Showing 123001 words to 126000 words out of 139085 words
Chapter 42 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*38*
Bai samu ganin Khadija ba saboda a lokacin suna sallah, kuma an rufe d'akin da Bilal ke kwance saboda hayaniyar da tayi yawa aka barshi shi kad'ai kafin wani lokaci, fita Usman d'in ya yi yace zai dawo anjima.
A wajen Haseenah ba yanda ta iya dole ta d'an d'auki abin da ta d'auka ta fito ta na kuka ta bar gidan, amma da taje gida kasa fad'an komai ta yi sai tace kawai ta na girki ya same ta yace ta taho gida ya sake ta saki biyu, su kam iyayen take su ka d'ora laifin kan Khadija cewa ita ta shiga ta fita aka sake ta, Haseenah dai komai ba tace ba sai sauraren su, mahaifin ta ne yace zai je ya samu mahaifin Usman d'in dan ba zai d'auki wannan wulak'ancin ba a sako masa 'ya da tsohon ciki, ba ta yi yunk'urin hanawa ba tunda ita kan ta za ta so ta koma d'in, haka ko akayi bayan sallah magriba anyi katari malam ya na gidan mahaifin Haseenah ya sallama ya fito, da ganin shi malam ya tarbe shi yanda ya kamata ya shinfid'a mu su tabarma a waje su ka zauna, nan fa malam *Mussa* ya fad'awa malam abin da ke faruwa, sosai malam ya jinjina ya kuma fad'a mi shi baisan me ke faruwa ba sai yanzu, amma ya yi alk'awarin tuntub'ar Fodio yaji dalilin yin hakan, nan dai ya kwantar masa da hankali suka rabu lafiya, malam kam baiyi k'asa a gwiwa ba wajen kiran Usman yace ya same shi gida, ana idar da sallah isha'i ya k'araso ya samu malam, a cikin gida suka samu waje tare da Hajia suka tattauna sosai sosai, anan ya fad'a mu su cewa "A gaskiya Baba ba zan iya zama da yarinyar nan ba, domin kuwa duk ita ce silar abubuwan da suka dinga faruwa da ni, kawai ku rabu da ita can ta haihu, idan ta haihu zanje na d'auko abinda ta haifa bayan ta shayar da shi dan ba zan iya barin abin da ta haifa a hannunta ba saboda mugun halin ta."
Malam ne yace "Amma duk abin da tayi Fodio bai kamata ka sake ta a wannan halin ba."
Shirun da ya yi yasa Hajia cewa "Koma dai menene ita taja, a gaskiya Hassenah ta bamu mamaki, yarinya sumi-sumi ashe lunbu-lunbu ce macijin k'yaik'ayi, muna ta wa Khadija kallon mai laifi ashe ita ce muguwar."
Murmushin gefen labb'a malam ya yi yace "Ai ni na sani dama *kallon kitse ne ku ke wa rogo*, kawai na zura mu ku ido ne har ita yarinyar ta mu ku ido, in banda hauka irin na ku ma ko gaske ne Khadija ta mallake Usman ai ni a gani na daidai ta yi, domin kuwa in har za mu iya yin magana irin ta jahilai to za mu iya cewa k'ashin arzik'in shi a jikin ta yake, shi ba kyau ba, shi ba hasken fata ba, shi ba kud'i ba a lokacin da ta aure shi, kuga kuwa tana da damar da za ta iya d'aukar kowane mataki dan ya zama na ta."
Cikin sanyin jiki Hajia tace "Gaskiya ne, wallahi sai yanzu na ke jin kunyar ta akan abubuwan da suka faru, daurewa kawai nake ina kallon ta."
Murmushi Usman yayi yace "Hajia ku kwantar da hankalinku in dai Khadija ce na tabbata ba ta kallon ku da wannan abun."
Nan dai suka gama tattaunawarsu kafin ya mu su sallama yace zai tafi asibiti, su kuma dama acan su ka yi sallah magriba, ba su jima da dawowa ba Abban Haseenah ya zo, daga nan asibiti ya nufa ya samu kam kamar ana wata sabga d'akin taf da mutane, Khadija dake zaune kusan Bilal muryar shi ce ta fallasa mi shi yanayin da yake ciki, duk sai taji ba dad'i tausayin shi ya kamata, gaisawa ya yi da mutanen dake d'akin kafin ya isa a gadon Bilal, kafe Khadija ya yi da ido yace "Nana ya mai jikin?"
Saida ta had'e abin da ya tokare mata mak'oshi ta kalle shi da murmushi ta sa hannu ta karb'i k'atuwar ledar hannun shi ta aje gefe tace "Mai jiki gashi nan da sauk'i."
