Showing 117001 words to 120000 words out of 139085 words
Chapter 40 - KALLON KITSE Book Complete Document by Halima k Mashi .txt
a gidan nan?"
A harzuk'e ta kalle shi tace "A ina zan samo ma ka kayan bacci? Na wa zan d'auko ma ka?"
Har ta yi shiru shi kuma ya fara dariya sai kuma ta kalle shi tace "Wai ma tsaya, idan na d'auko ma ka kayan baccin me za ka yi da su?"
Ba alamar wasa yace "Nan zan kwana yau, tunda na fahimci ba za ki koma gidan ki ba, kinga saina raba mu ku kwana, biyu a nan biyu a can."
Tasowa ta yi ta kamo hannun shi ta na fad'in "A'a wallahi, akan me? Haka kawai kasa a kafa min hak'ora, kwana a nan saboda me?"
Fizge hannun shi ya yi yace "In dai ba kya son na kwana nan to ya zamar mi ki dole ki had'a kayan ki yanzun nan mu tafi na mu gidan."
Cikin b'acin rai tace "Wallahi babu in da zanje, haka ake kawai ka b'ullo min ta wannan hanyar."
A nutse ya kalle ta yace "Na fad'a miki ki bani hak'uri tare da lallab'a ni dan na mi ki maganin matsalar ki, amma girman kai ya hana ki ko? To ba damuwa mu ci gaba da zama a hakan tunda haka ki ke so, yarinya sai taurin kai."
"Ni na fad'a ma ka wani abu na damu na?" Ta fad'a ta na nuna kan ta da yatsa, saida ya tashi zaune yace "Ke kuwa ke da damuwa, gata nan b'aro-b'aro ina gani a idon ki."
Duk da idon na ta na cikin gilashi amma saida ta mitsika idon ta kafin tace "Ban gane ba fa."
Kashe mata ido ya yi yace "Yaushe rabon ki da ni? Yaushe rabon da na yi wasa da ke? Hajia Dije yaushe rabon da ki ji zallar ingantacciyar madara a jikin ki?"
Shiru ta yi kawai sai kallon bangon d'akin da take, murmushi ya yi yace "Shi ya sa yanzu zuciyar ki ta cika saurin hawa, ki ka cika masifa da jaraba, sannan ba kya da kuzari kamar yanda ki ke a baya, sannan hakan zai shafi lafiyar abin da ke cikin ki, saboda ni d'in nan da kika raina to lafiyayyen abincin shi na jiki na, za ki iya haifar yaron ki babu kazar-kazar a jikin shi da walwala kamar sauran yara, saboda ya rasa wani muhimmin abu da ya kamata ya samu amma kin hana shi saboda ki na bak'in ciki."
Juyawa ta yi ta kalli agogo ta ga har k'arfe goma ta soma wucewa, dan dama shi ma tara ta wuce ya shigo, kallon shi ta yi tace "Dan Allah babban mutum ka tashi ka tafi dare ya yi, ni kai na bacci na ke so na yi."
"Wasa ki ke ko Khadija? Yanzu ki na nufin ba ki yarda da abin da na fad'a mi ki ba kenan? To shikenan, ni dai na yi niyyar kwana anan, idan ke ki na jin kunyar kar mu wayi gari mu fito a d'aki d'aya to ki je d'akin Bilal ki kwanta."
Dafe goshi ta yi tace "Na shiga uku na, Abban Bilal ya ka ke so na yi ne?"
Wani kallon mamaki ya bita da shi, saukowa ya yi daga kan gadon ya tsaya daf da ita yace "Khadija, ke da kan ki, ke ce yau saboda takura da gundurar da na mi ki har ki ke iya fad'a a cikin ido na cewa kin shiga uku, Khadija me nai mi ki da zafi har haka? A gaskiya ban yi tsammanin jin wannan maganar daga bakin ki ba."
Juyawa ya yi cikin sanyin jiki ya d'auki hular shi yasa ya kalle ta yace "Shikenan uwar yarima, ni zan tafi, bana iya ce mi ki ga ranar da zan dawo ba, dan gaskiya kin kashe min k'warin gwiwa na, tunda ba kya son komawa zan rabu da ke, idan kin haihu kuma sai ki min magana idan ki na buk'atar takardar ki."
Kama hanya ya yi zai bar d'akin Khadija da idon ta su ka cika taf da hawaye ji ta yi kamar ta k'urma ihu, saida ya kama hannun k'ofar zai murd'a ta yi k'arfin halin janyo rigar shi da k'arfi, baya ya yo kamar zai fad'i tare da kallon ta, kafin ya ankare ta hankad'a shi kan gadon ya fad'a da k'arfi, da iya k'arfin ta ta fad'a kan shi ba tare da tunanin cikin jikin ta ba, rufe shi ta yi da duka tako ina kamar Allah ne ya aiko ta, kallon ta kawai yake bai hana ta ba sai murmushi da yake dokawa, ita kam kuka take ta na fad'in "Aikin banza kawai, ashe dama ba so na ka ke ba shi ya sa har za ka iya saki na, so ka ke kaje kai da amaryar ka ku ci amarcin ku."
