Showing 39001 words to 42000 words out of 139085 words

Chapter 14 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

kayan a gida na?"


Har kas'an zuciya maganar ta ta tsaya mi shi a rai, amma sai ya kawar da kai kawai ya mik'e yace "Zan fita ni sai anjima."


Binshi kawai ta yi da harara, dan yau ita zuciyar ta fal take da tarin k'unci, wani faranti ta janyo gaban ta ta bud'a kwanukan, sai da taja numfashi saboda k'amshin da ya daki hancin ta, ai kuwa zubawa ta yi sosai ta kuma ci ta k'oshi ta ma manta waya girka, dan har ga Allah abincin ya mata bala'in dad'i, ko dan ta na jin yunwa ne oho.


Khadija ma na gama shiryawa sai da ta yi sallah kafin ta cika cikin ta da kayan marmari da yan dubaru, daga nan kuma bacci ta shiga dan a huta ma rai.




Kiran sallah ne ya tashe su duka gidan, Bilal masallaci ya nufa kafin ya dawo ya shirya zuwa makaranta, Usman da kan shi ya zo ya d'auke shi su ka tafi lokacin Haseenah har ta shiga girkin dare.




*Mummyn Sultan*
*Mamienmu*
*My sweet Hawwer*
*My lovely Hawwer*
*Mummyn Ameer & Khairat*
*Sis Alawiyya*
*Sis Fusseina*
*Momyn Rasil*


_Da duk wanda baiji sunan sa ba, zaiji anan gaba insha Allah._
23/01/2020 Γ  13:43 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘






_SAMIRA HAROUNA_




*Littatafan marubuciyar*




*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._




*SADAUKARWA GA*


_MATAN FARKO_πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)*




πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›




```Fatan alkairi masoya```




_Bismillahir rahamanir rahim_




*15*




Haseenah dai a shirye take da samu zuciyar mijinta ita ma, hakan ya sa yau ma abinci ware mu su na su ta yi ta kai falon ta, sannan ta zuba maganin saboda ta na so yau ya ci na uku kenan, Bilal ta k'walawa kira tun daga madafar, hankalin shi ya tafi kan kallon da ya ke a *mbc action*, Khadija da ta fito daga d'aki cikin doguwar riga ta shadda ne tace "Bilal ba ka ji auntyn ka na kiran ka ne?"


Da sauri ya mik'e ya nufi k'ofar ya na fad'in "Banji ba Mummy." Ganin ya nufi k'ofar falon ta ya sa tace "Ta na madafa ina jin."


Da sauri ya nufi can, ya na zuwa ta mik'o mi shi kular abinci tace "Abincin ku kai da maman ka."


Jiki a sanyaye ya karb'a ya na kallon ta da mamaki, haka ya juyo ya fito ya kawo abincin maman shi na zaune, aje kwanan ya yi gaban ta ya d'ago ya fad'a kusan k'afafun ta yace "Mummy abincin mu ne wai inji aunty."


"Abinci kuma?" Cewar Khadija ta na yamutsa fuska, "Eh." Cewar shima Bilal d'in, gyara zamanta ta yi kamar wata hamshak'iya matar shugaba akan kujerar tace "Ka kaiwa mai gadi shi."


Ba musu ya d'auki kwanon ya fita da shi, ya na zuwa ma har ya samu ya na cin na shi abincin, cike da ladabi ya aje kwanon gaban shi yace "Baba *Garba* ga abincin ka."


Da mamaki ya kalle shi yace "Abinci na kuma d'an Alhaji? Ai gashi nan har na kusan kai shi k'arshe ma, ko dai makuwa ka yi."


Da dariya Bilal yace "A'a Baba, wannan Mummy e tace na kawo ma ka."


Jim ya d'anyi kafin ya janyo kwanon gaban shi ya na fad'in "Allah sarki, Hajia ta d'auka ba a aiko min da shi bane ina ga? To ka ce angode ka ji ko, ai ba'a maida abinci ba, ko almajirai na bawa tun da na koshi ma."


Juyawa Bilal ya yi Garba ya bi shi da "Sai da safe d'an Alhaji." Duk abin da ya faru akan idon Haseenah wacce ke shirin rufe madafar, k'wafa ta yi tare da mirmushi ta rufe kafin ta wuce d'akin ta, sai da ta gama shirinta tsaf cikin riga da wando masu shegen kyau kafin ta zauna zaman jiran shi.


Kamar yanda ya zamar masa jiki haka yau ma, ya na dawowa da matsananciyar yunwa kai tsaye falon Khadija ya nufa, da sallama d'auke a bakin shi, da gudu Bilal ya tare shi ya na fad'in "Sannu da zuwa Abba."


Cike da rangaji ya d'an rumgume shi yace "Sannu yarima, ya ka ke?"


Mik'ewa Khadija ta yi ta d'auko ruwa da kofi lokacin ya zauna in da ta tashi ya cire hular kan shi, durk'usawa ta yi gwiwarta d'aya a k'asa ta fara tsiyaya ma sa ruwan ta na fad'in "Ko ba ka fad'a ba alamun sun nuna a gajiye ka ke, sannan ka na tare da matsananciyar yunwa wacce ke neman jigata min kai, amma yanzu ka fara da ruwa ma su sanyi." Ta fad'a hakane lokacin da ta mik'o masa kofin ruwan.


Da tattausan murmushi a fuskar shi ya karb'a ya kafa a baki, sai da ya shanye duka ruwan kafin ya sauke numfashi mai k'arfi ya mik'a mata ta karb'a, aje wa ta yi gefe ta janyo k'afar shi ta soma cire masa takalman sa k'afa ciki, zaunawa ta yi kusan shi ta na kallon shi, ido lumshe ya ke kallonta yace "Uwar gida na sarautar mata."


Da wani tsadadden murmushi ta amsa da "Labbaika."


Cike da kasala yace "Wanka na ke so na yi, amma kuma yunwa ba za ta barni ba, yanzu ki zab'a min wanda zai fara yi."


