Showing 48001 words to 51000 words out of 139085 words

Chapter 17 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

gida ya dawo."


Da dariya Bilal ya nufi k'ofar falon mahaifin shi, cikin daka tsawa Khadija tace "Kai Bilal, ka na da hankali kuwa? Dallah malam dawo ka zauna min nan."


Da mamaki duka su ka kalle ta, in da ta nuna masa da hannu ya zauna hakan ya bata damar kama kunnensa tace "Wallahi ka sake zuwa in da matar can take sai na b'ata ma ka rai, kaji ko?"


Yanda ta d'aga murya tare da k'ara murd'e kunnen shi ya sa yace "Na ji Mummy, ki yi hak'uri ba zan k'ara ba."


Nura da ke kallon ikon Allah ne yace "Khadija me ya sa za ki ma sa haka? Naga da ke da ita ai duk d'aya ne, iyayen shi ne ku."


Tsaye khadija ta mik'e tace "Dakata min Nura, ni daban ita daban, wallahi duk yanda za ta kyautata mi shi ba za ta tab'a zama kamar ni uwar shi ba, dan haka kar ka sake had'a min yaro da wata banzar mata da ba ta san darajar shi ba, idan ka zo gani na ne na gode, idan wajen ta ka zo ka shiga ta na ciki."


Juyawa ta yi ta shige uwar d'akin ta, mamaki ne ya kusa kashe Nura, dan shi dai a sanin shi wani ma ba su tab'a samun matsala da Khadija ba bare kuma dangin mijin ta, cikin sanyin jiki ya aje robar lemun hannun shi ya mik'e zuciyar shi na tunanin wane irin kishi ne da Khadija haka? Bilal ne ya mik'e yace "Tonton (uncle) Nura zan bika wajen Hajia."


Shafa kan shi ya yi yace "To ka fara fad'awa Maman ka, idan ta amince sai ka d'auko kayan ka mu tafi."


"To." Ya fad'a ya juya da k'arfi ya shiga d'akin, zaune ya same ta yace "Mummy, tonton Nura yace na d'auko kaya na mu tafi gida wajen Hajia."


Cikin jin haushi tace "Babu in da za ka je, ka wuce d'akin ka ka kwanta ko kuma ka yi karatu."


Hawaye ne su ka cika idon shi saboda shi dai haka ba ta tab'a faruwa tsakanin shi da maman shi ba sai yau, juyawa ya yi zai fita sai taji ya bata tausayi, amma kuma hushin ta da duk dangin Usman da suke murnar an mata kishiya, a hankali tace "Bilal."


Juyowa ya yi ya dawo ya tsaya, hannun shi ta kama tace "Ka had'a kayan ka zan kira tonton Naseer ya zo yanzu ya d'auke ka, hakan ya yi?"


Ba tare da sakin fuska ba ya d'aga kai alamar eh, fita ya yi Nura na tsaye yace "To ya? Za mu wuce ne?"


Kamar zai fashe da kuka yace "Mummy ta hana."


Ji ya yi kafin yace "Shikenan kar ka damu, ai gobe juma'a, watak'ila ku tafi gidan tare da Abban ka."


Shiru bai ce komai ba har ya fita daga gidan ba tare da ma ya shiga wajen Haseenah ba, ta na kiran Naseer kam dama bai shiga gida ba, dan haka ya taho d'aukar shi, sai dai lokacin Usman ya shigo gidan, sun gaisa kamar yanda su ka saba tare da wasa da dariya, amma har Khadija ta had'awa Bilal kayan shi su ka tafi babu fara'a a tare da ita bare ta yi magana, a tak'aice dai haka duka gidan su ka gudanar da daren su babu armashi a ciki, dan Usman ya nunawa Haseenah kuskuren ta ma ko abincin ta bai ci ba, haka ma a d'aki da suka kwanta juya mata baya ya yi, dan in har za ta iya cin zarafin d'an shi har haka to fa akwai yiwuwar ya nuna mata ba'a mi shi wasa da gudan jini.


