta kawo komai a ran ta ba dan bata nufin kowa da sharri, har falon Haseenah ya ke zaune ya na fad'a mata yanda za ta yi anfani da su, saida ya gama kafin ya bar gidan, Haseenah na ganin fitar shi ta kai magungunan d'aki ta aje, d'ibar wasu ta yi daga cikin wanda za ta yi anfani da su yanzun ta zubar.


Usman kuma na barin nan gidan su ya nufa, Hajia ya fad'a ma halin da ake ciki, ta jinjina al'amarin tare da dogon nazari akai, sai dai zuciyar ta ta kasa yarda cewa Khadija za ta iya cutar da ita, dan da za ta hana ta zaman gidan ai da bata ma barta ta shigo ba, amma dai "Allahu a'alam." Cewar Hajiar, ya na fita Aziza ta taso maganar dan ta na waje ta ke jin wasu maganganun, cike da damuwa Hajia ta fad'a mata yanda aka yi, ke Aziza ki na fitowa sai ki ka kira Hassana ki ka fad'a mata, kafin ka ce kwabo maganar ta karad'e yan uwan mata ana ta caccakar Khadija da maganganun b'atanci.


Yamma na yi Haseenah ta shiga madafa ta d'ora girki, sai bayan magriba ta k'arasa ta yi wanka ta shirya, ko da ya shigo ya yi wanka ya sake kaya ya zauna wajen cin abinci, kallon shi ta yi tace "Bara na kira su aunty Khadija su zo mu ci abinci."


Da ido kawai ya bita har ta fita, jim kad'an su ka shigo tare da Bilal, Khadija ba wai ta shigo bane saboda ta na son cin abinci sai dan gudun matsala, akan cinyar sh ya zaunar da Bilal in da Haseenah ta fara zuba abincin, a faranti d'aya suka fara ci shi da Bilal, amma Bilal na kai lomar farko ya kalli Haseenah ba ko k'yabtawa, da k'yar ya samu ya aika lomar ta gangara cikin shi, Khadija da Usman ma na kai wa suka yi saurin furzo shi waje suna goge baki, haka ita ma Haseenah ta na sawa ta firzo ta na ta faman goge baki, Usman ne ya kalle ta yace "Haseenah me ye haka? Kin d'and'ana girkin nan kuwa kinji?"


A marairaice ta kalle shi tace "...


*Yasin na gaji.*
11/02/2020 Γ  18:31 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘




_SAMIRA HAROUNA_




*Litattafan marubuciyar*




*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._


*SADAUKARWA GA*


_MATAN FARKO_ πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)*




πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›


_*H. UMAR*, mahaifin da ya fi na kowa, ina alfahari da kai Baba na, wannan sadaukarwa ce gare ka kai kad'ai, ka cancanci fiye da ita ma, ka huta ka ju dad'in ka, Allah ya k'ara girma da lafiya dattijon arzik'i, *kut.kut.kut.*πŸ˜‰ kaza._




```Fatan alkairi masoya```




_Bismillahir rahamanir rahim_




*22*




"Wallahi bansan ya akayi gishirin nan ya yi yawa haka ba, ni fa lafiya k'alau na kammala girki na, kuma babu yanda za ayi na yi girki ban d'and'ana na ji yanda ya ke ba, sannan idan ka duba ai haka ba ta tab'a faruwa ba."


Satar kallon Khadija ya yi wacce ta kafe Haseenah da ido ta na murmushi dan ita ta fahimci me take nufi da abin da ta fad'a, girgiza kai ya yi yace "Shikenan kar ki damu, komai ya wuce."


Mik'ewa ta yi duk ta yi kalar tausayi tace "Ku yi hak'uri dan Allah, bara na samo mu ku ko soyayyen k'wai ne ku ci."


Da sauri ya katse ta da "A'a ki barshi kawai, tunda hakane ake so mu zauna, ki kawo mana madara gari da sugar kawai sai mu had'a da farar shinkafar."


Haka kam akayi taje ta kawo ta zuba a kofofi ta had'a ma kowa, ta mik'owa Khadija ta mik'e tsaye tace "Gaskiya ba na cin wannan had'in da dare, zanje na samu wani abu na ci da zai d'auke ni a wannan daren."


Kai tsaye madafa ta nufa, ba ta ji wahalar d'aukar silallan naman dake cikin masuburbud'ar sanyi ba ta had'a sassauk'an miya mai kyau da dad'i, fitowa ta yi lokacin sai Bilal da Baban shi akan salon suna kallo ta zo gaban tebur d'in ta d'ibo sabuwar shinkafar ta zuba a faranti ta zuba miyar, Bilal ne ya juyo ya kalle ta yace "Mummy ni dai na k'oshi."


"Dama bance ka zo ka ci ba." Ta fad'a ta na kai lomar farko, hankali kwance ta kammala ta tashi tace wa su je su kwanta, kallon Usman ta yi tace "Saida safe."


"Saida safe." Ya amsa ya na shafa bayan Bilal, da ido ya bisu har suka b'acewa ganin shi, ya na ganin fitar su ya taso in da ta ci abinci, ya na bud'a k'aramin kwanon miyar ya lumshe ido, cokali ya sa ya d'auko tsokar nama ya jefa bakin shi, saida ya sake lumshe ido ya na taunawa ya na fad'in "Umm, umm."


Da sauri ya d'ebo shinkafar kad'an a wani faranti ya zuba miyar ya dinga turawa saboda gudun kar Haseenah ta riske shi, har ya gama bata fito ba dan haka ya same ta d'akin ta na ta shirin bacci, nan ya fara lulawa da ita wata duniyar, sunyi nisa sosai ya na neman gangara kawai ta raba kanta da shi ta sauko daga kan gadon, ya na kallon ta kamar wasa ta canza kayan jikin ta ta saka hijab, ba tare da ya taso ba yace "Lafiya dai? sallah za ki yi ne?"


Ko kallon shi ba ta yi ba ta nufi k'ofar fita, zaune ya tashi yace "Wai lafiya? Ina za ki je haka?"


"Gidan mu." Ta fad'a ta na fita daga d'akin, da sauri ya sauko shi ma ya zura doguwar riga ya fito, ko da ya fito har ta kai farfajiyar gidan, rik'o ta ya yi yace "Haba Haseenah, ina za ki je da daran nan haka?"


Kallon shi ta yi kamar za ta yi kuka tace "Ka yi hak'uri dan Allah ka barni na tafi gidan mu, wallahi ba zan iya kai safe gidan nan ba, ni kad'ai na san me na ke ji."


A tak'aice dai haka Usman ya yi juyin duniya Haseenah tace ba za ta kwana gidan nan ba, shi kuma a ganin shi abun kunya ne ya kai ta gidan su, a cikin daren nan ya kai ta gidan su wajen Hajia, sam abun bai wa iyayen dad'i ba haka su ka kwana suna jimami, shi ma da k'yar ya dawo gidan ya kwanta, sai dai ba wani bacci ya yi ba saboda Haseenah na nesa da shi, saida asuba da yaje ya tashi Bilal sun dawo daga masallaci ya ke ce ma Khadija "Kinsan yer uwar ki ba ta kwana gidan nan ba?"


Da mamaki ta kalle shi tace "Subhanallah, me ya faru da ita? Ta na ina to?"


Wani murmushin gefen labb'a ya yi yace "Kar ki damu, gari na k'arasa wayewa zanje na d'auko ta, Haseenah za ta zauna gidan nan kamar yanda ke ma ki ke zaune."


K'ala ba tace ba har ya fita, da kan ta ta had'a mu su abin kari suka karya kafin ya fita, daga nan gida ya yi lokacin magana ta gama kewaye dangi Haseenah ta kwana gidan surukanta saboda ba ta son kwana gidan mijin, wannan kuma ba komai bane sai sharrin Khadija da ke son korarta a gidan.