"To Allah ya bashi lafiya." Ya fad'a ya gyara tsayuwarsa, sake d'agowa ta yi ta kalle shi, saida ta k'are masa kallo tace "Babban mutum ka ci abinci kuwa?"
Wani murmushin gefen labb'a kawai ya yi bai bata amsa ba, duk da zuciyarta na raya mata wani abun amma kuma k'wak'walwarta na hasko mata wani abun, kawai anfani tayi da abin da k'walwarta ke hasko mata ta kalle shi ta mik'e tsaye tace "Ina ga mu tafi gida kawai, ga Mama nan za su kwana a wajen shi."
Da mamaki ya kalle ta ya kuma juya ya kalli Mama, mama ce tace "Kuje kawai zan zauna wajen shi, ai ni ce ke daidai dama na tsaya tare da shi tunda d'an gudaliyar mijin ne."
Murmushi su ka yi kafin Usman ya fara fita ita kuma ta had'a kayanta ta same shi a mota, kallonta ya yi yace "Wane gidan zan kai ki?"
Dariya ta yi tana kallon shi tace "Gidan miji na mana, ko ka manta yau ne zan dawo dama?"
Lumshe ido ya yi ya kwantar da kanshi jikin kujerar motar, d'agowa ya yi ya kalle ta yace "Khadija Allah ya miki albarka, kamar kinsan ina buk'atar kulawar ki, Khadija duk duniyar nan ke kad'ai ce macen da ta iyani."
Da murmushi a fuskarta tace "Muje to ka min wanka ka canza min kaya, sannan na sama mana abun da za mu ci sai muyi bacci."
Wata harara ya dallo mata yace "Baccin lafiya? Yau fa kamar amarya ki ke."
Dariya ta sake yi tace "To mu samu muje gidan ko." Tayar da motar ya yi su ka d'auki hanya, saida ya tsaya ya siya musu sandwichs a hanya kafin suka wuce gida, tare suka shiga wanka suka shirya cikin kayan bacci kafin suka d'an sama cikin su sandwich d'in nan, sam Khadija ta manta ma da maganar wata wai Haseenah, hakan yasa ba ta tambaye ta, shiru d'akin ya d'auka saida Khadija ta juyo in da Usman ke kwance, zaune ya ke akan gadon ya tangale bayan shi da pilow damuwa b'aro-b'aro a fuskar shi, tashi ta yi zaune ta matsa kusan shi ta d'ora hannun ta akan k'irjin shi tare da d'ora kanta a kafad'ar shi, gyara mata zaman ya yi ta yanda yake shafar kanta a hankali, cikin taushin murya tace "Bilal ka ke tunani ko?"
Shiru ya yi kamar ba zai amsa ba sai kuma ya sauke ajiyar zuciya yace "Hakane, muna kwana nesa da Bilal a lokacin da ya kwana gidan su Hajia ko gidan su Mama, amma ban tab'a tunanin akwai ranar da za ta zo ba ina kwance kan gado na cikin sanyi shi kuma ya na kwance a gadon asibiti, ban tab'a tunanin haka ba ko kad'an."
Zunbur ta tashi zaune tana kallon shi tace "Ba ka tab'a tunanin wannan ranar ba? Amma me ya sa? Ko ka manta da mutuwa ne?"
Shiru ya yi ya tsareta da ido, d'orawa tayi da "Abban Bilal, mu gode Allah daya kasance ya na raye mana, da fa ta Allah ta kasance da yanzu ka na kwance akan gadon nan ne shi kuma ya na kwance cikin rami, zanin rufar shi shine k'asa, kaga kuwa sai mu gode Allah a hakan ma."
Murmushi kawai ya yi bai ce mata komai sai kallon ta da yake, matsawa ta yi ta sake lafewa a jikin shi tace "Yau fa dare na ne na farko, kar ka bari tunani da damuwa suyi tasirin hana ka kula da ni da kuma wannan bawan da baisan ma asalin yana da mahaifi ba har yanzu, ka bamu kulawar ka mana na wannan dare, karka damu da Bilal insha Allahu ya na cikin kariyar ubangiji tare da kulawar Mama, zaiji sauk'i."
Dariya ya yi ya matse ta sosai a jikin shi yace "To yanzu me kuke so na fara mu ku, dan dole zansa wannan d'an baban farin ciki yasan cewa yau fa ya shigo hannun shi, amma ina fatan dai kin shirya karb'ar uk'ubata?"
Da mamaki ta kalle shi tace "Ban gane uk'ubar ka ba?" Murmushin mugunta ya mata yace "Nasha wahala sosai kafin ki yarda ki dawo gida na, kin whalar da ni sosai, kin azabtar da ni fiye da tunanin ki, dan haka nima yanzu zan rama a daren nan tunda kin shigo hannu na."