Washe gari da safe ma haka abin ya ke, kasancewar Khadija ta san a wannan lokacin ya na d'akin shi ya na karatu ya sa ta shiga har can ta gaishe shi, bai wani yi karin kummalo ba ya yi shirin masallaci, *11:00* cif ya fita ya bar gidan zuwa masallaci kamar yanda ya saba, bai dawo cin abinci da rana ba sai aikowa da ya yi aka d'aukar ma sa, da yamma kuma ya kira Khadija yace su shirya dukan su za su je su yi barka gidan Issoufou, tunda magriba Khadija ta gama shirin ta tana jiran shi, Haseenah ma ba ta b'ata lokaci ba wajen shirin duk da fitar ta ta farko kenan, watak'ila ta na zumud'i ne saboda yace zai aje ta har gidan su ma su gaisa da mutane, ana idar da sallah isha'i ya shigo gidan, shi ma sai da ya sake shiri kafin su ka fita gaba d'aya, Haseenah ce baya tare da kwanukan abincin da zata kai gidan su.


Babu mai magana a motar dan kowa da abin da ke ran shi, sai Khadija da ke latsa wayar ta hankali kwance, gidan su Haseenah su ka fara tsayawa dan ya fi kusa da gidan Issoufou, Usman da Haseenah ne su ka fita, amma ganin Khadija ba ta da niyyar fitowa ya sa ya kalle ta yace "Uwar gida sarautar ta motsa ne? Ko sai na fito da ke?"


Ko kallon shi ba ta yi ba tace "Ku shiga kawai zan jira ku."


Wani murmushi ya yi yace "Ke ma kinsan ba zan lamunci haka ba ai, fito mu wuce dallah."


Cike da damuwa tace "Ba na cikin yanayin dad'i, ba na so kowa ya fahimci hakan har a dasa min hak'ora, dan ina fitowa za ace ba na da mutumci na fiya kishi da yawa."


Bud'e murfin motar ya yi ya kamo hannun ta ta fito, bai saki hannun ta ba har sai da su ka shiga cikin gidan, sakin ta ya yi ya saci kallon ta yace "In dai ina da mahimmanci a wajen ki, to ki kankaro min mutunci na a gurin mutanen nan, kar ki bari laifin 'yar su ya shafe su."


Kallon shi ta yi da farko turo baki ta yi, amma da ya marairaice sai ta saki fuskar ta na murmushi, Haseenah da tuni ta shiga gidan su ba ta ma san tsiyar da ke faruwa ba, sallamar su ce ta sa ta mik'e ta d'auko mu su kujeru su ka zauna, mahaifin ta na daga gefe zaune akan kujera, sai mahaifiyar ta na cikin sange zaune akan katifa da alama sunyi shirin bacci kenan, sosai su ka gaisa cike da mutunci da girmamawa, jim kad'an su ka mik'e Khadija na fad'in "Mama mu za mu wuce, saida safen ku."


"To Allah ya bamu alkairi, Allah fisheku dare." Cewar maman.


Da "Ameen." Su ka amsa, Haseenah kamar kar ta tafi take ji haka dai ta taso su ka fito, su na d'aukar hanya Usman ya kalli Haseenah ta madubi yace "Ke Hajia haka ake harkar duniya, daga kawo ki ku gaisa sai ki yi ta wani mak'alewa ba kya so ki tafi."


Cikin turo baki tace "Ni wallahi da ka bar ni na kwana anan ma da zanji dad'i, gidan mu ne fa."


"Wai ki na nufin har kinyi kewar gidan da har ki ke so a bar ki ki kwana anan?"


"Sosai ma, ai tun ranar da aka kaini gidan ka na fara kewar gidan mu."


Kallon Khadija ya yi yace "Hajia ki na jin ta fa, yanzu ke dan Allah za ki yarda ace ki je gidan ku ki kwana?"