Ko da Usman ya je gidan ya samu iyayen Haseenah har sun zo suma, nan fa mahaifin ta ya nuna ba zai yarda a illata mi shi yarinya ba akan namiji, dab haka yace dole sai an kewaya Qur'ani a gidan, duk wanda ya cutar da wani to Qur'ani ne zai ci shi,πŸ˜‚ (tirk'sahi, Haseenah kin jawo bala'i), da k'yar mahaifin Usman ya rarrashe su ya basu hak'uri yace su bar komai a hannu shi zai d'auki mataki, saboda baya so cin zarafi ko mutumci ya fara shigowa lamarin, sun hak'ura amma sun ce dole a binciki gidan dan ga dukkan alama wani kafi ne a ciki da zai hana ta zama, sun yarda da hakan sosai dan haka ma suka ce zasu tura 'yan uwan Haseenah mata su je su duba.


Hassana da Husseina aka kira suka zo gidan, nan aka fad'a mu su abin da ya faru da wanda zai faru a gaba, gidan Usman suka nufa tare da Haseenah da ta yi shiru ta kasa magana.


Khadija na girkin rana a lokacin ta ga Mariya da kuma *Razina* sun shigo duk da ba ita ce aikin ba, cikin sakin fuska da mutumtawa suka gaisa sosai, ganin za su wuce ciki tace "Ina ga fa ba ta nan, ta fita ina jin."


Mariya ce tace "Eh mun sani, ta na nan ma zuwa yanzu."


"Ahan." Cewar Khadija ta ci gaba da aikin ta, ta na kusan gamawa kuma sai ga Haseenah tare da su Hassana, suma saida su ka gaisa kafin Khadija ta kalli Haseenah tace "Ke haka ake sai ku fita cikin dare babu wanda ya sani, saida safe ya ke fad'a min wai ba kya nan."


Kamar za ta yi kuka tace "Ki yi hak'uri dan Allah." Ta na fad'a ta wuce falon ta.


Kallon su Hassana ta yi tace "Ba ta da lafiya ne na ganta wani iri haka? Ko daga asibiti ku ke?"


Cikin d'age kai Hassana tace "Lafiyar ta lau." Ta na fad'a ita ma ta yi gaba sai Huseeina da ta bi bayan ta, su na shiga Hassana ta zauna kusa da Haseenah ta dafa ta tace "Haseenah, ki fad'a mana gaskiyar abin da matar nan take mi ki kinji?"


Girgiza kai ta yi tace "Ba komai."


"Kin tabbatar?" Cewar Mariya da suka zagaye su, shiru ta yi sai Hassana ce ta kalle su dukan su tace "Ku na ji ko, gaskiya dole a d'auki matakin kare yarinyar nan kafin ta cutar da ita, kunga fa yanzu nuna mana ta yi kamar ba ta san me ke faruwa ba, har da tambayar ko ba ta da lafiya ne kuma daga asibiti mu ke, dan haka Haseenah sai kinyi taka tsantsan sosai."


Husseina ce tace "Gaskiya wannan rashin tausayi da imani ya yi yawa, ace yarinya ko sati biyu ba ta cika ba amma ki na so ki fitar da ita daga gidan, wannan ai zalinci ne, shikenan fa so ta ke ta mayar da ita k'aramar bazawara."


"Haseenah ki na da ciki ne?" Da sauri ta kalli Razina da ta jefo mata tambayar, cikin rashin sani tace "Ban sani ba ni ma."


Hassana ce tace "To ko kin sani kar ki yarda ki bari ita ma ta sani, ko ki na ganin alamu kar ki bari ta gane tunda kinga ta fiki wayo, dan wallahi tasan da ciki jikin ki sai ta kusa kashe ki."


Mariya ce tace "Kisa fa ki ka ce?"


Cike da tabbatarwa tace "K'warai kuwa, ki na ganin ba ta iya wa ne? Wacce suka kwashe shekaru kullum da d'a k'waya d'aya, samun cikin Haseenah fa alama ce ta za ta fara hayayyafa gidan Usman, kinga kuwa dole a d'auki tsatsauran mataki."


"To Allah ya raba mu da sharrin wannan mata mu dai." Cewar Razina.


"Ameen." Su ka ji an amsa daga bakin k'ofa, wa za su gani in ba Khadija ba da kwanukan abinci tsaye, fik'i-fik'i su ka kama da ido cike da rashin gaskiya, cikin takon izza da isa ta k'araso in da suke ta aje kwanukan ta d'ago ta kalle su d'aya bayan d'aya, murmushi ta yi da ya k'ara mata kyau kafin tace "Ina rok'on Allah ya kare ku daga sharrin na kamar yanda ku ka yi fata, wani abu d'aya da na ke so ku gane shine, da ace ina kishi da Haseenah kuma haukan kishi, to wallahi tallahi da miji na bai ma kula ta ba bare har ta had'a kafad'a da ni, da ace za fitar da ita daga gidan nan bayan ma ta shigo wallahi da ba ma zan bari ta shigo ba, dan in ta shigo ai za ta iya yin alfahari da hakan, sannan za ta ga abin da yafi komai daraja a jikin miji na, za ta kwanta akan shinfid'a shi kamar yanda zan kwanta, to miye anfanin barin sai ta shigo sannan na fitar da ita? Ai ba ma za ta shigo ba wallahi da na so hakan, ku ji da kyau."


Ta fad'a ta na kallon su dukan su, ci gaba ta yi da cewa "Idan na yi niyyar mallakar Usman ta hanyar asiri ku sani ina da kud'in da zan iya biyan boka ko da na k'asar india ne, idan har na tashi mallakar Usman wallahi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login