Showing 63001 words to 66000 words out of 139085 words

Chapter 22 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt

kafe shi da ido da tsananin mamaki, jinkirin ne ya sa yasa Usman kallon ta ganin ba ta da niyyar zuba abincin ya sa yace "Abincin na ki ko na siyarwa ne? Sai ki mana baya ni ai."


Murmushi ta masa ta mik'e ta fara zubawa, shi ta fara zuba ma ta aje a gaban shi sannan ta zubawa Haseenah da ke ta kakkaryewa ta aje mata, ta na shirin zuba ma kan ta Haseenah ta ture faranti gefe ta mik'e tsaye ta kalle shi tace "Baby, zan koma d'aki na na kwanta, ba na jin sha'awar cin abincin nan kwata-kwata."


Kamar mazari haka ya fara tambayar ta "To me za ki ci idan ba ki ci abinci ba? Fad'a min me ki ke so ki ci to? Ai ba kya zauna da yunwa ba ki cutar da kan ki."


Cike da yatsina fuska tace "Umm, da ace zan samu indomie da na ji dad'i."


Kallon Khadija ya yi ya kula kallon ta yace "Abu mai sauk'i, bara yanzu a dafa mi ki, kije ki kwanta to." Kallon Khadija ya yi da ke tsaye yace "Am dan Allah na ce ba, ki taimaka mata ki d'ora mata, ina ganin kamar ba ta da lafiya ne fa, dan gaba d'aya yanayin ta ya canza."


Kallon shi Khadija ta yi ta na wani shegen murmushi mai kama da na mugunta tace "Ka yi hak'uri Abban Bilal, ban raina ka ba, kuma ka isa ka sani komai na yi maka, amma banda hidimar matar ka, gaskiya matsayi na bai taka wannan matakin ba, ka yi hak'uri idan na b'ata maka rai."


Ta na fad'a ta rufe kwanukan ta juya ta bar wajen, komai bai ce ba sai bayan Haseenah da ya bi da abincin ya lallab'a ta har ta ci, saida su ka gama kad'ai ya samu ya fita, saida ya shiga wajen Khadija ya same ta falo zaune, tsaye ya yi a kan ta ya ciro kud'i aljihun shi ya mik'o mata yace "Ba na da tabbacin za ki yi abin da na saka ki, amma dan Allah ki taimaka ki mana abinci mai yawa saboda ba zan dawo ci ba, zan aiko a d'auka saboda akwai bak'in da su ka zo mana."


Karb'a ta yi da hannu biyu tace "Zanyi farin ciki a lokacin da nake aikin nan, saboda hidimar ka ce."


Juyawa ya yi zai fita ta bishi da "Adawo lafiya."


"Allah ya sa." Ya fad'a a tsaurare.


Tun k'arfe d'aya Khadija ta kammala komai kamar ba ta yi ba, sai bayan sallah azahar Usman ya aiko aka d'auki manyan kwanukan tare da lemun da aka had'a na zallar abarba, ba jimawa ta kira shi tace su na so su koma ganin jikin Baba, cike da k'aguwa yace "Kuje, amma ki tabbatar tare ku ka tafi da Haseenah, dan ba na son raba kan nan da ku ke, sannan kar ki manta su na gida an sallame su."


Kafin ta yi magana ya datse kiran, dama a shirye take ita kam, Uwani ta kalla tace "Uwani ki je ki fad'awa Haseenah ta shirya yanzu za mu tafi ganin jikin Baba."


"To." Cewar Uwani ta nufi hanyar fita, jim kad'an ta dawo tace "Na fad'a mata tace ta na zuwa."


Kallo suke su na hira har sama da awa d'aya Haseenah ba ta fito ba, Khadija ta k'agu sosai dan haka ta kalli Uwani tace "Uwani dan Allah koma ki sake fad'a mata ta gaggauta, har uku ta na shirin yi mana a gida ba mu fita ba, ni kuma a wannan lokacin madafa ya kamata ace zan shiga."