Fuska ba annuri tace "Saboda ni banyi shak'uwar da zan iya kewar 'yan uwa na ba kenan? Ai ko yanzu ka ce tafi to sai dai ka aje ni na d'auki adaidaita, dan gani zanyi kamar motar nan ba ta gudu sosai."


Maida hankalin shi ya yi kan tuk'i yace "Kenan idan na fahimce ku duk cikin lamarin ni ne bare, kun nuna min har yanzu ba ku d'auka ta kamar yanda na ke d'aukar ku, kun nuna min har yanau babu wacce ta ke jin za ta iya k'arar da rayuwar ta a tare da ni."


Wata shegiyar harara Khadija ta masa tace "To me za mu zauna mu yi da tsoho, ka na so ne mu kai lokacin da za mu fara goge ma ka majina a hanci."


Hannu ya kai ya damk'o wuyan ta ya na dariya ya na fad'in "Ni ne ma tsohon? Yanzu ke mijin na ki ne tsoho? Lallai ma yarinyar."


Gwalo ta mi shi ta na fad'in "Gashi kai ma ka fad'a da bakin ka, har yanzu ni yarinya ce, tunda sai nan shekara biyu zan cika *talatin da biyar*."


Juyowa ya yi ya kalli Haseenah yace "Ke kin yarda mijin ki tsoho ne?"


Haseenah da haushi ya fara kashe ta ne tace " A zahiri wanda bai san ka ba zai iya kiran ka da tsoho, amma ni a wuri na ba tsoho bane, dan ni nasan k'arkon miji na."


Dariya Usman ya yi ya juyo ya bata hannu alamar su bige βœ‹ tare da fad'in "Ban biyar amarya ta." Bashi ta yi su ka bige su na dariya.


Kallon Khadija ya yi yace "Sai yanzu ai na fahimta, ashe ke ce ki ka tsufa ba ni ba."


Dariya ita ma ta yi tace "Amarya kam dole ta fad'i haka, amma da tasan waye kai lokacin da ka ke ji da k'uruciya, to fa da za ta gasgatani d'ari bisa d'ari, amma da ya ke zuwan shekaranjiya ce ita ba za ta gane komai ba, ko ba haka ba?"


Ta fad'a ta na kashe masa ido d'aya, turo baki ya yi gaba yace "Za ki yi magana ne idan ki ka shigo hannu na."


Bushewa ta yi da dariya tace "Yanzun haka ina matakin shekarun cikakkiyar mace ne da ke jin jini a jika, dan haka ba za ka tab'a tsorata ni ba malam Manu."


Wani mayan kallo ya mata ya na d'an cije labb'an shi na k'asa, sake tsinkewa ta yi da dariya har da kai mi shi duka a hannu ta na kwantar da kan ta a kafad'ar shi ta na fad'in "Ka tuna? Ka tuna wannan ranar da ka fad'a min haka? To nima na rama, yanzu ina kan shekaru na ne, dan ni yanzu ma ji na ke kamar yanzu ne na balaga, dan haka ka zama tsoho a wuri na."


Shi ma dariyar ya ke sosai yace "A ranar kam sai da na k'ara gyara tsayuwa ta sannan na ce mi ki, yanzu fa sai kinyi hak'uri da ni, dan ina ganiyar shekara talatin da biyar ne, shekarun hura wutar..."


Da sauri ta rufe ma sa baki su na ci gaba da dariya, d'an k'aramin tsaki Haseenah taja da ya sa su ka kalle ta, saita nutsuwar su su ka yi Khadija tace "Yi hak'uri amarya."


Take ta kalli Usman ta saisaita murya tace "Abban Bilal, munga shekaran jiya tare da kai, haka ma munga jiya da yau, insha Allahu da izinin ubangiji za mu ga gobe."


Wani fari ya mata da ido alamar wai ta sumbace shi, ita ma mayar masa ta yi da idon alamar a'a, Haseenah da abin duniya ya isheta ne tace "Wai har yanzu ba'a kawo gidan ba ne?"


Babu wanda ya kalle ta sai Usman da yace "Halan bacci ki ke ji?"