Ganin sosai ta ke kukan da gaskiyar ta ya sa ya kwantar da ita a k'irjin shi ya na shafa bayan ta ya na fad'in "Kinji yanda zuciya ta kuwa ta buga lokacin da na ambaci kalmar takardar nan, dan Allah Khadija ki daina azabtar da ni haka, gaba d'aya kinsa na zama kamar mahaukaci saboda k'ok'arin ganin kin dawo gare ni, ki tausayawa uban yaran ki mana."
Luf ta yi a k'irjin ta na share hawayen ta, sun jima a haka kafin yace "To ya ake ciki yanzu? Za ki koma ne ko ko sai na aiko mi ki da takardar har gida?"
Wani naushi ta kai mi shi a ciki wanda ya sa shi bushewa da dariya ya dafe ciki, tashi ta yi zaune kafin ta kalle shi tace "A gaskiya ba zan iya binka ba a daren nan, kawai ka je gobe na dawo da kaina."
Dariya ya yi ya kamo kunnen ta ya rad'a mata "Ashe yarinya ta na so na mata b'arin madara."
Murmushi ta yi tace "Matsala ta da kai rashin kunya."
"Um hakane, amma ai ke ki ka koya min."
Tashi ya yi yace "Da gaske za ki dawo gobe?"
"Zan dawo mana, ba ni na fad'a ba."
"Idan ma ba ki dawo ba wannan karan su Hajia Kaltume da Turai zan aiko su d'auke ki su kai min ke."
Kallon shi ta yi tace "Turai dai? Lallai."
Tsaye ya mik'e yace "Yanzu kira min Bilal da shi zan tafi, dan nasan dole ma ki dawo idan na tafi da shi ai."
Ita kam saboda ta yi niyyar komawa ya sa ta mik'e tace "Muje idan ka d'auke shi sai ka wuce."
Tare suka fita daga d'akin su ka nufi d'akin Bilal, idon shi biyu ya na rik'e da wayar shi a hannu, nan ta canza mi shi kaya su ka tafi da niuyar za ta zo mi shi da sauran kayan, saida ya shiga d'akin Mama da ta jima da bacci ya tsokane ta yace ya tafiyar shi, idan ta damu da shi ta je ta yi bikon shi ita ma, saida ta rako su har k'ofar gida Bilal ya bud'e motar ya shiga, Usman na ganin haka ya damk'i Khadija da wata wawar sumbata da ta rikita su dukansu, da k'yar ya sarara mata kafin ya kalle ta da jajayen ido yace "Ki yi sauri ki zo da wuri, ina buk'atar ki kusa da ni Hajia ta."
Motsa bakin da ta yi ya sa ya yi murmushi yace "Na ji dai idan kin kama ni ki yankanin amma fa bayan kin shayar da ni ruwan ki."
Dungure mi shi kai ta yi tace "Wai kai ka manta da ka tsufa ne, watanni kad'an fa su ka rage ma ka ka cika shekara *arba'in da biyar* cif a duniya, amma ka na abu kamar wani tsohon bazawari."
Saida ya sa hannu ya na shafar k'irjin ta yace "Kafin na cika hamsin da biyar kuma sai kun haifa min yara goma, kin ga ai ba na mayar da kai na tsoho ba, kuma ma ai ba daga nan abun yake ba, k'arfi da mazantakar na nan." Ya mata nuni da zuciyar shi.
Da haka suka rabu ya tafi da Bilal, yau kam Khadija ta yi bacci cikin nutsuwa saboda burin ta ya cika, ta juya Usman son ran ta ta hakane ma har ta gano yanzun Haseenah ba ta da wani girma a idon shi, dan haka ta yi bacci da zumud'in gari ya waye ta fara shirin komawa.
A wajen Usman kam Haseenah ba ta san da shigowar shi ba saboda har ta yi bacci ita ma, saida ya shinfid'e Bilal a gadon shi kafin ya wuce d'akin ta ba dan komai ba sai dan ganin halin da take ciki kamar yanda yake yi kullum, bud'a k'ofar da ya yi ne ya sa ta tashi ta na murza ido, kallon ta ya ke sosai ya na jin wata sha'awar na sake fizgar shi, sai dai kuma ba ya so ya neme ta saboda ba ita ta taso shi ba dama, da k'yar ya iya cewa "Ki yi hak'uri na tashe shi ko? Ashe hr kin kwanta ma, yau kam ban shigo da wuri ba."
Gyara zama ta yi tace "Sannu da shigowa."