Fita Uwani ta sake yi, amma ko da ta dawo sai cewa ta yi "Umman Bilal wallahi da na shiga na same ta kwance akan kujera da d'aurin k'irji, da na fad'a mata sai tace wai da zata shiga wanka, amma kula ba ta jin dad'in jikin ta kawai ki tafi za ta je daga baya."


Saida Khadija ta lumshe ido saboda haushi, mik'ewa ta yi ta kalli Bilal tace "Ka koma d'aki ka sako kayan makarantar ka daga nan saina aje ka, dan banga anfanin dawowar ba tunda mun riga da mun makara."


"To Mummy." Ya fad'a ya na nufa d'akin shi, bayan yan mintuna ya dawo da kayan makarantar shi da jakar shi a hannu, Khadija kuma bawa Uwani makullai tace "Ki rufe ko ina sai ki same ni a mota."


Karb'a ta yi ta kulle ko ina ta fita waje ta same su a k'ofar gida su na jiran ta, shiga ta yi su ka wuce suna tafe su na hira har suka isa, Uwani ce ta fito da kwanukan ita kuma ta na rik'e da jakar ta, haka suka shiga bayan sun gaisa suka zauna aka d'an tab'a hira, ana fara kiran sallah Khadija ta tashi su ka yi alwala su ka yi sallah, suna gamawa kuma suka musu sallama suka tafi saboda kar Bilal ya makara, haka suka aje shi sannan suka wuce gida kai tsaye, da shigar su ta hangi motar Usman, ba ta yi mamaki ba dan tasan wasu lokuta ya kan dawo ya yi wanka, su na shiga falon su suka ja birki ita da Uwani saboda ganin Usman zaune kai da gani kasan babu arziki ko mutunci cikin zaman, gabanta na fad'uwa ta k'arasa kusa da shi tace "Abban Bilal ashe ka dawo? Sannu da zuwa."


Uwani ya ma jan kallo yace "Kira min Haseenah."


Wucewa ta yi ba tace komai ba dan dama tun farko ya na mata kwarjini, Haseenah ta kira suka fito kusan a tare, tsaye duka su ka yi sai Uwani da ta fita farfajiyar gidan, tsaye ya mik'e yace "Nace ku tafi tare, amma me ya sa ki ka tafi ki ka barta?"


K'aramar ajiyar zuciya ta sauke ta kalli Haseenah tace "Na fad'a mata ai, da farko mun jira ta sai tace ba ta jin dad'i mu tafi kawai."


Kallon Haseenah ya yi yace "Ke ya ki ka fad'a min?"


Ko kallon Khadija ba ta yi ba ta kalle shi tace "Bansan za su tafi ba, fitar su kawai na gani daga gida, idan da ta fad'a min ai zan bisu tunda lafiya ta k'alau."


Kallon Khadija ya yi yace "Na d'auka zan iya fad'a mi ki kiji ashe ba haka bane, yanzu ina so naji raina ni ne ki ka yi ko me?"


Da mamaki ta kalli Haseenah ta kalle shi tace "Amma fa wann..."


"Amma me, ki na so ki nuna ba na da mahimmanci ne ko me? Zan fad'i yanda na ke so ayi a cikin gida amma ke kiyi gaban kan ki, wannan ai iskanci ne da d'aukar mutane yan iska, to ban makullin motar."


Da mamaki kawai ta ke kallon shi kafin tace "Makullin mota kuma?"


Zaro ido ya yi yace "Eh, ko taki ce? Ai ba yan uwan ki bane suka siya mi ki bare ki ji dad'in magana, ni ne na siya da kud'i saboda tunanin kin cancanta."


Hannu tasa a jaka ta fito da makullin ta mik'a mi shi, hannu ya zuro zai karb'a ta rik'e tace "Zan baka, amma ina so ka k'ara bincike akan lamarin nan, sanin kan ka ne wannan yarinyar ba ta kai na tsaya na mata k'arya ba, Uwani ita ce na aika ta mata magana, kuma Bilal ya na wajen."