Sai da ta d'an saci kallon Bilal da ya ke tsaye gaban telebijin ya na kallo sannan ta kalle shi tace "Ka k'arasa shiga mana wajen amaryarka, ita ce za ta zab'a ma ka, ko ka manta har yanzu kwananta ka ke?"


Wata doguwar hamma ya yi kafin ya kalle ta yace "Wai ni ban tambaye ki ba ma, yaushe ne kwananki zai zo ne?"


"Me ya sa ka tambaya?" Ta fad'a ta na shafa wuyanta, saida ya rufe ido yace "Ina so na san ranar da zan dawo hannunki ne kawai."


Shiru ta yi ba tace komai ba shi kuma ya mik'e yace "Zan shiga ciki na yi wanka, amma ki tabbatar kun shigo akan lokaci dan mu ci abinci."


Da kallo kawai ta bishi har ya shige ciki, takalman shi ta d'auka ta shiga da su d'akin ta, ya na shiga can ma wata tarairayar ya samu wajen Haseenah har sai da ya yi wanka ya canza kaya kafin su ka zo kan teburi, kallon ta ya yi yace "Ki saka hijab sai ki kirasu su zo mu ci abinci."


D'an jim ta yi kafin ta zagayo kujerar shi ta zauna akan k'afar shi ta na shafa d'an gajeran gemunshi tace "Hubbi na, ban san ko tunanin da na yi zai gamsar da kai ba, amma ina fatan ba zai zama kuskure a gare ka ba, ka ga ni amarya ce, kuma kowace amarya ta na so taga ta more amarcinta babu takura da matsi, wallahi har zuciya ta ba na jin aunty Khadija da Bilal a matsayin takura a gareni, sai dai ina so na sati d'ayan nan mu dinga cin abinci tare da kai, amma kuma na san hakan ba zai yiwu ba saboda ka saba cin abinci da iyalinka, amma gaskiya idan ba ka min wannan alfarmar ba zai sa na ji kamar ba ka d'auke ni a matsayin..."


Da sauri ya rufe mata baki yace "Wa ya fad'a mi ki ke ba iyali na bace? Ai tun ranar da aka d'aura mana aure mu ka zama iyali ni da ke, dan haka kar ki sake fad'in haka, yanzu ba dai maganar cin abinci tare bane?"


Kai ta d'aga cike da shagwab'a alamar eh, d'orawa ya yi da "Angama da wannan buk'atar, sai kuma wata idan akwai, zan wa Ummyn Bilal magana za ta fahimta, sai dai yanzu ki zuba mu su na su abincin sai ki kai mu su, ko ya ki ka gani? Tun da ai ba sa zauna da yunwa ba."


Shiru ta yi kamar za ta fashe da kuka ta kalle shi tace "Ban san me ya sa ba, amma dai da ido na naga Bilal ya kaiwa mai gadi abincin da na ba shi su ci, watak'ila bai mu su dad'i bane."


Shiru ya d'anyi kafin ya kalle ta yace "Shikenan, zuba mana abincin."


Zubwa ta yi amma kuma sam ta k'i yarda ta ci wai ita ta k'oshi, ba dan ran shi na so ba ya ci sai dan kar ta ji ba dad'i, amma har ga Allah abincin bai masa ba, domin kuwa yau ma dai shinkafa ce da jar miya, shi kuma bai fiya cin shinkafa ba da dare, sannan kuma ga ya ji da abincin ma ya yi, da k'yar ya d'an tuttura ba tare da ya nuna mata ba, su na kammalawa yace su je falon Khadija, cikin shagwab'a tace "Wanka fa zan shiga yanzu na yi shirin bacci."


Murmushi ya mata yace "To a shirya da kyau kafin na dawo."


Cikin kwarkwasa tace "To amma fa kar ka jima sosai, wallahi idan ka jima ni bacci na zanyi."


Sai da ya janyota jikin shi yace "To ki ba ni minti talatin, ya isa?"


Waro ido ta yi tace "Talatin? Ai na d'auka saida safe za ka musu, ashe wajen aunty Khadija za ka je ku sha soyayyar ku."


Yanda ta yi maganar da shagwab'a ya sa shi darawa, rusunawa ya yi yace "To ki ban minti ashirin, hakan ya yi?"


Turo baki ta yi tace "Gaskiya sai dai in ka amince da minti sha biyar, shi ma fa daurewa ne na yi wallahi, dan ban cika son yin nesa da kai ba."


Haka kawai ya tsinci kansa da kasa yi mata musu, a cewar shi kam "Angama ranki shi dad'e."