"Yawwa sannu, ya ki ke?"
Kallon shi kawai ta yi ba tace komai ba, juyawa ya yi zai fita yace "Saida safe ko, yau ma zan kwana a d'aki na saboda muna tare da yarima ne."
Da mamaki tace "Yarima kuma?"
Juyowa ya yi yace "Eh, Bilal ba."
Wani haushi ne taji ya kamata, saukowa ta yi daga kan gadon tace "Kenan a gidan na su ka yi dare haka? Babban mutum ka na ganin abin da ka ke yi ya dace kenan? Wannan fa ba adalci bane, ka daina kula ni, ka daina min magana, ba ka cin abinci na, sannan ba ka kwana a d'aki na, me nai ma ka hakane da ka ke min irin wannan hukuncin? Ni ba wani abu bane a gare ni dan na durk'usa har k'asa na ba ka hak'uri, ka fad'a min dan Allah."
Gyara tsayuwa ya yi ya na kallon ta, hak'ik'a komai gaskiya ta fad'a, sai dai baisan me zaice ba domin kuwa ba zai iya fad'a mata haka kawai ya ke jin tsanar ta ba, cikin taushin murya yace "Kinga ki yi hak'uri da duk abin da ke faruwa, kawai harkoki ne su ka d'anyi tsamari, amma insha Allahu komai ya kusan zuwa k'arshe, ki k'ara hak'uri kinji ko, saida safe."
Ya fad'a ya juya kenan ta sake cewa "Shikenan ka je ka kwana da Bilal, dad'inta dai ba ya da abin da ni ke da shi, komai daren dad'ewa nasan dole ka neme ni a duk in da na ke."
Juyowa ya yi ya kalle ta da mamaki yace "Da Bilal d'in za ki yi kishi? D'ana ne fa shi, kinsan mahimmancin shi a gare ni kuwa? To shi d'in kamar rayuwa ta ne, ina k'aunar sa fiye da komai, ki iya bakin ki in dai akan iyali na ne, ba na juran b'acin ran su ko kad'an."
Idon ta cike da ruwa tace "Usman ba ka adalci wallahi, kullum nunawa ka ke Khadija da d'an ta sune rayuwar ka, kullum sune ma su mahimmanci a wajen ka amma ni ko oho, to kasan ba ka so na me ya sa ka aure ni?"
Girgiza kai ya yi yace "Ni bance ba na son ki ba, sai dai abin da na sani kawai shine ina son iyali na, idan ki na son zama da ni ki so su kema, kuma kar ki d'auka Khadija kishiyar ki ce ki yi kishi da ita, maganar gaskiya ta wuce nan a wuri na, Bilal d'ana ne da ya fito daga jiki na tsatsona, amma ina wa mahaifiyar shi son da bana ma sa, kinsan me ya sa?"
*Ita rayuwa dama haka take, da kin zauna da su lafiya da wannan ranar ba ta zo ba, kuskuren da mu mata keyi wani lokaci shine, ba ma fahimtar abin da mazajenmu suke so, idan har ki ka fahimci mijinki na bala'in son mahaifiyarsa ko yan uwansa ko yayansa, sai ke ma ki bishi ki nuna musu so na gaskiya, ba dan komai ba dan kawai ki faranta mi shi, hakan zaisa ya dinga kallonki da daraja da kima, saboda kina son abin da yake so, amma kishi da hauka da wauta sai ta saka mu rufe idonmu mu nuna k'iyayya da kishi kan abinda suke so, yanzu dai gashi kalaman da a baya bai iya fad'a mata yanzu gashi ya na kallonta ya fad'a mata, kenan ta jima ba ta mutu ba, Allah kasa mufi k'arfin zuciyarmu.*
D'orawa ya yi da "Saboda da ita na fara had'uwa, ita Allah ya fara bani kafin ya bani Bilal, ita ce wacce Bilal d'in ya fito daga jikin ta, shi ya sa na ke mata k'aunar da ko shi Bilal ba na masa, zanji zafi matuk'a idan aka ce yau na rasa Bilal, amma kuma zanyi farin ciki idan na waiga naga Khadija a gefe na, ba dan komai ba saidan nasan za ta sake bani wani Bilal d'in."
Ya na gama fad'a ya juya ya bar d'akin ya koma na shi ya kwanta ya rumgume Bilal kamar zai had'e shi, ya na shafa shi har bacci ya d'auke shi shima, Haseenah kam kuka ta fashe da shi mai tsanani, wai abin da a baya yake ma sayawa baya fad'a yau gashi ya fad'a, kai lallai abin nan bana lafiya bane, tunaninta ne ya bata duk wani shiri da tayi a kan shi ya wargaje, dan haka dole ta sake sabo, da haka ita ma ta yi bacci da tunanin kiran Mariya idan gari ya waye.