Haseenah ce ta katse da cewa "Uwani? Ita ce tace mi ki ba zanje ba? K'arya take wallahi, wannan yarinyar fa munafuka ce wallahi."


A fysace Khadija ta kalle ta tace "Kar ki sake kiran Uwani munafuka dan ba ita ba ce, Uwani ba yau mu ke tare da ita ba, nafi sanin ta fiye da ke kamar yanda shi kan shi ya fi sanin ta fiya da ke."


Cike da rashin kunya tace "Idan an kira ta munafukar me za ki yi? Me ya sa ki ke son had'a yar aikin gidan nan da mu ne? Da alama wata rana ma cewa za ki yi matar shi ce ita ma."


"Kai." Ya daka musu tsawa, cikin b'acin rai yace "Akan wata banzar yar aiki ne za ku tsaya kuna musayar yawu? Ba na so, kowace ta wuce d'akin ta."


"Banza? Uwani ce banza?" Cewar Khadija ta na kallon shi, "Eh na fad'a, ko nima rashin kunyar za ki min?"


Rumgume hannaye Haseenah ta yi tace "To ai ba ka wuce ta maka ba tunda ka tab'a yar gold d'in ta, wallahi yarinyar can munafuka ce ta gidan gaba, ranar ma ai duk ita ta haddasa masifar da matar ka ta kusan k'ona ni da raina."


"Oho, hakane kenan?" K'ofar fita ya nufa ya na fad'in "To bara ki gani, yau zata bar gidan nan kuma na ga wanda ya isa ya hana tunda gida na ne."


Tun daga k'ofa ya fara kiran sunan Uwani, da sauri ta matso dan ba nisa ta yi sosai ba, Khadija ma bayan shi ta biyo ta na fad'in "Dan girman Allah Abban Bilal kar ka yi haka, ka k'yale yarinyar nan, in Allah ya yarda babu abin da zai sake faruwa da za ka ji sunan Uwani a ciki."


Ko sauraren ta baiyi ba saida ya tsaya gaban Uwani ya kalle ta yace "Ke, na fahimci zaman ki a gidan nan ba zai yiwu ba saboda matsalar da ake samu, dan haka karb'i nan." Ya fad'a ya na fito da kud'i aljihun shi masu yawan gaske da baisan ko nawa ne ba ya mik'a mata yace "Ki je na kore ki, ba na son sake ganin ki a gidan nan, kinji ko?"


Ruwa ne ya cika idon Uwani ta na kallon Khadija, ganin ta k'i amsar kud'in ya sa ya janyo hannun ta ya damk'a mata ya na fad'in "Karb'i na ce ko."


Juyawa ya yi ya koma ciki sai Khadija ta dafa ta tace "Ki yi hak'uri Uwani, wannan ita ce jarabawa ta a game da k'ara auren Usman, kije Uwani, ban ji dad'in korar ki da ya yi ba, amma dai hakan ya sa hankali na ya kwanta, dan a yanda ya ke jin kansa yanzu zai iya wulak'anta ni a gaban koma waye, wanda ni kuma ba zan so hakan ba."


Kuka sosai Uwani keyi da k'yar Khadija ta rarrashe ta ta juya ta tafi, falo ta koma ta same shi tsaye da alama ita yake jira, makullin motar ya nuna mata yace "Daga yau motar nan ta zama ta duka yan gida, zan samo mu ku dreba da zai dinga kai ku duk in da za ku je, sannan daga yau ban yarda wata ta fita ta bar d'aya ba in dai har fita ce ta dangi na data shafe ni, wannan hukunci na ne."


Zai bud'a k'ofar falon shi dake falon ta ya wuce ta tare gaban shi ta na kallon k'wayar idon shi tace "Abban Bilal wane laifi na yi ma ka? Ka fad'a min dan Allah na baka hak'uri, wallahi tallahi ba zan juri wannan sabon yanayin ba, ka sani kai ma ba zan iya ba ko kad'an."