Banza ta yi da shi daga haka har su ka isa gidan, nan ma da suka shiga wata sabuwar hira aka dasa Khadija da Usman da Issoufou da mai jego kasancewar babu kowa a gidan sai yaran su da kula mai tayata kwana, da ganin yanda suke hira kasan akwai shak'uwa da fahimtar juna da kuma mutunta juna, saida dare ya yi su ka taso su ka dawo gida, kowa d'akin shi ya nufa ya yi shirin kwanciya, sai da Usman ya zo ya wa Khadija saida safe kafin ya koma, duk da Haseenah ba ta bashi hak'uri ba akan abin da ya faru, amma da ya neme ta sai ya sa ta sake jin girman kai, hakan ya nuna mata ko ka wa namiji laifi ran shi ya b'ace dole shi zai neme ka ko dan biyan buk'atar shi, da haka gari ya waye.




*Yau kuma da wacce aka wayi gari? Sai kun biyo ni.*
02/02/2020 Γ  20:58 - πŸ’‹πŸ˜˜πŸ’‹: πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘πŸ’‘






_SAMIRA HAROUNA_




*Littatafan marubuciyar*




*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._




*SADAUKARWA GA*


_MATAN FARKO_πŸ§•πŸΌ *(UWAYEN GIDA)*




πŸ‡ΈπŸ‡¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_πŸ€œπŸ€›




```Fatan alkairi masoya```


*Godiya masoya, πŸ˜‚na yi dariya sosai ganin comment d'in ku rututu, Haseenah no fan's.*πŸ˜‚


πŸ’• _A sannu a hankali sai cinye shekaru na na ke tamkar yanda nake cinye abinci na, damuwa ko tunanin hakan ba shine mafita ba, domin kuwa babu abin da zai dakatar da ita idan har ta zo, fata na bai wuce na gama da duniyar nan lafiya ba, sannan na rabu da iyaye na lafiya da 'yan uwa da masoya, ba na buk'atar tsawon shekaru, na fi buk'atar k'arancin su in dai masu albarka ne da anfani, *ina taya kai na bak'in ciki*, domin ba na ce farin ciki ba, domin har yanzu banyi wani tanadi dan ranar gobe ba, amma abun mamaki dayawa su na murna ne har da shagali saboda sun k'ara shekara, basa la'akari da shekarun su ne suke tafiya basu ankara, sai sun wayi gari sun jisu cikin k'abari, Allah ka bamu shekaru ma su albarka._πŸ’ž




_Bismillahir rahamanir rahim_




*18*




Ya shirya zai fita ya shigo wajen Khadija ya same ta zaune a falo sai Uwani da ke aiki, bayan sun gaisa ne tace "Babban mutum ina neman izinin ka zanje wajen kitso da lalle?"


Murmushi ya mata yace "Ko ban tambaya ba nasan za ki fara shirya min kan ki ne, dan haka kin samu izini na, sannan..." Ya fad'a ya na saka hannu aljihu ya ciro kud'i, mik'a mata ya yi yace "Ga wannan ko, sai a k'ara ayi kwalliya da kyau."


Sunkuyar da kai ta yi ta rufe ido da hannayen ta, sunkuyowa ya yi ya lek'a fuskar ta yace "Iyeee! Kunya ce wannan? Kin tuna amarcin kenan? To shikenan bara ki gani."


Tsakiyar maman ta ya tusa mata kud'in tare da sumbatar goshin ta yace "Ni na tafi sai na dawo."


Sai da ya ksa kaiwa ga k'ofar fita ta d'ago tace "A dawo lafiya, godiyar kuma na mik'o ta zuwa wani lokacin." Yanda ta k'arashe maganar da fari ya sa ya saki murmushi yace "Ina jira, dan nasan abun zai k'ayatar tunda ke ce za ki yi shi."