*Luv u all.*π
09/03/2020 Γ 15:01 - πππ: ππππππππππ
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
ππππππππππ
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)*
πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€
```Fatan alkairi masoya```
_π Masoya wannan littafi wannan kyautar ku ce, nagode da soyayyar da kuke nuna min ni da kaya naπ, Allah ya barmu tare._π
_Bismillahir rahamanir rahim_
*37*
Ko da gari ya waye Bilal ya shirya cikin k'ananan kaya dan yau alhamis ce ba karatu, Usman ma kamar kullum cikin shadda ruwan madara ya shirya, tare suka fito falon Haseenah sun same ta zaune tana waya da Mariya, bayan ta fad'a mata akwai matsala ne Mariya tace ta sake fito da kud'i kawai a mata aiki, kafin ta yi magana ta ji fitowar su hakan ya tilasta mata aje wayar, juyowa ta yi ta na kallon su, duk da cikin hushi take amma tabbas tasan an samo Bilal ne daga Usman, dan zubin hallitarsu ma iri d'aya ce, duk da ba ta zauna da yaron sosai ba amma ta fahimci ya na da miskilanci fiye da ubansa, kai tsaye teburin cin abinci su ka nufa dan ba su ma lura da ita a zaune ba, saida ta ga sun zauna ta taso ta nufo su dan zuba mu su abinci, sai dai ta na mamaki yanda yau Usman zai ci abincin ta tunda ya jima baici ba, shi kuma zai ci ne kawai saboda Bilal na gidan yau, amma sam baya sha'awar cin abincin ta tunda ya lura kullum abinci kala d'aya ta iya sarrafawa, tun kafin ta tsaya wajen Bilal yace "Aunty ina kwana?"
Cike da makirci ta shafo kan shi tace "Yarima, ashe gidan mu ka kwana jiya, lokacin da ku ka shigo har na yi bacci, ya ka ke?"
Shi kam yaron fuskar shi ba fara'a yace "Lafiya lau."
Kallon Usman ta yi wanda ke kallon cikin ta shi ma tace "Ina kwana babban mutum?"
Ba walwala a tare da shi yace "Lafiya lau, ya jikin na ki?"
Da murmushi ta amsa da "Da sauk'i sosai." Shayi ta fara had'awa Bilal ta aje ma sa kafin Usman d'in, tare su ka karya dukan su bayan sun gama Usman ya mik'e zai fita, hannun Bilal ya kamo yace "Muje ko yarima, yau da kai za mu fita."
Da zumud'i ya mik'e tsaye dan bin mahaifin shi amma sai Haseenah tace "Haba dai babban mutum, wannan ma ai son kai ne wallahi, yaushe rabon da na ga Bilal, yau ya zo kuma shine za ka fice da shi, gaskiya ni dai ban yarda ba."
Kallon ta ya yi yace "To ya ki ke so ayi?" Kallon Bilal ta yi tace "Ka bar min shi mana, anjima idan ka dawo sai ku fita tare."
Duk da ya samu labarin dalilin da yanzun mahaifiyar shi ke gida, amma kuma ba ya jin akwai wani abu da za ta iya yi wa Bilal tunda ya na gari, ajiyar zuciya ya sauke ya kalli Bilal yace "Yarima, ka zauna tare da auntyn ka kaji, zan fita amma ba zan jima ba zan dawo, idan kuma ka gaji da zaman gidan ka na iya fita k'ofar gida wajen Rabe sai kuyi hira."
Saida Bilal ya kalli Haseenah kafin ya kalli Usman yace "To Abba, amma fa kar ka jima sosai."
Dafa kan shi ya yi yace "Ba zan jima ba insha Allahu."
Saida ya sumbace shi kafin ya kalli Haseenah yace "Ba wani abin da ki ke buk'ata?"
Sosa kai ta yi irin na kunyar nan ta kasa magana, hannu kawai ya sa aljihu ya fito da kud'i ya bata, karb'a ta yi ta mi shi godiya kafin tabi bayan shi har ya shiga mota, Rabe da ke zaune da littafin karatu (dan tunda aka ce za'a maidashi makaranta abun ya sake shiga ran shi) ya taso suka gaisa kafin ya bud'e mi shi k'ofa ya fice ya na binshi da addu'a, rufewa ya yi har ya zauna Haseenah ta k'wala mi shi kira ya zo, tsaye ya ke kamar yanda take su na kallon juna tace "Wannan pliwoyin ka basu ruwa mana, ya ka ke abu kamar ba ka san aikin ba ne."
Wani kallon raini ya mata dan babu abin da bai wani ba game da ita kafin yace "Tofa, to na ji zan ba su ruwan, shikenan?" Ya na fad'a ya juya ya bar mata wajen, ciki ta koma ba ta damu da shi ba dan a cewar ta k'aramin arne ne shi ba ta shi take ba, yau