Zabura ta yi ta na neman durkuwo daga kan gadon ya yi saurin rik'o ta yana fad'in "Ai ba ki isa wallahi, ina ki ke tunanin za ki je a daren nan? Daga ni sai ke fa a gidan."
Kukan shagwab'a ta saka mi shi tana zillewa tana fad'in "Allah bar ma gidan ka zanyi, ciki na fa k'arami ne, so ka ke min asarar shi bayan 'yan uwan ka har tsegumi suka fara min saboda ban k'ara haihuwa ba, Allah ni dai ka rabu da ni."
Sosai ya rumgume ta yace "Mak'aryaciya kawai, na fa san komai, cikin ki ya kusa shiga wata shida, a hakanne zan zubar da shi?"
"Ni dai ka sake ni na koma d'aki na kawai tunda mugunta za ka min." Ta fad'a ta na son raba kanta da shi, ya rik'e ta sosai ya rad'a mata a kunne "Na mi ki alk'awarin tafiyar da ke a hankali, abinci kawai zan baku cike da k'aunar ku."
D'ago kai ta yi ta kalle shi tace "Na ga idon ka idan gaskiya ka ke fad'a." Da sauri ya sa tafukan hannayen shi ya rufe fuska ya juya mata baya yace "Um um, ban yarda ba gaskiya."
Cakulkuli ta fara masa ta na fad'in "Ashe ba gaskiya ka fad'a ba, yeee Allah ya tona min kai."
Da irin haka suka tafiyar da daren su cike da kewar juna, bayan komai ya kammala ma alwala su ka yi Usman na gaba ita a bayan shi su ka yi k'iyamun-laili, ana kiran sallah farko ya nufi masallaci ita kuma ta mayar da sallahnta, daga nan kan darduma bacci ya d'auke ta, ko da ya dawo ya ganta d'aukar ta ya yi ya kwantar akan gado, makullin mota ya d'auka ya fita ya samo mu su abin karyawa ya aje kafin ya shirya ya fita zuwa asibiti, duk lokacin Dije na bacci bata farka ba, ya jima a asibiti tare da Mama da malam da Hajia suna ta hira kafin ya baro asibitin, gida ya dawo kai tsaye ya samu Khadija zaune akan teburin cin abinci ta na zubawa za ta ci, k'arasowa ya yi ya zauna yace "Dijangala tame gari, Dije sarkin hutu har an tashi kenan?"
Murmushi kawai ta yi tace "Na tashi, amma kuma saina nemi mijina na rasa in da ya shiga, kad'an ya rage na bayar da sanarwa a gidan radio sau kuma ga ka."
Cikin dariya yace "Allah ya na son ki da rahama shi ya sa ba ki yi asarar kud'in ki ba."
Zaune ta yi ta na aje farantin abincin gaban shi tace "Kuma na yi sa'a miji na ya na iya jiyo bugun zuciya ta daga duk in da yake, hakan ma ya taimaka wajen dawowar ka kusa da ni."
Hannu suka saka tare, kafin ta kai loma bakin ta tace "Wai ina Haseenah ne? Ba za ta fito cin abincin ba?"
Jim ya d'anyi kafin yace "Bata nan." Ba tare da damuwa ba tace "Ok, ko ta tafi asibiti ne awo?"
Shiru ya yi kamar ba zai amsa ba sai kuma yace "Ta na gidan su." Kallon shi ta yi tace "Gidan su kuma? Lafiya dai ko?"
Cike da jin an takura shi yace "Kai Khadija, ta na gidan su na ce mana, sakin ta na yi."
Dam, taji gaban ta ya fad'i, tabbas tasan ba su yi zaman lafiya da Haseenah ba, kuma ta na kishinta sosai ta na kuma ji haushin irin cutar da ta mata, amma hakan ba shi zaisa ta yi farin ciki da mutuwar auren ta ba, abu d'aya da ta sani shine ita ma mace ce kamar ita, tasan dole wannan kalmar ta girgiza tunanin ta, abun duba kuma anan shine cikin da ke jikin ta, in har za ta iya fad'an gaskiya to duk abin da ta yi ya kamata ace an mata uzuri, dan ko ita ce ba ta san irin damuwar da za ta shiga ba idan aka ce haka ta faru da ita, bare Haseenah da ko wata takwas ba ta yi ba a gidan miji amma ace an sake ta da cikin fari a jiki, a hankali ta kalle shi tace "Amma Abban Bilal zan iya cewa wani abu?"