D'aki ta nufa shi kuma ya nufi falon, ya na shiga ya same su a d'akin Bilal ya yi shirin kwanciyar shi, amma da littafi a hannun shi na addu'o'i Khadija na karanta masa ya na maimaitawa, Bilal na ganin shi ya yi saurin daka tsalle ya mak'ale a wuyanshi, cike da zolaya Usman ya fad'a kan gadon ya na fad'in "Wai wai wai, wannan yaron me ka ci hakane da ka yi nauyi? Kaga ka na shirin karya ni."


Tsaye Bilal ya yi ya d'aga rigar shi ya na shafa cikin sa yace "Sarauniya ta cika min ciki na da kayan dad'i."


Tashi ya yi zaune ya na ma Khadija wani kallo yace "Me ki ka ba shi ya ci?"


Bilal ta kalla tace "Ka tambaye shi mana ga ka gashi."


Jayo Bilal ya yi ya kwantar da shi ya ja zanin rufa ya rufe shi, da kan shi ya tofa addu'a a hannu ya shafa mi shi kafin ya sumbaci kan shi yace "Yi baccinka yariman mahaifin shi, safe lafiya."


Kallon shi Bilal ya yi ya sumbaci hannun shi yace "Saida safe Abba."


Murmushi ya masa ya mik'e, zagayawa ya yi wajen da Khadija ke zaune ya kamo hannunta yace "Muje ko kema na shinfid'e ki."


Da sauri Bilal ya juyo ya kalle shi yace "Abba, yau ma ba za ka kwanta tare da mu ba?"


Dukansu ne su ka kafe shi da ido, cikin rashin kuzari yace "Zan kwanta mana, me ka gani?"


"Ka fad'a masa gaskiya, ka ce wajen amaryarka za ka koma, ba na so ka fara sawa yarona wani tunani na daban." Khadija ce ta yi maganar fuska a had'e, juyawa ta yi ta fita daga d'akin, kallon Bilal ya yi yace "Ka kwanta kaji ko, banda tambaya akan abin da bai shafe ka."


"Ka yi hak'uri Abba." Ya fad'a ya na k'ara jan zanin rufarsa.


Ya na shiga ya samu Khadija har ta cire rigar ta za ta shiga ta watsa ruwa, ta na ganin shi ta sa kai za ta wuce ban d'akin, da sauri ya rik'ota ta fad'a jikin shi ya na kallon fuskar ta yace "Me ye haka wai? Me ya ke damunki ne?"


Da k'arfi ta ture shi daga jikinta ta na fad'in "Dallah ni rabu da ni, ka koma wajen amaryarka mana, nasan ai ta na can ta na jiranka, me ka zo yi mana anan? Saida safe? To mun gode Allah tashe mu lafiya."


Ta na fad'a ta juya dan shiga ban d'akin ya sake rik'o ta, had'e fuska ya yi yace "Haseenah ta aiko mu ku da abinci, amma ba ku ci ba kin bawa mai gadi, ko me ya sa?"


Cikin k'unar zuci da wani zafi da ke cikin zuciya tace "Eh, ba zan ci ba, kuma d'ana ma ba zai ci ba, sannan ka fad'a mata karta sake aiko min da abinci dan ba zan ci ba, tun da ai bata ga yunwa a tare da mu ba."


Cike da mamaki yace "Khadijaaa, me ya sa ba za ki ci ba?"


Rik'e k'ugu ta yi tace "Kai me ya sa ka daina cin abinci tare da mu? Ita ce ta buk'aci hakan ko? To ya yi kyau, amma ka sani ni ba sakarya bace da za'a rainawa hankali, kai da ita ku ci na ku tare, ni da d'ana kuma ta ware mana na mu, ma'ana mu kad'ai ne ake son bala'in ya samemu, to ba zai yiwu ba wallahi, abincinta har abada ba zan ci ba."


A hankali ya zauna bakin gadonta dafe da kanshi ya kalle ta yace "Khadija a haka ki ka fahimci abun? Haba dan Allah, me ya sa ki ke haka? Karfa ina yabonki sallah kuma alwala ta gagare ki."


"Sai me?" Ta fad'a har da hararan shi, zunbur ya mik'e ya had'a da jikinshi da k'arfi ya had'e ta da bango ya na kallon k'wayar idonta, k'asa tayi da idon dan haka yace "Kalle ni nan."


Kallon shi ta yi kai tsaye kuma ta sake k'asa da idon ta, cikin daka tsawa yace "Kalle ni nan nace."


A hankali ta d'ago ta kalle shi, hawayen da suka taho mata ne yasa shi cire mata gilashinta ya wurgar da shi akan gado, duk da ta na ganinshi tsaye a gabanta, amma ba ta iya ganin shi da kyau, sassauta murya ya yi yace "Khadija, tun da muke da ke kin tab'a ko da hararan baya na bare kuma gaba na?"