Lumshe ido ya yi saboda ganin fitowar hawayen ta, amma saboda tasirin sihiri sai kawai ya basar yace "Ba zan d'auki hukuncin da ya dace ba dole sai kin min wani laifi? Ba komai to."


Shigewa ya yi ya barta tsaye, da k'yar ta samu ta shiga d'aki ta cire kayan jikin ta ta wuce madafa, yau girki kala d'aya ta yi saboda yanayin da take ciki.


Ba wani shiri ta yi ba kuma tare da Bilal suka ci abinci, sai kusan goma ya shigo gidan, kasancewar Bilal baiyi bacci ba ya sa suka zauna falon shi suna kallo, abinci ya ci kafin ya shiga yi wa Haseenah saida safe, da k'yar ya baro d'akin ta dan baya son rabuwa da ita, Khadija ma d'aki ta raka Bilal ya kwanta kafin ta saka kayan bacci ta nufi d'akin shi, ta na kwance ya shigo ya wuce ban d'aki, ya d'an jima kafin ya fito ta na kallo har ya canza kaya, kashe wuta ya yi kafin ya kwanta gefen ta kuma nesa da ita ya juya mata baya, ta na ganin haka ta d'auki gilashin ta gefen ta saka ta janyo wata ma'ajiya ta d'auki Qur'ani ta fara karatu, Usman na so ya yi bacci amma fitinar sha'awar da ta taso mi shi saboda wasan da su ka yi da Haseenah ya sa ya kasa baccin, a k'alla awa d'aya su na haka ita ta na karatu shi ya na juye juye da matsar mara, a zabure ya juyo gefen Khadija ya rarumota ya danna bakin shi cikin nata, cikin dubara ta samu ta aje Qur'anin hannun ta...


Tabbas sihiri gaskiya ne kuma ya na iya kama kowa, Usman da ke bala'in jin dad'in kasancewa da Khadija a kowane lokaci, matar da take gamsar da shi fiye da tunanin mai tunani, amma yau ya kusanceta ba dan ya na so ba sai dan sauke abin da ke damun shi, da kuma *tsananin rabo*, da k'yar ya iya hak'ura ya kai bakin gab'a saboda ji ya ke kamar a cikin yaji ne ya ke link'aya da kayan shi, ta wani b'angaren kuma kamar a cikin tab'o ne ya jefa ta haka ya ke ji, babu wani dad'i da ya ji bare ayi maganar gamsuwa, gaba d'aya jin ta ya yi a k'afe babu ruwa kamar tabkin da ya tsotse, wanka ya shiga ya fito ya sake kwantawa ya juya mata baya, tsakin da ya yi ne ya sa Khadija juyawa ta kalle shi, tashi ta yi ita ma ta yi wanka ta dawo ta ci gaba da karatun ta.


Ana kiran sallah farko ya fita, ko Bilal bai waiwaya ba yau ya tafi masallaci, ya na dawowa kuma wajen Haseenah ya wuce, ko tashi ba ta yi ba ita kam ta na bacci, rufe d'akin ya yi ya zame kayan jikin shi a hankali ya shiga cikin zanin rufar, kamar a mafarki Haseenah ta ji wata wawar cakuma da ya wa k'irjin ta d'aya da hannu d'aya a baki, ta so raba kan ta da shi amma bai bata damar hakan ba saboda rik'on gaske ya mata ba kad'an ba, ya na jefa k'wallon sa a raga ya sauke wata arniyar ajiyar zuciya, kwance ya yi akan k'irjin ta ya yi shiru dan abin da ya ke ji ma kamar zai tafi da numfashin shi, saida ya d'auki kusan minti biyu a haka kafin ya fara aiki da gaske, irin sambatu da surutan da ya ke da ihu kamar wani zararre...Hum yau fa suruki na kad'an b'ata min rai gaskiya,😎 ka kiyaye ba na son haka.