Ba tare da ya kalle ta ba yace "In dai akan wannan yarinyar ce ba buk'ata, hukunci ne kuma na yanke, zan kula da komai daga yanzu har lokacin da za ta haihu, idan ta haihu kuma ta gama shayar da abin da ta haifa zan d'auko shi na dawo da shi kusa da ni, nasan banda matsala wajen samun wanda zai rik'e shi, ko ke za ki yi min wannan karamcin."
Wani mamakin ne ya sake bayyana a fuskar ta ta na kallon shi, ganin haka ya sa ya mik'e yace "Ni zan fita waje, idan kin gama ki same ni saina aje ki asibiti."
Da kallo kawai ta bishi har ya fita, ji ta yi abincin ya fita a ran ta ita ma sai kawai ta tattara ta shiga da shi madafa, juyewa ta yi a kwano ta fito da shi ta bawa Rabe, godiya ya mata kafin ta samu Usman suka wuce, babu mai magana har suka isa asibiti ya aje ta a bakin k'ofar, saida ta fito ta rufe k'ofar ta kalle shi tace "Allah ya kiyaye hanya, sai ka dawo."
Kallon ta ya yi yace "Ameen, Allah ya sa." Da haka ta shiga ciki shi la ya wuce, sosai ta yi farin cikin ganin Bilal a zaune ya na shan koko mai d'umi, godiya ta yi ga Allah da ya sa yaron ta ya rayu kula har za ka iya cewa ma jikin shi da sauk'i fiy da jiya da ba za ka ce ya na raye ba, sai dai fatan Allah ya k'ara mi shi lafiya mai anfani.
Haka su ka ci gaba da jinyar Bilal cike da kulawa, in da aka d'auke shi daga gidan gaggawa aka mayar da shi cikin asibitin, kullum 'yan uwa su na zirganiya a hanyar asibiti ganin Bilal, Khadija kuma da Usee suna farin ciki idan suka koma gida, har yanzu ba ta sake mi shi maganar Haseenah ba amma abun na damunta sosai, kullum tana auna hakan da kanta ta na ganin idan ita ce ya za ta yi? Ta na so ta sake mi shi magana amma da ta yi magana da Hajia sai tace kawai ta share ta kar ma tasa ran shi ya b'ace akan wata, shi ya sa ta d'anyi shiru amma ba wai ta hak'ura bane, dan abin da take tunani ba kowa bane ke tunanin shi, a haka suka kwashe *sati d'aya* a asibiti.
*Kwana goma sha d'aya* aka sallami Bilal saboda jikin shi ya yi sauk'i sosai cikin hukuncin ubangiji, a lokacin kuma Haseenah rayuwa ta fara gara ta yanda take so...
*Allah ka sa mu dace.*
13/03/2020 Γ 14:14 - πππ: ππππππππππ
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*39*
Sabo da jar miya da cin abin da rai ke so ya sa Haseenah ba ta iya cin abincin gidan su, da yake ta na da 'yan kud'in da ta samu hannun Usman sai take anfani da su wajen siyan abin da take so, sannu-sannu kuma sai k'annan ta suka fara d'ora mata raini ta yanda ko aikensu ta yi ba sa zuwa, da k'yar wani lokacin za ta basu kud'i su tafi, wani lokacin kuma sai dai ta tafi da kanta ta siyo dan abu mai galmi da yaji, gaba d'aya a takure take jin kanta a zaman gidan nan, d'akin da suke kwana ita da k'annan su ga zafi ga rashin sarari, yau dai data tashi ta d'auko jakar yan kud'in ta da nufin siyo abin kari sai kud'i suka ce nemi in da ki ka aje, nan ta yi haukan nema amma ba ta gani ba, ta tambaya maman ta kuma tace to ita ina za ta sani, kuma ba kowa gidan sai su duk sauran su na makaranta, dole d'umamen tuwon da aka yi shi ta dank'ara tasha ruwa, ruwa ta kai ta d'auki kwandon sabulu dan yin wanka, amma sabulun sai kad'an ya rage wanda ba zai mata komai ba, cikin jin haushi ta kalli maman ta tace "Mama, wai yanzu shi ma sabulun da na saka saida wani ya d'auka?"
Cikin sanyin hali tsohuwar tace "To Haseenah ba sai ki yi hak'uri ba, da kina gidan ki nan kowa ke wadace da sabulun, sun d'an saba ne da wanka da mai k'amshin shi ya sa da su ka ga naki su ka d'auke."
"To amma Mama ni fa kad'an ne na taho da shi sabulun, yanzu haka ina ga bai wuce uku ba wanda ya yi saura, idan ya k'are sai mu yi ya kenan?" Duk ta yi maganar ne kamar za ta fashe da kuka, a tak'aice tace "Sai ku taru ku hak'ura."
Tsaki ta yi ta shiga d'aki ta d'auko wani ta saka ta shiga ban d'akin, wanka ta