Girgiza kai ta yi alamar a'a, k'ara tausasa murya ya yi yace "To me ya sa zuwan Haseenah gidan nan zai zama sanadin da raini zai shiga tsakanina da ke?"


Shiru ta yi sai hawayen da suka sake bulbulo mata, ganin shirun ya sa yace "Me ya sa idan dare ya yi b'acin ranki ke nunkuwa ne? Wani abu na ke mi ki da ba kya so?"


Da k'arfi tace "Eh, dubi can." Ta fad'a da nuna mi shi makeken gadonta da yatsa, kallo ya yi ita kuma tace "Na yi rashinka akan shinfid'a ta Abban Bilal, kwana hud'u ne kawai mu ka yi nesa da juna, amma jinsu nake tamkar shekara hud'u ne, Abban Bilal na..."


Had'e bakin shi ya yi da nata, dan gaskiyar magana akan abin da take magana baida kalaman da zai iya tausarta da su, tun da bai isa yace bai kusanci Haseenah ba, bai kuma isa yace ba zai k'ara ba, kamar yanda ba zai iya cewa ya datse kwanan Haseenahr ba, tsayuwar ce ya ji ta gagare shi hakan ya sa ya gangara zai kwantar da ita, da k'arfi ta ture shi daga jikin ta ta kalle shi tace "Kar ka sake had'a jikinka da nawa, ba na buk'atar ka."


Ban d'aki ta nufa tana goge bakin ta, shi kam fad'awa ya yi akan gado ido lumshe, ya yi iya k'ok'arin shi wajen gayyato nutsuwar shi amma ya kasa, haka ya mik'e ya fita daga d'akin amma har zuciyar shi ya na sha'awar kasancewa da Khadija, dan ita kad'ai ce ta iyashi yanda take samar mi shi da nutsuwa, ta na jin fitar shi ta fito ta zura farar doguwar riga mai kauri ta kwanta, kuka sai da ta ci ta k'oshi har ta godewa Allah, a k'arshe dai mik'ewa ta yi ta d'auki Qur'ani ta fara karatu, cikin k'ank'anin lokaci sai zuciyarta ta washe ta yi wasai da ita babu ko d'igon damuwa a tare da ita.


Usman kam na shiga dama a rikice ya ke, har d'aki ya samu Haseenah ta shirya cikin arniyar rigar bacci, ta na jin an bud'a k'ofa ta juya, amma abin da ya fito shine ya d'auki hankalinta, a tsaye ya ke k'yam abun har ya bata tsoro saboda ba ta tab'a ganin irin haka ba a rayuwarta, kafin ta ankara ya cakumota jikin shi ya manne bakinta da na shi ha haura da ita kan gado, dama dai rigar wata d'ogal ce, dan haka baisha wahalar cire ta ba, ya na shirin kaiwa ga gaci Haseenah ta dakatar da shi ta hanyar sauka daga kan gadon, kallonta ya yi a raunane yace "L...afi..y.a?"


Kayan ta ta bud'a ta d'auko riga ta zura, da sauri ya sauko daga kan gadon ya rumgumota ya sumbatar wuyanta, dan ba zai iya magana ba, d'an ture shi ta yi taja baya ta na kallon shi tace "Ka je kawai ka kwanta ka yi bacci."


Kamar wanda ya sha kuka haka idon shi su ka yi jawur, girgiza mata kai ya yi da k'yar ya had'a kalmar "B...ba ...zan iya ba."


Ba tare da shakka ko tunani ba tace "To ka je wajen wacce ta d'ora ka sai ta sauke ka."


Banza ya yi da ita ya kumo janyota jikin shi, ture shi ta kuma yi ta kalli idon shi tace "Wallahi kaji na rantse ko ba za ka samu abin da ka ke so ba, a gaskiya ba zan iya d'aukar wannan wulak'ancin ba, haka kawai ranar kwana na amma kaje wajen wata har ka bari ta ribace ka, shine sai ka dawo min kamar kasha wani abu, to ba zai yiwu ba gaskiya."


Ta na fad'a ta kwanta kan gadon ta ja zani ta rufa, kan gadon ya haura ya dinga shafarta ya na rarrashi, amma ko kallo bai isheta ba bare ta kalli idonshi ta tausayawa halin da yake ciki, duk da ranshi ya b'ace haka ya danne ya rumgume ta har baccin wahala marar dad'i ya d'auke shi.


πŸ˜‚πŸ˜‚πŸ˜‚ *Surukin sis Chappa fa yau ba kanta*


Washe gari da safe haka Khadija ta gaggauta had'a sassauk'an abin karyawa, Haseenah ma haka shayi kawai ta had'a da k'wai sannan ta yi wanka, a tak'aice dai safiyar babu mai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login