Ya na fita ta tashi ta k'arasa shirin ta, tare da Uwani su ka tafi a motar ta gidan kitso da lalle da ma sauran gyaran jiki, kasancewar babu mutane a wurin ya sa aka fara mata abin da ya kai ta, sun jima sosai a wajen, dan sai kusan k'arfe biyar na yamma su ka koma gida ita da Uwani, tun a hanya ta tsaya ta siye salade dan ta ci, su na zuwa gida Uwani ta shiga gyaren shi ita kuma ta shiga wanka, ko da ta gama shiri Uwani har ta fara yankawa, zaune ta yi su na hira su na aiki har magriba, kuma har lokacin ba ta ga Haseenah sai motsin ta da su ke ji a madafa, a haka duka suka gama aiyukan gaban su suka koma d'aki.


Tunda wuri ta yi shirin baccin ta yau saboda ta huta dan gobe ita ce da aiki, doguwar rigar bacci ce a jikin ta da ta sauka har k'asa haka ma hannayen rigar, sanin Usman zai shigo ya sa ta k'i saka komai daga cikin rigar, ma'ana dai babu komai daga ciki bayan rigar, ai kam ta na jin motsin shi ta yi sauri ta mik'e ta fara kai da kawon iska, ya na bud'a k'ofar da sallama a bakin shi, da sauri ya d'ora da "Wai wai wai, kar dai na shigo lokacin da bai dace ba?"


Juyowa ta yi da murmushi tace "Wane lokaci ne bai dace Abban Bilal ya ga Umman Bilal ba?"


Takowa ya yi zuwa gaban ta ya na kallon ta yace "Ba na tunanin akwai lokacin gaskiya."


"Kuma ka fad'a?" Ta fad'a da kafe shi da ido.


Hannu ya kai zai kamo ta ta janye ta zauna kan gado ta na fad'in "Dama ina son magana da kai."


Zaunawa ya yi ya na fad'in "Uhum, akan me?"


Satar kallon shi ta yi tace "Akan maganar kwana ne dama."


Da sauri ya kalle ta yace "Me ya faru da kwanan ki? Ina ce gobe ne ko?"


Ajiyar zuciya ta sauke tace " Eh gobe ne, amma kuma da matsala."


Gyara zama ya yi ya na kallon ta yace "Matsalar me? Ki yi magana mana dan kinsa hankali na ya fara tashi."


Mik'ewa ta yi tsaye kamar marar gaskiya ta na kallon shi ta na wasa da yatsunta tace "Eh to, gaskiya dai ba na sallah, shi ya sa na barwa amarya kwanan na wa."


"Me?" Ya fad'a ya na tashi tsaye, janyo ta ya yi jikin shi yace "In dai ba b'ata na yi ba ai tunani na lokacin zuwan bak'on ki baiyi ba, me zai sa ya canza lokacin zuwa yanzun? Saboda ya san ina buk'atar ki ne a kusa da ni kome? Ko shi ma haushi na ya ke ji ya na taya ki kishi ne?"


Da sauri ta janye daga jikin shi ta yi baya ta na fad'in "A'a ba ko d'aya, gaskiya na ke fad'a ma ka fa, ka yarda mana."


Had'e fuska ya yi yace "Naga tafin hannun ki."


Da sauri ta mayar da hannayen baya tace "Um um."


Murmushi ya yi yace "Wata kala ce kawai ki ke so ki min kuma na gano ki, dan haka ki ci gaba da min shirye shirye kawai."


Juyawa ta yi ta nufi ban d'aki ta na fad'in "Ni fai na fad'a ma ka na barwa amarya kai, dan yanzu har na saba da bacci ni kad'ai."


Har da gudu ya had'a wajen janyo ta jikin shi ya na shafa ta ya na fad'in "Kenan ba ki yi kewata ba ko kad'an?"


Cikin narkakkun idon ta ta kalle shi ta gilashi tace "Idan ma na yi ko banyi ba, idan ka shigo hannu na za sani."


A hankali ya matso kan shi ya na son had'e bakin su da sauri ta fizge daga gare shi, juyawa ta yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login