Kusan awa d'aya ya d'auka kafin ya rabu da ita ya shiga ya yi wanka ya fito, kayan shi ya mayar a jikin kafin ya kalli Haseenah da ta had'a kai da gwiwa ta na kallon tace "Yanzu abin da ka yi ka kyauta? Yau fa ba kwana ne bane, me ka ke so a kalle mu dan Allah?"


Cike da nuna rashin damuwa yace "Ke ni dallah rabu dani, to zaunawa zanyi na kashe kai na bayan ina da maganin a cikin gida na, can babu abin da ke akwai sai kayan haushi da k'yama, to ya ki ke so na yi?"


Wani kallo ta masa tace "Ka na so ka ce babu abin da ka ke ji acan sai anan?"


Da sauri ya matso kusan ta ya rik'e hannun ta yace "Dan Allah kar ki fad'awa kowa maganar nan, amma wallahi matar can ba ta da dad'i, yanda ki ka san mutum ya fad'a a kwata haka take, ita fa ko miya marar kayan d'and'ano ta fita armashi."


Ba ta san lokacin da ta fashe da dariya ba saboda mugunta, shi kam rufe mata baki ya yi yace "Yanzu fad'a min me ki ke so na baki a matsayin tukuici? Wallahi na ji dad'in kasancewar mu yanzun nan." Ya k'arashe da sumbatar wuyan ta.


Cikin rik'e dariya tace "Ba na son komai miji na, tunda ma ka yi farin ciki hakan ya ishe ni."


Mik'ewa ya yi yace "Nagode matata, ni zan koma can na canza kaya, amma ki tashi ki yi wanka yanzu sai ki fito mu ci abinci."


Cike da makirci tace "Toh."


Ya na fita ta sauka da gaggawa ta shiga ta yi wanka ta fito ta yi sallah, riga ta saka iya gwiwa yar kanti ta fito da ita kai babu d'an kwali, lokacin Bilal har ya shirya Bilyamin ya d'auke shi sun tafi, Usman na zaune akan kujera Khadija na zuba masa abinci, yanda ya d'aure fuska babu annuri ne ya sa ta share shi ita ma, mayar da kallon shi ya yi ga Haseenah da ta fito ta na karkad'e gashin ta cikin takon jan hankali, kallon ta Khadija ta yi har ta zauna akan kujera, da wani shegen murmushi Usman yace mata "Sannu da fitowa."


Turo baki ta yi cikin shagwab'a tace "Ba zan sake ma ka magana ba sai nan da wata d'aya."


"Me?" Ya fad'a da zaro ido, d'orawa ya yi da "Haba amarya rufa min asiri mana, ina zan saka kai na to idan ki ka daina min magana, kinsan fa ke ce haske kuma fitilar zuciya ta dama gidan nan ba ki d'aya."


Sake turo baki ta yi ta kawar da kai tace "Ni ka k'yale ni kawai."


"To wai me na yi ma da za'a min wannan hukuncin?"


Kallon Khadija ya yi saboda aje farantin abinci da ta yi gaban shi, ita ma zubawa ta yi ta zauna ta fara tsakura ta na satar kallon su, amma zuciyar ta ta kai k'arshe wajen k'una, cike da shagwab'a tace "Ka ma manta kenan? Haka kawai ina bacci na za ka zo ka tara min gajiya, yanzu gashi duk jiki na ciwo ya ke, kuma saida na fad'a ma ka kar ka yi amma ka k'i saurara ta."


Hannu ya sa ya na shafa wuyan shi cikin alamun rashin gaskiya, satar kallon Khadija ya yi wacce ta k'i d'ago kai saboda hawayen da ke son taho mata, dan ya kawar da zancen ya sa ya kalle ta yace "Ba ki zuba mata abincin ba ita."


Wani jan kallo ta mi shi tace "Au! Wai ni ce ma zan zuba mata? To ai na ga duka yau kwanan mu ne ni da ita, me zai hana ta zuba da kan ta ko kuma ka zuba mata."


Had'e rai ya yi yace "Ke me ki ke nufi ne?

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login